Ticker

6/recent/ticker-posts

Yarfe A Wasu Wakokin Yabo Na Haruna Aliyu Ningi

Citation: Nasir Abdullahi USMAN (2025). Yarfe A Wasu Waƙoƙin Yabo Na Haruna Aliyu Ningi. Yobe Journal of Language, Literature and Culture (YOJOLLAC), Vol. 13, Number 1. Department of African Languages and Linguistics, Yobe State University, Damaturu, Nigeria. ISSN 2449-0660

YARFE A WASU WAƘOƘIN YABO NA HARUNA ALIYU NINGI

NA

NASIR ABDULLAHI USMAN

Tsakure

Wannan takarda mai take: Yarfe A Wasu Waƙoƙin Yabo Na Haruna Aliyu Ningi an shirya ta ne domin nazarin yadda mawaƙa suke amfani da abubuwa na yarfe a zamantakewar irin yau da kullum duba da yadda suka mayar da yarfe in babu shi to babu waƙar ballantana ma waƙar yabo duk ba za ta yiwu ba, ko kuma za ta zama kamar miya ba gishiri ma’ana ba za ta yi armashi ba. Manufar wannan bincike ita ce yin nazarin yarfe a cikin waƙoƙin yabo na zamantakewar rayuwa a cikin waƙoƙin Haruna Aliyu Ningi. Takardar ta mayar da hankali ne ga waƙoƙinsa na zamantakewar rayuwa, domin ganin yadda yarfe ya ginu a cikinsu. An yi amfani da ra’in Awon baka wanda aka ɗora binciken a kansa, wanda a ƙarshe takardar ta gano cewa yarfe abu ne da ya ginu a cikin waƙoƙin yabo na Haruna Aliyu Ningi. tun lokaci mai tsawo kuma har yanzu ana amfani da shi.

1.1 Shimfiɗa

Nazari a kan ayyukan adabi da suka haɗa da waƙoƙi da wasannin kwaikwayo da kuma rubutattun zube ba sabon abu ne a fagen nazarin Hausa ba, musamman idan aka yi la’akari da irin gudummawar da masana da manazarta suka bayar wajen fito da muhimman abubuwan da suka ƙunsa. Masana da manazarta irin su Mashi (1986) da Birniwa (1987) da Funtua (2003) da Ɗangulbi (2003) da Ɗan’illela (2010) da Sani (2012) da Adamu (2019) da Adamu (2021) sun yi waɗannan nazarce-nazarce ne ta la'akari da yadda adibai suka baje kolin basirarsu kan al'amuran ayyukansu na adabi. Yawancin nazarce-nazarce da ayyukan da aka gudanar sun shafi nazarin zubi da tsari da salo da turke ko jigo ne, yayin da aikin Yahaya (2016) ya yi nazarin bijirewa a waƙoƙin siyasa da Yusuf (2018) wanda ya yi nazarin tarihin jam'iyyar PDP a cikin rubutattun waƙoƙin siyasa.

Dangane da batun samuwa da bunƙasar siyasar zamantakewar rayuwa ko siyasar jam’iyya kuwa, za a iya alaƙanta shi da cuɗanyar da aka samu tsakanin Turawa da al’ummar ƙasar Hausa. Birniwa, (1987, sh 27-28) ya bayyana cewa tun a wuraren shekarun 1930-1940 ne aka fara jin ƙamshin samuwar ƙungiyoyin siyasa a Arewacin Nijeriya. An samu ɓullar ƙungiyoyi da dama duk da cewa ba su fito fili ƙarara a karon farko sun kira kansu da jam’iyyun siyasa ba, amma dai sun samar da cibiyoyin da sukan riƙa haɗuwa lokaci-lokaci domin tattauna al’amuran siyasa. Su kuwa Dudley (1968, sh 78-79) da Idris (2016, sh 51) suna da ra’ayin cewa, an fara samun ɓullar ƙungiyoyi ne a tsakankanin shekarar 1943. Ƙungiyoyin da aka samar wannan lokacin sun haɗa da; Ƙungiyar Inganta Rayuwar Mutanen Bauchi (Bauchi General Improɓement Union) wadda Sa’adu Zungur ya kafa a 1943, da Ƙungiyar Tattaunawa ta Mutanen Bauchi Discussions Circle) a 1944, da Ƙungiyar Zumunta ta Sakkwato (Youth Social Circle) a 1945, da Ƙungiyar Matasa ta Kano (Kano Youth Association) a 1948 da Ƙungiyar Matasan Zariya (Zaria Youth Association) ita ma a 1948 da sauransu. Waɗannan ƙungiyoyi da ma wasu duk an kafa su ne a tsakankanin 1943 zuwa 1948, waɗanda su ne suka narke suka zama jam’iyyar (Northern Poeple Congress) a shekarar 1951. Daga baya, sai wasu mutane suka ɓalle, suka kafa jam’iyyar (Northern Element ProgressiɓUnion). Waɗannan jam’iyyun da aka samu, wato Northern Element ProgressiɓUnion da Northern Poeple Congress, su ne suka kasance manyan jam’iyyun siyasa guda biyu masu hamayya da juna a ƙasar Hausa.

