Ticker

6/recent/ticker-posts

Wanda Ya Kashe Kansa, Shin Zai Dawwama Ne A Wutar Jahannama Ko A'a?

TAMBAYA TA 3091

Assalamu alaikum barka da warhaka Malam da fatan malam yana cikin koshin lafiya.

Tambayana shi ne mene ne matsayin wanda ya kashe kansa?

A ranan tashin kiyama shin zai dauwama ne a cikin wutan jahannama ne ko akwai wa'adin fitarsa?.

AMSA

Wa alaikumus salam wa rahmatullahi wa barakatuhu.

Hakika kisan kai ko kuma mutum ya kashe kansa, babban laifi ne a addinin Musulunci. Kuma Allah mai girma da ɗaukaka ya haramta wa bayinsa yin haka. Allah ya ce "KADA KU KASHE KAWUNANKU, HAKIKA ALLAH TABBAS MAI JIN ƘAI NE GAREKU".

"WANDA DUK YA AIKATA WANNAN DOMIN KETARE IYAKA DA KUMA ZALUNCI, DA SANNU ZAMU SHIGAR DA SHI WUTA, KUMA YIN HAKAN YA KASANCE ABU NE MAI SAUKI GA ALLAH".

A cikin hadisai da dama, Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya yi bayanin cewa duk wanda ya kashe kansa ta wata hanya, to zai dawwama a wutar jahannama ana azabtar da shi da wannan abin da ya kashe kansa din.

Misali akwai hadisin Sayyiduna Abu Hurairah (radhiyallahu anhu) wanda Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce:

"Duk wanda ya fado da kansa daga saman wani tsauni kuma ya kashe kansa, to hakanan zai kasance yana jefo da kansa awutar jahannama har abada.

Duk wanda yasha guba ya kashe kansa, to hakanan zai dawwama a wutar jahannama yana kwankwadar guba.

Wanda ya kashe kansa da wani Ƙarfe, to zai rike wannan Ƙarfen nasa a hannunsa yana chakawa a cikinsa a cikin wutar jahannama.

Sannan akwai wata ruwayar itama ta Bukhariy da Muslim din ce, daga Sayyiduna Thabitu bn Dhahhak, (radhiyallahu anhu) ya ce Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce:

"DUK WANDA YA KASHE KANSA DA WANI ABU, TO za a AZABTAR DA SHI DA WANNAN ABUN A RANAR ALƘIYAMAH".

Sai dai Malamai sun yi saɓani game da shin wanda ya kashe kansa, zai dawwama ne a wutar jahannama ko kuwa akwai ranar fitarsa?

Mafiya rinjaye sun ce kalmar "KHALIDAN MUKHALLADAN" da ta zo a cikin hadisan ba wai tana nufin dawwama ne har abada ba. A'a tana nufin dai za a yi musu azaba mai tsawo ne. Amma akwai ranar fitarsu.

Sun kafa hujjah da cewa ai laifin kashe kai ba shirka ba ne. Kuma shirka ne kaɗai laifin da Allah ya ce ba zai gafarta wa wanda ya mutu yana yinsa ba. Amma duk wani laifi komai girmansa Allah yana iya yafewa wanda ya aikatashi.

Sannan sun ce kalmar "KHALIDAN" din nan ba ta zo a cikin riwayar Imamul Bukhariy ba. A cikin riwayar Muslim ne kawai tazo. Kuma Bukhariy yana gaba da Muslim. Don haka malaman hadisi suke ganin cewar kalmar nan ba ta inganta ba.

Wasu malaman kuma suka ce an ambaci dawwama ne a cikin maganar domin a tsoratar da mutane kada su aikata laifin.

Amma dai abin da Maluman Ahlus Sunnah sukayi ittifaki ko ijma'i akansa shi ne duk wanda ya mutu bisa imani, to ba zai dawwama awuta ba. Komai girman laifin da ya mutu yana yi, in dai ba shirka ba ne, to akwai ranar fitarsa daga wuta.

WALLAHU A'ALAM.

ƘARIN BAYANI

Tambaya:

Wanda ya kashe kansa, shin zai dawwama ne a wutar Jahannama ko kuwa akwai wa’adin fitarsa?

Amsa:

Wa Alaikumus Salaam wa Rahmatullahi wa Barakatuhu.

Hakika kisan kai, ko kuma kashe kansa da gangan, babban zunubi ne a Musulunci. Allah Mai girma da ɗaukaka Ya haramta wa bayinsa yin haka, Ya ce:

القرآن الكريم – سورة النساء: 29

وَلَا تَقْتُلُوا أَنفُسَكُمْ إِنَّ اللَّهَ كَانَ بِكُمْ رَحِيمًا

Kada ku kashe kanku; lalle Allah Mai jin ƙai ne gareku.” (Surah An-Nisaa’: 29)

Manzon Allah ya bayyana a cikin hadisai cewa duk wanda ya kashe kansa ta wata hanya, zai fuskanci azaba daga Allah saboda wannan laifi. Misali:

حديث – صحيح البخاري و صحيح مسلم

Abu Hurairah (radhiyallahu anhu) ya ruwaito cewa Annabi ya ce:

Duk wanda ya fado daga wani wuri ya kashe kansa, zai dawwama a wutar Jahannama yana jefo da kansa. Duk wanda ya sha guba ya kashe kansa, zai dawwama a wuta yana kwankwadar guba. Duk wanda ya kashe kansa da wani ƙarfe, zai riƙe wannan ƙarfen a hannunsa yana chakawa a cikinsa a wutar Jahannama.”

Whoever kills himself with something, he will be punished with it on the Day of Resurrection.” (Sahih Muslim, Thabit bn Dhahhak, r.a.)

Wasu malamai sun yi saɓani akan ko wannan azaba za ta dawwama har abada ko kuwa akwai wa’adin fitarsa daga wuta.

Ra’ayin mafi rinjaye:

Kalmar “خَالِدًا (Khalidan – dawwama) da ta bayyana a cikin wasu hadisai ba lallai ta nufin har abada ba ce. Ana fassara ta ne a matsayin azaba mai tsanani da tsawo, amma Allah Mai Rahama yana iya gafarta wa wanda ya yi wannan zunubi idan ba ya cikin shirka.

Dalilin wannan ra’ayi:

1. Laifin kashe kai ba shirka ba ne, shirka shi kadai ne laifi da Allah Ya bayyana cewa ba zai gafarta wa wanda ya mutu a ciki ba. Duk wani laifi da mutum ya aikata, Allah yana iya gafarta wa wanda ya mutu bisa imani.

2. Riwayar da ta ambaci “Khalidan” ba ta zo a cikin Sahih Bukhari ba, sai a riwayar Muslim, kuma Bukhariy ya fi Muslim a matsayin ingancin riwaya. Wannan ya sa wasu malaman hadisai ke ganin cewa kalmar ba ta da tabbacin nuna dawwama har abada.

3. Wasu kuma sun ce an ambaci wannan hukunci ne don tsoratar da mutane daga aikata wannan babban zunubi.

Ittifaqin Ahlus Sunnah:

Duk wanda ya mutu cikin imani, ba zai dawwama a wutar Jahannama ba, komai girman zunubinsa. Idan laifin da ya aikata ba shirka ba ne, akwai wa’adin fitarsa daga wuta.

Wallahu A’lam.

 ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

WALLAHU A'ALAM.

https://t.me/TambayaDaAnsa

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments