Nana Aicha Hamissou (2023). Wanda Bai Ji Bari Ba…. Ɗaukar Jinka (Labaran Da Suka Samu Nasara A Gasar Gajerun Labarai Ta Arc. Ahmed Musa Dangiwa, 2022). Kangiwa Multimedia and Communication Company LTD
WANDA
BAI JI BARI BA...
Na
Nana
Aicha Hamissou
Tun
daren jiya da na yi tozali da taliya gidan Hajiya Marka, yawuna yake tsinkewa,
harshena ya kwaɗaitu da ɗanɗana
ta, sai dai kash! Tsabar rowarta sai dawowa gida na yi ina haɗiyar
yawu, duk yadda nake muradin ta. Ladar wankin da na shafe awanni ina yi, sai ƙarshen wata za a ba ni ballatana na sayo
taliyar da kuɗin. Ga shi ba ni da ko sisi, ko wata
kadarar da zan bayar a musanya mini da taliya. Mamaki! Kwalli a kunne. Ni da
taliya ba ta sha mini kai ba, nake haɗa
yawu a kanta, lallai da walakin gishiri a ruwa.
Kawar
da mamakina na yi ta hanyar yafa gyalena ina ficewa daga ɗaki,
a falo na tarar da Habib yana latsa waya. Kallo guda na yi masa na kawar da kai
haɗe da
ficewa, ba tare da na amsa tambayar da yake yi mini ba akan inda zan tafi.
Haushinsa ya cika mini zuciya, da a ce ya tashi tsaye ya nemi na kansa har ni
Maryam Alhaji Mansur taliya za ta gagara?
Kaina
na ji yana sara mini tamkar zai fashe, na dafe shi ina tunanin rashin shan haɗin
da na saba yi ne ya haifar mini shi, wanda matsalar kuɗi ce
ta yi mini shamaki ga muradin nawa.
Ina
kaiwa daidai shagon Ɗan-Sala
na ja gefe ina jiran mutane su ragu, kafin na je masa da kokon barata kamar
yadda na saba. Bayan ya ba ni bashin sirof, na shanye shi tas tun a hanya.
Sannan na yi gaba zuwa gidan Alhaji Na-Hantsi, ɗayan
gidan da nake musu wanki, ko zan samu wani abu cikin albashina.
Ban
san me ya sake faruwa ba, sai tsintar kaina na yi a gadon asibiti, hannuna da ƙarin ruwa. Ko ranar da iyayena suka rasu
ban yi irin kukan da na yi yau ba, sakamakon abin da ya yi silar tsintar kaina
a asibiti da aka sanar da ni. Watau shigata falon gidan santsi ya kwashe ni na
zube sai jini aka ga yana bin ƙafafuwana,
dalilin da ya sa aka kawo ni asibiti. A nan aka tabbatar da ɓarin
ciki na yi sakamakon faɗuwar. Silar shan kayan maye
na yi asarar gudan jinina wanda na shafe shekaru ina nema, wanda nake tunanin
zai yi mini addu’a bayan ƙasa
ta rufe idona.
Na
same shi a lokacin da na yanke tsammani, sai dai rashin sani ya fi dare duhu.
Ban san ina da juna biyu ba, ban san yaya aka yi na kasa ganewa ba. Sai yanzu
da lokaci ya ƙure mini ƙwaƙwalwata
take tuno mini ƙwaɗayin
taliyar da nake yi yana da alaƙa da
cikin. Ban taɓa nadamar auren Habib ba sai yau, ban taɓa
jin tsanar shi ba kamar yau. Shi ne silar jefa ni cikin ƙaddararriyar rayuwa wacce ko maƙiyina ba na yi wa fatan irinta. Abin da
ya fi damu na a halin yanzu shi ne zubewar cikina, yaya zan yi ya dawo? Ba zai
yiyu ba jirgin ƙasa
saman gajimare, hannun agogo ba zai taɓa
dawowa baya ba. Wanda ya tuna bara, bai ji daɗin
bana ba, na yarda da azancin nan saboda ko kaɗan
ba ni son tuna rayuwata ta baya, sakamakon irin gatan da na taso cikinsa amma ƙaddararren auren Habib ya sauya mini
rayuwa daga haske zuwa duhu. Silarsa na aikata babban zunubin da ba zan iya
yafe wa kaina ba. Shafa cikina na yi ina fashewa da kuka, hawaye suna ambaliya
daga ƙoramar idanuwana suna gangarowa saman
kuncina. Radaɗi da zugin da jikina yake mini, ba su
kai kwatar zafin da nake ji a zuciyata ba sa’ilin da nake tuna rayuwata, daga
lokacin da ƙaddara ta haɗa ni
inuwa guda da Habib a matsayin ma’aurata.
