HUKUNCIN WANDA YA KASHE KANSA BAYAN YA AIKATA LUWAƊI
TAMBAYA TA 3231
Assalamualaikum malan
Ina yini
Malam na ce idan
mutum ya aikata luwaɗi sannan ba a yi masa
hukunci ba sai ya kashe kansa
Me hukunci sa?
AMSA
Wa alaikumus salam wa
rahmatullahi wa barakatuhu.
Wanda ya aikata haka
tabbas ya aikata manyan laifuka guda uku wadanda ukubar da ke cikin kowannensu
mai girma ce.
Laifin farko shi ne
aikata luwaɗi. A cikin Alƙur'ani Allah ya ba mu
labarin cewa shi dai luwaɗi laifi ne mummuna
wanda babu wanda ya taɓa aikatashi a cikin
halittu baki ɗaya sai mutanen
Annabi Luut (alaihis salam). Harma a cikin Suratul Anbiya Allah ya ce
"HAKIKA SU MUTANEN BANZA NE FASIKAI".
Daga ƙarshe kuma Allah ya
fadi irin hallakar da ta samesu tun daga nan duniya. An kifar da su da garin
nasu, an yi musu ruwan duwatsun garwashin wutar jahannama.
Shi ya sa ma Manzon
Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce "ALLAH YA TSINE WA DUK WANDA YAKE
AIKATA IRIN AIKIN MUTANEN ANNABI LUUT (ya fada ya maimaita har sau uku). Imamu
Ahmad ne ya riwaitoshi).
Sayyiduna Abubakr da
Sayyiduna Aliy bn Abee Talib da Sayyiduna Khalid bn Waleed da Sayyiduna
Abdullahi bn Zubair sun ce wajibi ne haddin ɗan luwaɗi ya fi na mazinaci tsanani.
Kasancewar ba a yi
masa haddi ba, wannan ba zai zama dalilin da zaije ya kashe kansa ba. Domin
hakika kisan da ya yi wa kansa ba zai rage komai cikin azabar da Allah zai masa
ba. Hasali ma ya Ƙara aikata wani zunubin ne mafi muni daga wancan. Domin
banda shirka babu wani zunubin da ya kai kisan kai girma a wajen Allah.
A cikin Hadirhin Abu
Huraira wanda Imamul Bukhara da Muslim suka riwaito, Manzon Allah (Sallallahu
Alaihi Wasallam) ya ce:
"Duk wanda ya
gangarar da kansa daga kan wani dutse (Ko abu mai tudu) Kuma ya kashe kansa, to
hakanan zai rika jefo kansa zuwa cikin wutar jahannama har abada, kuma shi abin
dawwamarwa ne a cikinta har abada.
"Wanda kuma
yasha wata guba (poison) har ya kashe kansa, to wannan gubar za ta kasance a
hannunsa zai ci gaba da kurbarta a cikin wutar jahannama har abada, kuma shi
abun dawwamarwa ne a cikinta".
"Wanda ya kashe
kansa da wani karfe (kamar wuka ko takobi ko bindiga) To wannan makamin zai
kasance ahannunsa zai ci gaba da chakawa (ko yankawa ko harbawa) a cikinsa har
abada a cikin wutar jahannama kuma shi abun dawwamarwa ne a cikinta"
(Sahihul Bukhariy hadithi na 5442 da Sahihu
Muslim hadithi na 109).
Hakika babban dalilin
da zai kaishi ga jashe kansa ba zai wuce fidda tsammani daga samun rahamar
Allah ba. Kuma shi ma wannan babban laifi ne.
Sayyiduna Abdullahi
bn Abbas (radhiyal-Lahu anhuma) ya ce "Wani mutum ya tambayi Manzon Allah
(Sallallahu Alaihi Wasallam) cewa: "Ya Rasulallahi mene ne kaba'ira?
"
Sai ya ce "YIN
SHIRKA DA ALLAH DA FITAR DA TSAMMANI DAGA RAHAMAR ALLAH..."