Bayan kafuwar jam’iyyun siyasa na farko, an riƙa samun musayar yawu daga magoya bayan jamiyyun biyu, inda aka samu rubuce-rubuce cikin jaridu da wasiƙu da jawaban siyasa waɗanda suke ƙunshe da al’amuran siyasa da suka faru a wancan lokacin. Irin waɗannan abubuwa sun ci gaba da gudana har zuwa wannan jamhuriya da ake ciki, wato jamhuriya ta huɗu, inda ayyukan adabi suka riƙa nuna hoton yadda al’amura da suka riƙa gudana waɗanda suka shafi waƙoƙin yabo.

Duk da cewa masana da manazarta sun bayar da gagarumar gudummawa da sukcancanci yabo, amma ba a samu wani aiki na nazarin ilimi da hannu ya kai kansa wanda aka yi nazarin yarfe daga cikin waƙoƙin yabo na Haruna Aliyu ba. Wannan ne ya sa aka ga dacewar tattauna wannan batu a wannan takarda domin ganin yadda yake da kuma yadda ake gudanar da shi a har kokin yau da kullum.

2.1 Bayani A Kan Muhimman Kalmomin Bincike

2.1.1 Ma’anar Yarfe

Kalmar Yarfe Bahaushiyar kalma ce, kuma kalma ce ta fannu aka aro domin a yi amfani da ita a kan waƙoƙin yabo, tana ajin suna ne mai ɗauke da jinsin namiji. Kalmomin Ƙage da Ƙazafi suna da makusantan ma’anoni da juna ko ma a ce ma’anarsu guda, sai dai kowacce da asalinta, kuma ana iya amfani da wata a maimakon wata. Kalmar tana nufin a ce mutum ya yi abin da bai ji ba, bai gani ba ko kuma a ƙulla masa sharri (CNHN, 2006 sh 273)Ƙazafi kuwa kalma ce da take da asali daga Larabci wato ‘Ƙazaf, wadda Hausawa suka ara suka yi mata Karin -i a ƙarshenta ta koma Ƙazafi. Ma’anar kalmar a Hausa da Larabci duk abu guda take nufi. Kalmar Ƙazafi suna ne mai ɗauke da jinsin namiji, kalmar tana nufin laƙa wa mutum laifi ko yi masa sharri da (CNHN, 2006 sh 279).

Ƙamusun CNHN (2006, sh 479-480) ya bai wa kalmar yarfe ma’anoni guda biyar kamar haka:

i.Maka ko daka

ii.Watsa

iii.Ƙaga

iv.Aika da, musamman na zagi

v.Amfani da hannu don share wani abu.

Daga cikin waɗannan ma’anonin, ma’ana ta biyu da ta uku ne suke da alaƙa kai tsaye da wannan takardar, domin a ƙarƙashin ma’ana ta biyu an ba da misali da ‘na watsa masa taɓo’ kuma duk abin da aka watsa masa taɓo to an bata wannan abin, domin zai nuna alamomi a wurare da dama a jikinsa. Ita ma ma’ana ta uku daga cikin ma’anonin an ba da misali ƙarƙashinta kamar haka: ‘Sun ƙaga masa laifi’. Ke nan kalmar yarfe tana nufin ƙaga wa wani mutum wani laifi kamar yadda aka bayyana ta a sama. Idan aka ƙaga wa wani mutum wani laifi wanda bai ji ba, bai gani ba yakan zubar masa da ƙima ko ya rage masa ƙima a idon mutane. Idan magoya bayansa ne sai a samu wasu su dawo daga rakiyarsa.

Don haka, kalmar tana nufin a sanya wani baƙon abu a jikin wani ta yadda zai iya yin ɗigo-ɗigo a jikinsa har ya fito a gani. Alal misali, kamar a samu farar tufa a yarfa mata manja ko wani baƙin mai wanda zai zama an ɓata wannan tufar. Manufar yarfe a nan ita ce ɓatawa, kamar yadda aka yarfa wa wannan farar tufar wasu launuka don a ɓata ta.

Kalmomi biyu na farko wato ‘yarfe’ da ‘ƙazafi’ dukkansu kalmomi ne da ake amfani da ma’anarsu a cikin harkokin yau da kullum, kuma in aka yi amfani da su suna iya dacewa da ko wa aka jefa da su. Za kuma a iya cewa an yi wa wane yarfe, ko an yi wa wane ƙazafi. A cikin waƙoƙin yabo ko waɗanda ba na yabo ba, za a iya faɗa an yi wa mutum yarfe ko ƙazafi, ma’ana an yi mishi ɓatanci ko an yi sharri. Ke nan, daga bayanan da suka gabata za a fahimci cewa, kowane yarfe ko ƙazafi duk abu ɗaya ne wato sharri ne, kuma ɓatanci ne, da ake yi wa wani a cikin waƙoƙi na zamantakewar rayuwa ciki har da na yabo, domin a daƙushe shi kuma a ɓata shi a idon mutane, ta hanyar ɗora masa wani abu da bai ji ba bai gani ba. A taƙaice dai, kalmar yarfe bisa fahimtar mai nazari a wannan binciken tana nufin faɗin wani abu da bai tabbata ba, tare da danganta shi kan wani mutum.

2.1.2 Ma’anar Waƙa

Masana da manazarta adabi da dama sun bayyana ra’ayoyinsu tare da bayar da fahimtar su dangane da ma’anar waƙar Hausa. Daga cikin su akwai:

Ɗangambo, (1982), “Waƙa wani furuci ne wato lafazi ko saƙo cikin azanci da ake aiwatarwa ta hanyar rerawa da daidaita kalmomi cikin wani tsari ko ƙa’ida da kuma yin amfani da dabaru ko salon armashi”.

Umar, (1980, sh 3) “Waƙa tana zuwa ne a sigar gunduwoyin zantuka waɗanda ake kira baitoci ko ɗiyoyi kuma ake rerawa da wani irin sautin murya na musamman”.

Shi kuwa Yahaya, (1976). “Waƙa magana ce ta fasaha a cure wuri ɗaya a cikin tsari na musamman”

Yahya, (1984). “Waƙa maganar hikima ce da ake rerawa ba faɗa kurum ba wadda ke da wani saƙo da ke ƙunshe cikin wasu kalmomi zaɓaɓɓu, tsararru kuma zaunannu”.

Waƙa ita ce maƙerar mawaƙi. A nan ne yake narka kalmomi ya fito da saƙonsa zuwa ga al’umma. A nan ne kuma yake narka su ya yi maganganun hikima, hikima ta harshe ko ta hanyar rayuwa. Waƙa magana ce ta tsakanin zukata ko bayan cewa tunani ma yana naƙalta. Abin nufi a nan ita waƙa takan yi tsari ne kai tsaye kan zuciya fiye da sauran nau’o’in magana. (Yahya, 2016, sh 26).

A fayyace ana iya cewa waƙa magana ce da aka zayyana ba wadda aka sako kara-zube ba. Magana ce wadda aka aza bisa sanannu ko ayyanannun ƙa’idoji waɗanda ke daidaita furuci da sauti, su kuma tilasta zaɓar kalmomi domin dacewar ma’ana da furuci. Ta haka ne maganar take zuwa babu karo da juna ta furuci ko kalmomi ta fuskar daidaiton tsawon gaɓoɓi, saɓanin magana ta yau da kullum. (Yahya 2016, sh 27) Waƙa wasu zantuka ne da ke ɗauke da saƙo mai nusarwa tare da nishaɗi cikin hikima.

2.1.3 Ma’anar Yabo

Wannan kalma ta yabo abu ne da kowane mutum ke ƙaunar ya samu ko ya ji alaƙanta shi da ita a cikin harkokin rayuwarsa ta yau da kullum, sannan kuma bai son akasinta a ma’amalarsa irin ta yau da gobe, Kalmar yabo tana ƙara wa mutum ƙwarin guiwa da karsashi a rayuwarsa. CNHN (2006) ya bayyana yabo kamar haka ‘faɗar duk wata kalma mai daɗi ga wani mutum da ya aikata wani kyakkyawan abu. Misali (i) saboda ya yi masu (ii) ambaton sunayen Annabi da yi masa addu’a, kamar irin na Ishiriniya da Diwani.

3.1 Ra’in Bincike

An ɗora wannan aiki ne a kan Ra’in Awon Baka (Oral Formulaic Theory). Wannan ra’i an ƙirƙire shi ne a ƙasar Sabiya, wato Philips Ɓiscy (1767-1834) ne ya ƙirƙiro shi, kuma shi ne ya yaɗa ra’in a ƙasar Sabiya har zuwa wasu sassa na Turai da Amurka. Wannan mazhaba ta sami bunƙasa ne tun a farkon ƙarni na ashirin (1920-1935) a lokacin da masana na Turai suke nazarin dogayen waƙoƙi, musamman irin ayyukan Milman Parry da ɗalibansa Albert Lord. Amma fitaccen wanda ya ɗabbaƙa wannan mazhaba shi ne John Miles Foley, tare da taimakon wani mutumin Sabiya wato Francis Peabody suka bunƙasa ta. Daga bisani kuma Albert Lord ya yi ƙoƙarin ɗora wannan mazhaba a kan tsofaffin waƙoƙi na Turawa tare da fito da bambance-bambance da ke cikin waƙoƙin.