Kamar
yadda na samu labari, Habib da kuɗin
gadon wajen mahaifinsa ya aure ni, aka sha biki na kece-raini. Yana tunanin
bayan aure zai samu aikin ofis. Sai dai aiki ya ce ɗauke
ni inda ka ajiye ni, duk inda yake tunanin zai samu aiki ya je amma magana ɗaya
ce ɗan
wuta ya ga kafiri. Maimakon ya fara sana’ar hannu sai ya yi kunnen uwar-shegu
da zancen sana’a. Ba shi da wata magana sai tunanin aikin ofis saboda yana da
kyakyawan sakamako.
Abin
da ya kasa ganewa akwai waɗanda suka zarta shi
kyakkyawan sakamako, suna kasuwanci ko aikin ƙarfi,
ba su yi kwance sai an kashe an ba su ba balle takaici ya kashe su. Kullum sai
ya fita nema ko zai dace amma tamkar an aiki loma kewayar moƙoshi. Kasancewar ina aikina sai ya
zamana ni ce na ci gaba da jan ragamar gidanmu bayan kuɗin
hannunsa da garar aure sun ƙare.
Ina
da shekara biyu da aure iyayena suka samu hatsarin mota suka rasu. Bayan an ba
ni gadona gabaɗaya na damƙa
masa, burina ya fara juya su ko kukanmu zai ƙare.
Don albashina ba wani isar mu yake yi ba, don ma ban haihu ba har a lokacin, da
abin sai ya yi mana yawa. Tiryan-tiryan na yi masa bayanin abin da nake so a yi
da dukiyar, watau sayar da kayan masarufi da kayan miya. Na yi masa bayanin
sana’a ce wacce ko ba mu yi
ciniki ba, muna iya ɗauka ciki mu ciyar da kanmu.
Ballatana mai sana’ar kayan miya rana ba za ta taɓa
fitowa ta faɗi ba tare ya yi ciniki ba.
Yini
guda cur ya kwashe a waje, ina tunanin yana can kasuwa yana sayayyar sai dai me
zai faru? Dila guda ta kaya ya shigo da ita irin su shaddodi; yadi; kayan ado
na maza da sauran su. Mamaki ya hana ni magana har ya gama buɗe
kayan, ido ne nawa ba tare da na ce uffan ba. Don ba haka na so ba, ra’ayina
sana’ar kayan masarufi amma ya ɓige da saɓanin
ra’ayin nawa.
Cikin
wani irin yanayi nake tuhumarsa akan me ya sa zai yi hakan? Waɗannan
kayan ba su da wani ciniki na a-zo-a-gani a zamanin da muke ciki, me ya sa ya ƙi amfani da shawarata akan sayo kayan
masarufi kamar yadda na yi masa bayani? Wani ƙululun
bakinciki ya samu matsuguni a ma’adanar
sirrina sakamakon amsar da ya ba ni wacce ta shayar da ni gubar mamaki. Wai
kayan jiki ne ya sayo masu kyau da tsada, idan ya ɗinka
su yana zuwa neman aiki ba zai sha wahalar samu ba.
Za a
yi tunanin ɗan wani ne shi, da ma an fi hana ‘ya’yan
talakawa aiki. Saura kaɗan na zube ƙasa lokacin da yake sanar da ni bahagon
hangensa. Ko kaɗan bai kula da yanayin
fuskata ba, ya nuna mini sabuwar waya ƙirar
iPhone, yana sanar da ni idan ana ganin sa da ita zai samu aiki, saboda tsadar
wayar kuma ba kowa ya san ta ba. Ban gama shan mamaki ba sai da ya sake nuna
mini makullin mota, yana faɗa mini su ne abin da sayo da
kuɗin,
ya san zuwa wannan lokacin babu wata ma’aikata da za a gan sa da mota a hana
shi aiki.