Amma fa duk da haka
bai kafirta ba. Musulmi ne shi don haka ya halatta sauran Musulmai su yi masa
wanka su sallaceshi, kuma ya halatta ka yi masa addu'ar samun gafara da afuwar
Ubangiji.
WALLAHU A'ALAM.
ƘARIN BAYANI
Tambaya:
Mene ne hukuncin wanda ya kashe
kansa bayan ya aikata laifin luwaɗi?
Amsa:
Wa Alaikumus Salaam wa
Rahmatullahi wa Barakatuhu.
Wanda ya aikata wannan aiki,
tabbas ya aikata manyan laifuka guda uku, dukkaninsu manya ne a wajen Allah.
Laifi na farko shi ne aikata luwaɗi,
wanda Allah Ya bayyana a Alkur’ani a matsayin mummunan zunubi wanda babu wanda
ya taɓa aikatawa a
cikin halittu sai mutanen Annabi Lût (alaihis salam). Allah Ya ce:
القرآن الكريم – سورة الأنبياء: 74-75
وَأَهْلَ لُوطٍ إِذْ قَالُوا لَهُ أَخْرِجْ
قَوْمَكَ هَـٰذِهِ فِجْرَةٌ إِنَّهُمْ أُنَاسٌ يَسْعَوْنَ فِي الشَّهْوَةِ… فَجَعَلْنَا
الَّذِينَ آمَنُوا وَالَّذِينَ هَاجَرُوا فِي أَرْضِ الْبَرَارِي … وَأَهْلَكَ أُمَّهُمْ
فَجَعَلْنَاهُمْ غُثَاءً
“Kuma mutanen
Lût, sa’ad da suka ce masa: Fitar da mutanen ka! Lallai waɗannan mutane ne masu
zunubi, suna aikata abin banza… Sai Mu tsira da waɗanda suka yi Imani da waɗanda suka hijira, sai Mu
halaka mutanen su, Mun mayar da su garwashin ruwaya.” (Surah Al-Anbiyaa: 74-75)
Annabi ﷺ ya ce:
“Allah Ya
tsine wa duk wanda yake aikata irin aikin mutanen Annabi Lût.” (Riwayar Imam
Ahmad)
Laifi na biyu shi ne kashe kai,
wanda babban zunubi ne a Musulunci. Annabi ﷺ ya bayyana:
حديث – صحيح البخاري: 5442; صحيح مسلم: 109
“Duk wanda ya
gangarar da kansa daga wani dutse ko wani abu mai tudu, zai rika jefo kansa
cikin wutar Jahannama. Duk wanda ya sha guba har ya kashe kansa, zai rika riƙe
gubar a hannunsa a wutar Jahannama. Duk wanda ya kashe kansa da wani ƙarfe
(kamar wuka, takobi, ko bindiga), wannan makamin zai kasance a hannunsa yana
chakawa a cikinsa a wuta.”
Wannan ya nuna cewa kashe kai
babban zunubi ne, kuma yana kara zunubi ga wanda ya riga ya aikata babban
zunubi kamar luwaɗi.
Dalilin da yasa mutum zai iya
kaiwa ga wannan kisan kai shi ne fidda tsammani daga rahamar Allah, wanda shi
ne babban zunubi a Musulunci. Sayyiduna Abdullah ibn Abbas (radhiyallahu
anhuma) ya ruwaito cewa wani mutum ya tambayi Manzon Allah ﷺ:
“Ya
Rasulullah, menene kabairi (manyan zunubai)?”
Annabi ﷺ ya ce:
“Shirka da
Allah, da fitar da tsammani daga rahamar Allah.”
Ko da yake mutum ya aikata wannan
laifi, muddin ya mutu cikin imani, har yanzu musulmi ne, kuma ya halatta sauran
Musulmai su yi masa wanka, su yi sallarsa, su yi addu’a ga Allah ya gafarta
masa. Wannan yana nuna cewa duk da girman zunubi, Allah Mai Rahama yana da iko
ya gafarta wa bayinsa.
Wallahu A’lam.
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.