An ɗora wannan aiki a kan ra’in Awon Baka saboda la’akari da aka yi cewa, abubuwan da aka kula da su a kan wannan ra’i sun haɗa da layukan ɗan waƙa da ƙulli da ƙari, ta nazarin waƙar baka Bahaushiya (ta hanyar duba hawa da sauka da saukar sauka da amsa-amo kari da amfani da sassan adabin baka da sauran su) kamar yadda Gusau (2015) ya yi nuni. Ire-iren ayyukan da waɗannan masana na cikin gida suka aiwatar mai nasaba da wannan ra’i sun haɗa da: Abdulƙadir (1975) da Bichi (1975) da Ibrahim (1983) da Gusau (1983 da 1988 da 2014).

Wannan Ra’i yana ganin cewa waƙoƙi rumbu ne na hikimomi, wanda ake amfani da su yau da gobe kuma ya bayyana irin al’amuran da suke faruwa cikin hikima tare da danganta su cikin magana, daga ƙarshe suke rikiɗewa su koma ɗiya na waƙa. Wannan mazhaba tana da manufofi kamar haka:

· Nazarin azancin magana na baka kamar karin magana da adon harshe.

· Duba aikin adabi musamman adabin baka

· Fito da hanyoyin nazarin awon baka na waƙoƙi, domin gane irin hanyar da aka bi wajen irin awon baka da aka ɗora waƙa a kai.

· Ƙoƙarin faɗaɗa fahimta da nuna burgewa dangane da yadda ake gudanar da waƙoƙin baka.

· Neman bayanin tarihin mawaƙin da zamaninsa.

· Nazarin dokokin al’umma ta hanyar adabin baka kamar camfe-camfe da sauran su.

· Adana labarun gargajiya a ka ta hanyar naƙalta da adanawa a ka ba tare da rubutu ba.

· Tattara tatsuniyoyi da waƙa daga wata al’umma zuwa wata.

· Lalubo yadda yanayin waƙoƙi suke a bakunan mutane.

(http://en wikipedia.org/wiki/maɗist literary criticism).

Duba da waɗannan manufofi na wannan mazhaba ta Awon baka, ya sa wannan bincike ya dace a ɗora shi bisa wannan mazhaba ta awon baka, musamman ganin cewa wannan aiki ya yi duba ne a kan wasu waƙoƙin yabo na baka na Haruna Aliyu Ningi.

4.1 Taƙaitaccen Tarihin Haruna Aliyu Ningi.

An haifi Haruna Aliyu Ningi ne a ranar talata ashirin da biyu ga watan Nuwamba alif ɗari tara da saba’in da bakwai (22-11-1977) a garin Ningi. Sunan mahaifinsa Abdullahi amma yana amfani da sunan kakansa Aliyu saboda tunawa da kakan da kuma irin addu’o’in da ya yi wa iyayensu da kuma dangin su.

Bayan ya samu kimanin shekaru biyar ne, sai aka sashi a makarantar firamare a shekarar alif ɗari tara da tamani da biyu (1982), makarantar firamare ta Rumbu inda ya shekara biyu 1982-1984. Daga nan ne sai ya wuce makarantar firamare ta Garɗo daga (1984-1985), kuma (1985-1986) ya koma makarantar firamaren Ziɗaga dukansu a gariNingi. A wannan shekarar ya tafi sakandare dakBurra daga 1986-1988. Bayan ya ƙara zama a gida na kimanin shekaru huɗu, shekarar 1992 ya koma aji hudu a babban sakandare ta Dagauda a karamar hukumar Dambam ta Jihar Bauchi inda ya kammala makarantar a shekarar 1993.

A shekarar 1994 ya tafi makarantar kimiyya da fasaha da ke Ƙauran Namoda a inda ya samu Diploma a kan harkokin kuɗi (financial studies) a shekarar 1996, Ya zauna a gida na shekara ɗaya, kuma wannan shekarar ana cikin siyasar UNCP da DPN, kuma a wannan shekarar ya rubuta waƙa ta siyasa. Wannako ya faru ne a sanadiyyar murɗiya ko maguɗi wanda aka yi ma ɗan takarar su a ƙarƙashin jam’iyyar DPN, wanda shi ne Ɗanlami Garba Bara’u. Mawaƙin ya yi wannan waƙa ba kai ba gindi, domin ya ce ko suna bai sa mata ba balle ƙafiya. Kuma bai ajiye ta ba, Sabodhaka a yanzu ta ɓace. Daga baya sai ya lura akwai hannun gwamnati a wannan murɗiya da aka yi, saboda haka sai ya rabu da siyasar Bauchi ya koma Kano, a nan sai ya fara yi wa UNCP waƙa da kuma shugabanta Alhaji Shehu Shanono.