Tsabar
takaici ban kalle shi ba na shige ɗaki
ina mamakin rayuwarsa, mutum har mutum amma ya ɗauki
burin duniya ya ɗora shi ga aikin ofis? Aikin
da in har kana da ƙwaƙwaran sana’ar da za ka tsaya da kafafuwanka ta fiye maka
shi, kodayake ya riga da ya kurumce sai fatan Ubangiji Ya taro shi. Dayake ya
yi mugun ba ni haushi ko kuɗin da ya kashe ban tambaye
shi ba, shi ɗin ma bai ce mini komai ba sai faman kiɗansa
da rawarsa yake yi.
Haka
ya fara fita da sabbin kaya da takardun karatu a hannu. Nan nake jira na ji ya
samu aiki amma tsit kamar Malam ya ci shirwa. A haka aka kuma kwashe wasu
shekaru lokacin sabbin kayan da yake tunƙaho
yana da su sun fara tsufa, kuma ya daina fita a-kai-a-kai neman aiki, hatta
motar ba kullum yake fita da ita ba saboda ba ruwa zai tayar da ita ba. Dukiyar
gadona miliyoyin kuɗi ta lalace cikin lokaci ƙanƙane.
Abu biyu kaɗai na fita da su gidan da muke ciki
wanda na ci gadonsa sai firij da na saya ina sayar da zobo.
Watarana
na tashi ba kuɗi sosai a hannuna, sakamakon kwana biyu
ba mu samun wuta ba, ban samu na yi zobo ba, ga kuma wata ya yi nisa. Kuɗin
motar tafiya aiki kaɗai nake da, na yi latti
ballatana na tafi a ƙafa
idan na dawo na hau mota. Babu yadda na iya na tafi a mota, a hanyar dawowata
ban ankara ba sai na ji an yi sama-sama da ni an zube ƙasa, mai mashin ya kaɗe
ni. Babu tsoron Allah haka ya ɓace wa ganina, a galabaice
aka samu wasu suka tafi asibiti da ni. Bayan gwaje-gwaje aka tabbatar na karye
a ƙafa sai an mini ɗori.
Tashin hankali! Wanda ba a sa masa rana! Haka Habib ya shiga fafutukar neman
inda zai samu kuɗi, mahaifiyarsa ba ta da
shi, ita ma ta kanta take yi. Shi ne babba kuma bai nema ba balle ya amfane su.
A haka na wuni ba a yi mini aiki ba, azaba ta addabe ni. Ni kuma dangina ban
neme su ba bayan na samu gadona bare na nemi taimakonsu. Sai washegari ya samo
kuɗi
aka yi mini aiki. Ban tambaye shi inda ya samo ba don a lokacin burina na samu
waraka.
Haka
muka ci gaba da jinya a asibiti, har aka sallamo mu. Washegarin ranar da aka
sallamo mu tun da safe ina kwance nake jin hayaniya, cikin matuƙar tsoro na ji yara suna ihun ‘yansanda sun tafi da Habib.
Tashin hankali! Faɗa da maigari ranar salla!
Ina zan sa kaina? Duk iya tunanina amma ban hasaso abin da zai sa a kama shi
ba. Haka na wuni na kwana cikin ƙunci,
da ƙunar zuciya ina tunanin mijina. Ban sake
tozali da shi ba sai bayan kwana biyu, shi ɗin
ma tare da ‘yansanda ne ya shigo. Kai tsaye ɗakinsa
ya wuce, bai jima ciki ba suka kuma tafiya ba tare da sun ce mini ci kanki ba.
Ban
sake tozali da shi ba sai da yamma, a nan yake sanar mini kuɗin
da aka yi mini aikin asibiti ne ya ranta. Mutumin ne ya kai sa ofishin
‘yansanda, yanzu motarsa aka sayar a wulakance aka biya shi kuɗinsa.
Na yi kuka sosai cikin tausaya wa mijina, da kuma taurin kai irin nasa. Sauran
kuɗin
da suka rage na motar na ba shi shawarar me zai hana ya saro kayan miya ko
cikin gida mu riƙa
sayarwa? Amma dayake har a lokacin bai saduda ba sai ya shafa wa idonsa toka ya
ƙi ɗaukar
maganata, a cewarsa ba zai iya sana’ar nan ba. Babbar damuwata albashina ya
tsaya tun da ba aikin gwamnati ba ne, balle na ci gaba da ɗauka
har zuwa lokacin da zan ji sauki. A haka muka dawo da rayuwa yau daɗi
gobe godiyar Ubangiji, watarana mu ci watarana sai mu yi kwana biyu ba mu ci
ba. Ga shi ina jinyar ɗori ya kamata a kula da ni
amma ban samun wata kulawa ta a-zo-a-gani ba, don daga kwance nake haɗa
zobo shi kuma ya saka a firij.
