𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Mene ne yake kai ga a kashe Musulmi ko Wanda ba Musulmi ba a Shari’a?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Alhamdu lillah, Tsira
da Amincin Allah su tabbata ga shugabanmu Annabi Muhammad Sallallahu Alaihi
Wasallam.
Inna Lillahi wa inna
Ilaihi Raji’una, Lallai rai a gurin Allah tana da daraja kuma Allah ya haramta
kashe ta:
وَمَنْ يَقْتُلْ مُؤْمِنًا مُتَعَمِّدًا فَجَزَاؤُهُ جَهَنَّمُ خَالِدًا فِيهَا وَغَضِبَ اللَّهُ عَلَيْهِ وَلَعَنَهُ وَأَعَدَّ لَهُ عَذَابًا عَظِيمًا
Kuma wanda ya kashe
mumini da gangar, to sakamakonsa Wutar Jahannama ce, yana mai dawwama a
cikinta, kuma Allaah ya yi fushi da shi, kuma ya la’ance shi, kuma ya yi masa
tattalin azaba mai girma. (Surah An-Nisaa’: 93).
Hadisi ya inganta
daga Annabi Sallallahu Alaihi Wasallam Ya ce duk wanda ya taimaka wajen kashe
wata rai, to ba zai ji kanshin Aljanna ba ko ba zai samu rahamar Allah ba.
Hakika halin kunchi
da muke ciki a duniyar na je riya ta yau, baya rasa nasaba da kisan rayukan da
ba su ji ba, ba su gani ba. Allah ya shiryemu.
Rayuwar Musulmi da na
wanda ba Musulmi ba, duk rayuka ne masu alfarma a waje Allah SWT. Kuma Allah ya
hana kashe ko wace irin rai ne ba tare da hakki ba. A musulunci hukuma kaɗai takeda hurumin
kissa idan hukunci ya tabbata cewa mutum ya yi ɗaya daga abubuwa masu yawa, ga kaɗan daga cikin wanda
nassi ya zo da su:
1. Idan mutum ya
kashe wani kisan ganganci, to shi ma Shari’ah za ta kashe shi.
2. Idan mutum ya ba
da haɗin kai ko goyon baya
ko ya taimaka wajen kashe wani, kuma Shari’ah ta zartar masa da hukuncin kisa.
3. Ma-auraci kuma
ma-zinacin da Shari’ah ta yanke masa hunkun kisa.
4. Riddajen Musulmin
da Sari’ah ta yanke masa hukuncin ridda.
5. Ɗan fashin da shari’ah
ta zartar masa da hukuncin kisa.
6. Ɗan ta’addan
da ke kashe mutane da makami, bindiga, ko bam, ko kwaya da sauran muyagun
yanyoyin ta’addancin da Shari’ah
ta bayyana.
7. Mai Luwaɗi da wanda ake yin
luwaɗin da shi.
8. Mutumin da ya hana
zakka.
9. Mutumin da ya bar
Sallah.
10. Mutumin da ya yi tawaye
ga shugaban da al’umma suka yi wa Mubaya’ah.
11. Mutumin da ya
jakoranci tawaye ga shugaba.
12. Idan aka yi wa mutane
biyu Mubaya’ah, to akashe danyansu idan suka ki dai-daitawa.
13. Mutumin da ya
raba kan al’umma.
14. Mutumin da yake
fasadi kuma yana yaɗa shi abayan kasa.
A ƙarshe, dukkan abin da
hukuma ta yanke hukuncin kisa akai, to ya zamo dalili na kashe mutumin da ya
taka wannan hukunci. Allah shi ne mafi sani.
Ya Allah! Ka taimaki
shugabanni da hukumomi wajen tsare rayukan al’umma da dukiyar su. Amin.
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance damu cikin wannan group domin Fadakarwa...
ƘARIN BAYANI
Mene ne yake kai ga kashe mutum a Shari’a, ko Musulmi ne ko wanda ba Musulmi ba?
Amsa:
Alhamdulillahi, Tsira da Amincin
Allah su tabbata ga shugabanmu, Annabi Muhammad ﷺ.
Rayuwa ce daga cikin manyan ni’imomin Allah kuma tana da daraja sosai. Allah Ya
bayyana a cikin Alkur’ani cewa kashe rai ba tare da hujja ba haramun ne, kuma
yana ɗauke da hukunci mai tsanani:
القرآن
الكريم – سورة النساء: 93
وَمَنْ
يَقْتُلْ مُؤْمِنًا مُتَعَمِّدًا فَجَزَاؤُهُ جَهَنَّمُ خَالِدًا فِيهَا وَغَضِبَ
اللَّهُ عَلَيْهِ وَلَعَنَهُ وَأَعَدَّ لَهُ عَذَابًا عَظِيمًا
“Kuma wanda ya kashe mumini da ganganci, to sakamakonsa Wutar Jahannama ce,
yana mai dawwama a cikinta, kuma Allah ya yi fushi da shi, ya la’ance shi, kuma
Ya tanadar masa azaba mai girma.” (Surah An-Nisaa’: 93)
Hadisi daga Annabi Muhammad ﷺ ya ƙara tabbatar da girman wannan haramci:
عَنْ
أَبِي هُرَيْرَةَ رَضِيَ اللَّهُ عَنْهُ، قَالَ: قَالَ رَسُولُ اللَّهِ ﷺ:
"مَنْ يَقْتُلُ نَفْسًا فَلَا يَجِدُ رَائِحَةَ الْجَنَّةِ وَلَا يَرْحَمُهُ
اللَّهُ"
“Duk wanda ya taimaka wajen kashe
rai ba tare da hujja ba, ba zai ji kamshin Aljanna ba, kuma Allah ba zai yi
masa rahama ba.” (Sahih Bukhari da Muslim)
A Musulunci, rayuwar kowa – Musulmi
ko wanda ba Musulmi ba – tana da daraja. Allah Ya haramta kashe kowa ba tare da
hujja ba. Hukuncin kisa a Shari’a yana faruwa ne kawai lokacin da hujjoji suka
tabbatar da cewa mutum ya aikata wani laifi da nassoshi suka bayyana:
- Kisan ganganci: Idan
mutum ya kashe wani da gangan, Shari’a na ba da izinin hukuncin kisa.
- Taimako wajen kisa: Duk
wanda ya bada goyon baya ko ya taimaka wajen kashe mutum.
- Laifuka masu nasaba da zina ko rashin biyayya:
Misali, maza da mata masu yin zina da hukuncin kisa, ko wanda ya yi ridda
(taɓarɓarewar addini).
- Ta’addanci: Ɗan ta’addan da ke kashe
mutane da makami, bam, ko kwayoyi.
- Fasadi a ƙasa: Mutanen da ke yada fitina,
hana zakka, barin sallah, ko raba kan al’umma.
Wannan tsarin hukunci yana nuna cewa
Shari’a ba ta yarda da kashe rai ba tare da adalci ba, kuma duk wanda aka yanke
masa hukuncin kisa bisa Shari’a, wannan ne kawai dalilin da zai sa a kashe shi.
Daga karshe, muna roƙon Allah:
“Ya Allah! Ka taimaki shugabanni da
hukumomi wajen kare rayukan al’umma da dukiyarsu, Ka tsare mu daga zalunci da
rashin adalci. Amin.”
Rayuwar ɗan Adam babban amanar Allah
ce. Duk wani yunkuri na kashe mutum ba bisa ka’ida ba babban zunubi ne kuma
yana kai mutum zuwa fushin Allah da azaba mai girma.
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.