 Haruna Aliyu Ningi ya sake rubuta waƙa a lokacin siyasar PDP. Dalilin da ya sa ya yi wa PDP waƙa kuwa shi ne ya karanci jama’arta kaf ‘yan siyasa ne. Waƙar da ya fara rubuta ma PDP ita ce “Iyata Sarauniya”. Inda ya yaba wa jam’iyyar da ‘ya’yanta tare da kuɗa da washi’. Dagnan sai ya zarce da rubuta wa mutane waƙoƙin yabo masu armashi da kama zukata.

A halin yanzu Haruna Aliyu Ningi ya sauke farali wato aikin hajji, kuma ya yi auren fari a ranar a 23 ga watan Augusta 2003. Sannan Allah ya albarkace shi da ɗa namiji a ranar 26 ga watan Yuli 2005, inda aka sa wa yaron Umar Faruk, sanan matarsa Fatima.

Dangane da karatun allo kuwa Haruna Aliyu ya yi na ɗan ƙanƙanin lokaci ne, wanda bai wuce wata uku ba, sai kuma wanda ya yi a makarantar firamare daga aji ɗaya zuwa uku.

5.Yarfe A Wasu Waƙoƙin Yabo Haruna Aliyu Ningi

Haruna Aliyu Ningi fasihin mawaƙi ne wanda ya shahara a fagen rera waƙoƙin Hausa, musamman ma waƙoƙin yabo da kuma waɗanda ba na yabo ba. Mutane da yawa a ƙasan nan sun sami ɗaukaka da sanuwa ta dalilin waƙoƙi da ya yi masu, saboda yadda ya riƙɗabbaƙa manufofinsu ta hanyar yabo a idon mutane har suka amince suka karɓe su. Kasancewarsa gwani a fagen waƙoƙin ya sabbaba masa iya yin yarfe yayin da yake rera waƙa. Alal misali, a waƙarsa ta ‘Ba Za Mu Ɗau Coge Ba’ wanda ya yi wa Faruƙ Adamu Jigawa, inda ya yi wa wani yarfe a cikin waƙar kamar haka:

A Jigawa an takura an kai mu bango bana,

 An mai da kaf al’ummammu kamar dashen zogala,

 A rashin sani mun ɓata da hannunmu mun ɗau rina,

Ba za mu sake zuwa Kogi da ɗan kurme ba. Usman (2011).

Wannan ɗan waƙar, mawaƙin ya yi yarfe da kalmarina, wato wani ɗan ƙwarbaƙi mai fiffike wanda ya fi zama a kan bishiya wanda yake harbin mutumin da ya hau bishiyar da gidansa yake kanta kuma ya kusanci gidan. To babu shakka sai dai ya ji saukar harbi, kuma da ya yi harbin, zai ɗauke ƙarinsa ya tafi da shi.

Kuma ya sake yin yarfe inda ya ce, ba za su sake zuwa kogi da ɗan kurme ba. Wannan kalma ta kurme ma’anarta shi ne yin nutso can ƙasan ruwa a daɗe ana tafiya ana kamo kifi wanda masunci yake yi, wato nutsa ƙasan ruwa a kogi a daɗe ana kama kifi ba tare da ɗagowa sama ba shi ne kurme, kuma ba duk masunci ne yake yi ba saboda yana da haɗari. Kalmomin rina da kurme duk yarfe ne.

 Kullum a yawo yake tamkar Karen Barbara,

Ba za ya zauna ba ne ko za mu ɗau kokara,

 Don dai da amsar faɗawa Jigawa ko mun jira,

 Sai tafka sata yake bai gane mun farga ba.

A wannan ɗan waƙan na sama kuwa, ya yi masa yarfe da cewa kullum bai tsaya wa ya sauke nauyin da ke kansa, wato haƙƙin mutane da ya yi alƙawarin zai iya, sai yawon yake ta yi kamar karen Barbara. Ma’ana a nan shi ne, karan Barbara kare ne wanda ba na kowa ba kuma ba shi da wani tsayayyen waje da ake samunsa, shi duk inda ya ga matan karnuka bin su kawai zai kama yi. Sannan ga tafka sata kamar ɓera. Ma’ana a nan shi ne duk abin da ya gani wanda hannunsa ya kai gare shi ko ya ƙyalla ido ya gani to zai ɗauke. Waɗannan kalmomi guda biyu duk yarfe ne.

Mawaƙi Haruna Aliyu Ningi ya yi wa Bola Ahmad Tinibu yarfe a cikin waƙarsa, inda ya ayyana shi da:

Baba Hamed Bola Tinibu Lagos ya take?

Ba ni da tambayar in ji ya jama’ar Lagos suke,

Shi ba ya sani ba sabo in ka ƙi ya take,

Cinnaka yake baka san na gida a ɗangaren yarbawa. Usman (2011).