Bayan
shafe watanni kwance na koma ma’aikatar da nake aiki suka ba ni haƙuri sun samu madadina, ba zai yiyu a bar
wuri ba kowa ba, saboda kamfanin aika kuɗaɗe ne
na gari-gari da ƙasa-ƙasa. A hanyar dawowa saura kaɗan a kaɗe ni
saboda tsabar rashin nutsuwa. Sai ga ni da kuka
a hanya kamar wacce aka yi wa mutuwa. Da na iso gida kuka na fashe wa Habib da
shi akan lallai sai ya fara sana’a amma haka ya kalallame ni da romon baka da kalamansa na
yaudara, wai na ci gaba da yi masa addu’a wataran sai labari, yana ji a jikinsa
zai samu aiki. Babu yadda na iya na zuba wa sarautar Allah ido. Babu iyayena
balle na kai musu kokon barata su taimake ni, sauran dangina kuwa ban kula da
su ba bayan na samu gadona balle na tunkare su. Ga shi mu biyu ne a wajen
iyayenmu, yayata tana ƙasar
waje ita da mijinta. Ko labarinta na daina samu tun da ba waya a hannuna.
Tun
daga wannan ranar abubuwan da suka haskaka rayuwata suka fara gushewa, wani
duhu ya fara mamaye ta. Babu yadda ban yi da Habib ba akan ya sayar da iPhone ɗinsa,
amma ya ƙi. Sai dai mu kwana da yunwa ina ji ina
gani ga kadarar da za mu iya sayarwa amma Habib ya ce bai san zancen ba. Ai
kuwa olsa ta kayar da shi har da zaman asibiti na kwana biyu.
Muna
can asibitin aka shigo aka sace mana firij ɗin
da muke taƙama da ita, wanda shi
kaɗai
ya yi mini sauran da zan bugi ƙirji
in ce ina da shi. Allah da ikonSa wani yana rabon zakka ya biya mana kuɗin
asibiti. Muka dawo gida aka ɗora daga inda aka tsaya.
Yunwa ta riga da zame mana jiki. Ganin zan cuci kaina, da raina da lafiyata na
fara aikatau. Idan na yi shara da wanke-wanke a ba ni abinci na zo gida da shi,
tamkar mayunwatan zaki haka muka dawo, nakan sha mamaki da tunanin wai ni ce
Maryam nake aikatau? Silar auren mai dogon buri? Kasancewar abincin da suke ba
ni ba ya isar mu sai na koma neman wankau.
Na
samu wankin sai dai ba nan gizo ke saƙa
ba, ban iya aikin wahala ba don ko a gidanmu ba na wanki, gidan aure ne na fara
yi. Idan na yi wanki sai na sha wahala, ga rashin sabo ga kuma wulakanci da
nake sha a wurin masu gida. Ba na mancewa watarana na yi wa yaran gidan wanki,
ina tsaka da guga sai ga budurwar gidan ta watso mini kayan a ka tana masifa
akan lallai sai na biya ta leshinta, don tsabar na raina ta dauɗa
kawai na jiƙa mata a kaya ga shi
leshinta daga ƙasar waje aka sayo
mata shi. Inda take shiga ba nan take fita ba. Ban iya ba ta amsa ba sai kallon
ta nake yi zuciyata tana bugawa da ƙarfi,
ƙwaƙwalwata
tana faman tariyo mini rayuwata ta baya.
Ni
Maryam ake yi wa cin mutumci don ina aiki ƙarƙashin inuwar wasu. Tsabar na cika da
mamaki ina kallon ta har na ƙone
musu kaya ba tare da na kula ba sai ƙauri
da muka ji yana tashi. Sababi! In ji Arawa! Nan wata rigima ta ƙara sarƙewa
sai da na ƙwammace kiɗa da
karatu, wulakanci dami-dami, cin mutumci ba wanda ban sha ba. Babban tashin
hankalina gabaɗaya kuɗin
aikina na wata suka ce za su fanshi kuɗin
kayansu da na ƙone, sannan kafin na
baro gidan sai da na sake wanke leshin yarinyar ina wankin ina kuka mai cin
rai. Zuciyata sai tafarfasa take yi, na san a lokacin da za a auna ni babu abin
da zai hana sakamakon gwajin nuna hawan jini, tsabar damuwa da ta lulluɓe
ma’adanar sirrina.