A cikin wannan ɗan waƙar ya yi amfani da kalmar cinnaka, wato wani ɗan ƙwaro ne baƙɗan ƙarami mai fitowa daga cikin rami a ƙasa lokacin damina. Yana da fuffuke da yake tashi sama ya maƙe wa mutum cikin tufa ya yi ta cizonsa, in ma a ƙasa ne haka zai yi wa duk wanda ya maƙale masa a jikin tufafi. Saboda haka Bahaushe ke masa kirari da cinnaka ba ka san na gida ba, kowa cizo yake, matuƙar dai ka raɓe shi, to babu shakka sai ya cije ka. A wajen Bahaushe da zarar aka ce wannan mutum ai cinnaka ne, to abin da ke zuwa a ransa shi ne wannan mutum azzalumi ne ko maƙetaci. Duk kalmomin biyu na yarfe ne.

A waƙar ‘Dokin Ƙarfe’ ma, ya yi yarfe ga wani mutum kamar yadda ya faɗa a ɗan waƙar da yake tafe:

 Wakilinmu na ɗazu mun ga illa,

 Muna kai shi ya fara sunce dala,

 Ya mance alai la da ƙila,

 Ya kwanta a hakin mu ya ɓace yai mana laya. Hussaini (2009).

Mawaƙin ya yi yarfe da kalmar sunce dala, kalmar kuɗi ne irin na ƙasar Amurka wanda aka fi yin hada-hadar hulɗar cinikayya a duniya, saboda haka wani mutum sai ya riƙa kwashe wa yana sawa a aljihunsa.

ɗan waƙar ‘Ƙalubale’ da ke tafe Mawaƙi Haruna Aliyu Ningi nan ma ya yi yarfe a cikinta inda yake cewa:

Kan ‘yanci da tararradin wai a yi gardama,

Idan za ka shigo gidanmu sai ka yi sallama,

Muna shuka fara wa’yansu na shuka baƙar rama,

Macutan nan Baba kaf suke kashe Nijeriya. Yusuf, (2018).

A cikin wannan ɗan waƙar mawaƙin sojoji ya yi wa yarfe inda ya kira wasu mutane da Macuta kuma ya ce su ne suke ɓata ƙasar, cuta tilo macuta jam’i saboda kullum idan suka tashi shigowa ƙasarmu ba sa sallama sai dai a wayi gari da su ko’ina kurum, kuna so ko baku so, oho dai, wannan dai ku ta shafa su ba ruwansu.

A wannan ɗan waƙar ‘Iyata Sarauniya’ ya yi wa rundunar sojojin ƙasarmu yarfe domin al’umma su ƙara tsanarsu tare da ƙyamatarsu ta hanyar ƙanga masu wasu batutuwa kamar haka:

Kai ina Abba Haruna Ningi Rimin mabuƙata,

Wa’yanda muke so a kauda mulkin matsiyata,

Suna iƙirarin yasu-yasu za su wadata,

Da yardarm Allah ƙasarmu mu za mu riƙeta. Yusuf (2018).

A nan ma ya yi yarfe a ɗiyan wannan waƙar ga mulkin sojoji inda ya kira shi da mulkin matsiyata sannan kuma ya yi masu yarfe da cewa suna iƙirarin yasu-yasu za su wadata, ma’ana su kaɗai ne kawai za su amfana da wannan mulki da suke yi, sauran al’umar ƙasa kuwa ba za su amfana da wannan mulkin nasu ba. Mulkin sojoji mulki ne na danniya wanda jama’ar ƙasa ba su da ‘yancin faɗin albarkacin bakisu game da yadda suke jagorantar su.

Ai na san jama’ar ƙasarmu yau sun yi tunanai,

Da al’ummomin ƙasarmu duk an mana rauni

 A yau mun gama shawarar mu ɗauko mai mana Danni,

 Ta fishe mu ga dukka jalli-jogon matsiyata. Usman (2011).

ɗan wannan waƙar mai suna ‘Abar So A Zukata’ ya yi yarfe ga wasu mutane da cewa al’ummomin ƙasa sun wahala sun sha wuya saboda irin rauni da suka yi masu, wannan kalma ta rauni tana nufin lahani ko ciwo don haka tun wuri bari su rabu da waɗannan batutuwa, yarfe ne.

Haruna Aliyu Ningi ya yi wa wani yarfe a cikin waƙar Hazo rufe rana a wannan ɗan waƙar inda yake cewa:

 Ga gwanje a cikin Arewa wanda yake ƙyamar mutane,

 Bai taɓa jaddada ƙa’ida ba duk lamarinsa a yaudara ne,

 Ya yi ada kuma ya matsanta wai ya daɗa koma ta yane,

 Yau da Zidani ƙwallo take yi ba da Agentina ba Baba. Usman (2011).

A wannan ɗan waƙa mawaƙin ya yi masa yarfe da cewa shi mutum ne wanda yake ƙyamar mutane, a nan ana nufi bai son mutane. Haka kuma ya sake cewa bai taɓa jaddada ƙa’ida ba, sannan kuma duk lamarinsa yaudara ne, wato ba gaskiya, saboda ba a gane inda aka sa gaba. Ke nan duk kalmomin biyu yarfe ne.

Mawaƙi Haruna Aliyu Ningi ya yi wa wani shugaba yarfe a cikin waƙarsa, inda yake cewa:

 Zan fara batun mantau ya mance Jiharsa cikin yaƙi,

 Rikici suka huhhura dubbab jama’a aka yayyanke,

 Bai kai masu diyya ba bai damu ba su aka faffarke,

 Inda a tazarce ne da kun ga shirin rikici babba. Hussaini (2009).

MawaƙHaruna Aliyu Ningi ya yi yarfe a waƙar ‘Ba Mu Yarda Ba’ ga wani jagoran al’umma inda yake cewa ya mance Jiharsa cikin yaƙi, yaƙi shi ne faɗa tare da kashe rai, da ɓarnar dukiya. Sannan kuma har ila yau ya sake yarfe da cewa rikici suka huhhura dubban jama’a aka yayyanke waɗannan batutuwa yarfe ne.

6.Sakamakon Bincike

Daga bayanan da aka kawo a sama, an fahimci cewa waƙoƙin yabo na Haruna Aliyu Ningi suna cike da wasu al’amura waɗanda suka zama tamkar gishiri a cikin miya. Daga cikin waɗannan abubuwa kuwa akwai yarfe, wanda Haruna Aliyu Ningi yake yin amfani da shi a zahiri da kuma tsarin wanda yin hakan ba daidai ba ne. Domin a wasu lokuta yakan taɓa mutuncin wani kai tsaye cikin abin da bai ji ba bai gani ba sannan ma babu tabbas ko ma ba gaskiya ba ne, sai dai ya zama hanyar jawo ra’ayin al’umma ne da su ƙara jin daɗin waƙoƙin yabo na Haruna Aliyu Ningi.

Binciken ya gano cewa, yarfe ba sabon abu ba ne a cikin waƙoƙin yabo na Haruna Aliyu Ningi, wato daɗaɗɗan abu ne, kuma yana amfani da shi ne domin cim ma wani burinsa a waƙoƙinsa na yabo da yake yi wa mutane. Kuma har yanzu yana ci gaba da amfani da shi a waƙoƙin nasa kamar yadda wasu mawaƙan da suka gabace shi suke amfani da shi.

Wani abu kuma da binciken ya gano shi ne, yarfe yana taimaka wa mawaƙi wajen samun nasara a cikin waƙoƙinsa na yabo, musamman Haruna Aliyu Ningi, domin faranta ran wanda ya yi wa waƙar, ya kuma baƙanta ran wanda aka yi wa yarfen.

7.1 Naɗewa

Wannan maƙala ta tattauna a kan yadda Haruna Aliyu Ningi ya riƙa amfani da yarfe a cikin waƙoƙinsa na yabo. Tun da farko a cikin gabatarwa an kawo taƙaitaccen tarihinsa da kuma waƙoƙinsa na yabo. Daga nan sai aka kawo ma’anar yarfe da waƙa da yabo domin haska inda sunan takardar ta dosa. Daga bisani sai aka tsunduma cikin nazarin yarfe a cikin waƙoƙin yabo na Haruna Aliyu Ningi tare da kawo misalai daga cikin waƙoƙin. A ƙarshe, binciken ya gano cewa waƙoƙin yabo na Haruna Aliyu Ningi mafi yawa suna ɗauke da yarfe, wanda ya samo asali tun farkon fara waƙoƙinsa, kuma ba abin mamaki ba ne idan aka ga ya ci gaba da amfani da shi a waƙoƙinsa na yau da gobe, a matsayin wata hanya ta faranta waɗanda yake yi wa waƙoƙin yabo.


 

Manazarta

Adamu, M. (2019). Kawatanci Tsakanin Rubutattun Waƙoƙin Siyasar Jumhuriya Ta Uku Da na Jumhuriya Ta Huɗu A Nijeriya. Jami’ar Umaru Musa ‘Yar’adua.

Adamu, A. I. (2021). Dabarun Jawo Hankali AWasu Waƙoƙin Siyasa A Jihohin Kano da Katsina da Zamfara Daga 2007 Zuwa 2018. ƊKundin digiri na ukuɗ sashen koyar da harsunan Nijeriya. Jami’ar Bayero.

Bichi, A.Y. (1975). Waƙoƙin Aure a Ƙasar Hausa (Hausa Wedding Song). Cikin Yahaya, I.Y. Bello, G, Bichi, A.Y, Dresel L., Sa’id, B. Harsunan Najeriya Vol. 41-45.

Birniwa, H. A. (1987). Conserɓatism and Dissent: A Comparatiɓe Study of NPC/NPN and NEPU/PRP Hausa Political Ɓerse from Circa 1946 To 1983, Ɗkundin digiri na ukuɗ, sashen harsunan Nijeriya. Jami’ar Usmanu Danfodiyo.