A
hanyar komawa gida nake bayyana wa Maraliya mai aikin gidan, rashin sabo ne ya
sa nake shan wahala. Ta ba ni shawarar na sayi magani na riƙa sha, zan yi ta aiki ba tare da na gaji
ba kamar jaka. Babu ɓata lokaci na fara amfani da
ƙwayoyi, sai ga shi wanki komai yawansa
nakan yi shi ba tare da na gaji ba. Tun ina shan ƙwayoyi
har na fara ta’amalli
da sirof waɗanda suke sanya maye, ban damu ba ko kaɗan
saboda ina samun kuɗi, gwanjon sutura sannan ina
ci ina koshi.
Na
ci gaba da wankau ba kama hannun yaro, sai dai matuƙar ban sha magani ba za a samu gagarumar
matsala. Saboda zuwa lokacin ya riga da zame mini jiki. Idan ba ni da kuɗi
nakan je amsar bashi wurin mai sayarwa.
Wataran
bayan farkawa daga barci na tsinci kaina a farfajiyar gidan aikina, jikina ciwo
tamkar an ɗora mini duwatsu saman sa, kayan jikina
duk sun yi baje-baje da ƙasa.
Na rasa me ya same ni don haka sai na miƙe a
tsorace da nufin shiga falon gidan, kafin na isa maigadi ya ƙwala mini kira. Ina zuwa yake sanar da
ni kar na kuskura na shiga ciki, idan ina son lafiyar jikina, dukan da zan sha
sai ya fi wanda suka yi mini da farko. Kallon mamaki nake yi masa tamkar
shashasha, ganin irin kallon da nake masa ne ya sanar da ni abin da ya faru.
Amai na kila
saman kujeru ga shi suna da manyan baƙi,
dalilin da ya sa suka yi mini dukan kawo-wuƙa.
Hawaye ne suka ci gaba da ambaliya daga idanuwana, zuciyata ta fara raɗaɗi da
zafi kamar za ta ƙone.
Sai a lokacin ƙwaƙwalwata ta fara tariyo mini baya.
Tabbas
sun sanar da ni za su yi baƙi,
na kama wa mai aikinsu sharar falo, ni kuma lokacin na sha haɗin
da na saba. Da wannan na fara sharar falon kaina yana juyawa ban sake sanin
abin da ya faru ba sai da na tsinci kaina a farfajiya. Hawaye na goge ina yi wa
maigadi godiya sannan na bar gidan. Bayan kwana biyu na koma gidan ko sun huce
amma sai na iske har sun samu wata mai wankin, na buƙaci kuɗina
suka hana ni wai sun biya an wanke musu kujerun da na ɓata.
Lallai na tabbatar matar gidan ba ta da kirki, da tana da shi ba za ta biye wa
yaranta su tafka mini rashin mutumci ba. Haka na dawo gida ina jin zafi a
zuciyata. A lokacin muka sake komawa ‘yar gidan jiya, gudun yunwa ta sake
hallaka ni na sayar da gadona, na kwaso kayan abinci.
Har
zuwa wannan lokacin Habib bai saduda ba, ba shi da wani aiki face ya kwanta ya
yi wanka ya kai wayarsa wajen caji. Don wutar ma mun jima ba mu da ita, rashin
kuɗi ya
sa aka yanke mana ita da daɗewa.
Tuni
na yi wuri na ajiye Habib, babbar damuwata ita ce na samu haihuwa. Na samu
wanda zai rarrashe ni idan ina cikin damuwa, wanda zai mini nasiha, saboda
Habib bai taɓa damuwa da halin da nake ciki ba, duk
da yana da masaniya akan komai. Babbar damuwarsa aikin ofis wanda har lokacin
bai yanke tsammani ba.