CNHN. (2006). Kamusun Hausa na Jamiar Bayero. Ahmadu Bello University Press.

Ɗan’illela, A. (2010). Rubutattun Waƙoƙin Siyasa: Nazari A Kan Jihohin Sakkwato Da Kebbi da Kuma Zamfara. ƊKundin digiri na biyuɗ sashen harsunan Nijeriya. Jami’ar Usmanu Danfodiyo.

Ɗangambo, A. (1984). Rabe-raben Adabin Hausa da Mahimmancisa ga Ryuwar Hausawa. Triumph Comfany.

ƊangamboA. (1975). The Role of an Oral Singer in Hausa/Fulani Society: A case study of Mamman Shata. ƊKundin digiri na ukuɗ. jami’ar Indina.

Ɗangambo A. (2007) Daurayar Gadon Fiɗe Waƙa (sabon tsari). K.D.G. Publishers.

Ɗangulbi, A. R. (2003). Siyasa A Nijeriya: Gudunmawar Marubuta Waƙoƙin Siyasa Na Hausa ga Kafa Dimokuraɗiyya a Jumhuriya ta Hudu Zango na Farko. ƊKundin digiri na biyuɗ sashen harsunan Nijeriya. Jami’ar Usmanu Danfodiyo.

Dudley, B. J. (1968). Parties and Politics in Northern Nigeria. Frank Cass and C Ltd.

Funtua, A. I. (2003). Waƙoƙin siyasa na Hausa a Jumhuriya ta uku: yanaye-yanayensu da sigoginsu, Ɗkundin digiri na biyu, sashen harsunan Nijeriya. Jami’ar Bayero.

Gusau, S. M. (2003). Jagoran Nazarin Waƙar Baka. Benchmark Publishers.

Gusau, S. M. (2008). Waƙoƙin Baka a Ƙasar Hausa: Yanaye-yanayensu da Sigoginsu. Benchmark Publishers.

Gusau, G. U. (2014). Al’ada da Ɗabi’un Mawaƙan Hausa, Zauren Waƙa Journal. Jami’ar Usman Ɗanfodio.

Gusau, S. M. (2015). Mashabobin Ra’i da Tarke da Al’ada na Hausa. Kano: Center Research and Publishers.

Gusau, S. M. (1983). Waƙoƙin Noma na Baka: Yanaye-yanayensu da jigoginsu musamman a Sakkwato, Ɗkudin digiri na biyuɗ sashen koyar da harsunan Nigeria. Jami’ar Bayero.

Gusau, S. M. (1988) ‘‘Waƙoƙin Makaɗan Fada: Sigoginsu da Yanaye- Yanayensu, Ɗkundin digiri na ukuɗ sashen koyar da harsunan Nijeriya, Jami’ar Bayero.

Hussaini, B. (2009). Haruna Aliyu Ningi Da Waƙoƙinsa. Amana Pulishers.

Ibrahim, M. S. (1983). Kowa Ya Sha Kiɗa. Longman Nigeria.

Idris, Y. (2016). Bijirewa A Waƙoƙin Siyasa: Bincike Kan Wakokin 1903-2015, Ɗkundin digiri na biyuɗ sashen harsuna da al’adun Afirka. Jami’ar Ahmadu Bello.

Mashi, M. B. (1986). Waƙoƙin Baka na Siyasa, Dalilansu da Sababinsu ga Rayuwar Hausawa, Ɗkundin digiri na biyuɗ Jami’ar Bayero.

Mustapha, O. (2015, Satumba 4). Yarfen Siyasa Ce A Ce Muna Gaba Da Buhari –Ali Wakil. An samo daga https://aminiya.ng/yarfen- siyasa-ce-a-ce-muna-gaba-da-buhari-ali-wakili/

Umar, M. B. (1980). Nazarin Waƙoƙin Hausa. Publications Centre.

Usman, N. A. (2011). Tarken Waƙoƙin Adawar Siyasa na Haruna Aliyu Ningi, Ɗkundin digiri na biyuɗ. Jami’ar Ahmadu Bello.

Sani, M. M. (2012). Tunanin Siyasa a Waƙoƙin Malam Hassan Nakutama, Ɗkundin digiri na biyuɗ. Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo.

Yahaya, A. B. (1984). Matsayin Waƙoƙin Baka a Cikin Adabin Hausa. Maƙala Wadda Ya Gabatar A Makon Hausa. Kwalejin Horar da Malamai Mata ta Larabci.

Yahaya, I. Y. (2016). Hausa a Rubuce: Tarihin Rubuce-Rubuce Cikin Hausa. NNPC

Yusuf, J. (2018). Tarihin Jam’iyyar PDP a Bakin Marubuta Waƙa, Ɗkundin digiri na biyuɗ. Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo

 Yobe Journal of Language, Literature and Culture (YOJOLLAC)

Post a Comment

0 Comments