Bayan
wani lokaci, abincinmu ya ƙare
na sake shiga damuwa, ga yunwa ga kuma rashin kuɗin
kayan maye. Matuƙar
ban sha haɗina ba kaina zai kama ciwo kamar zai
tarwatse. Aladole na sake neman aiki, na samu gidan Hajiya Asabe. Kafin wata ya
mutu nakan saci kuɗinta don lokacin na kai maƙura game da shaye-shaye.
Abin
yana damu na amma ba yadda zan yi, don ita kaɗai
ce mafita a gare ni. Ranar da ta yi tozali da ni a ofishin ‘yansanda na kwana,
an gana mini azaba, sosai aka sauya mini kamanni kamar ba Maryam ba, sai da suka zubar mini
da haƙora biyu na gaba. Duk yadda Habib zai
yi, ya yi an ƙi fitar da ni, don
babban sharri suka ɗora mini, wai sarƙar gwal na sata. Babu yadda Habib ya iya
ya sayar da wayarsa da katifarmu, ya biya kuɗin
da suka gindaya aka sallamo ni muka dawo gida, na kama jinyar jikina.
Ban
daddara na kuma komawa neman aiki ido rufe, saboda na kai maƙura game da shan haɗina,
ba zan iya bari ba, ban jin akwai abin da zai hana ni sha. Lokaci guda na samu
wankau gida biyu. Gidan Hajiya Marka da gidan Alhaji Na-Hantsi. Bayan ƙarewar wata na karɓi
albashina da ɗan nauyi, sai na ajiye su saboda buƙata. Na duba zan ɗan
tsakura don sayen haɗina, kuɗi
suka ce ɗauke
ni inda kika ajiye mu. Sai ganin Habib na yi da waya, shakka babu su ne ya ɗauka,
babu tausayi ko jinƙai.
Kallon sa kawai na yi don na rasa abin da zan ce masa.
Hajiya
Marka mace ce mai rowar tsiya, ba a cin abin hannunta, wani lokacin albashina
har sai na tambaya da kaina. Yinin jiya a can na shafe sa ina wanki. Ina kallo
tana girki, har ta sanya ni duba mata tukunya a lokacin da ta yi baƙuwa. Sai faman haɗa
yawu nake yi ina son ci, haka ta sauke suka ci ita da baƙuwarta ba ta zuba mini ba.
Sai
ma ƙoƙarin
kora ta daga falon ta yi tana faɗa
mini gobe na zo da wuri na ƙarasa
sauran wankin. Haka na dawo gida ina haɗa
yawu, har na kwana ina tunanin taliyar. Dalilin da ya sa na fita neman kuɗin
saya na mayar da yawuna, wannan ƙaddarar
ta afka mini.
Runtse
idanuwana na yi zuciyata na ci gaba da tafarfasa. Ina jin yadda Habib yake yi
mini sannu amma ko kallo bai ishe ni ba. Ba ni da burin da ya wuce ya sawwake
mini, ko da zan ƙare
rayuwata ni kaɗai. Aurensa babu abin da ya tsinana mini
sai tarin nadama da da-na-sani. Likita ta shigo tana yi mini bayanin irin
rashin lafiyar da na kamu da ita, hatta mahaifata ta samu matsala, na kuma kamu
da rashin lafiya mai tsanani silar shaye-shaye, sannan jinina ya yi ƙololuwar hawa. Don haka ya rage nawa,
idan zan ci gaba da yi matsalata ce.
Da
wannan na roki alfarmar ta ba ni sallama, amma ta hana ni a cewarta sai na ƙara samun sauƙi. Tana barin ɗakin
ita da Habib na cika bujena da iska na bar asibitin. Ban jima da zuwa gida ba
sai ga Habib. Babu ɓata lokaci na fara sauke
masa rashin mutumci kwando-kwando, na umarci ya sawwake mini, ya bar mini
gidana idan kuwa ya ƙi
hukuma ce za ta raba ni da shi.
Ban
taɓa
ganin shi cikin tashin hankali ba kamar yau. Kuka wi-wi yake akan na gafarta
masa, kowacce irin sana’a nake so ya amince zai yi. Tamkar gunki haka na zama,
don idan mutumin da ke yi wa hoto magana ya amsa, ni ma na amsa masa. Tuban
Habib tuban muzuru ne da ɗan-tsaƙo a baki. Na ci gaba da masifa ina faɗin
duk inda yayata take a faɗin duniyar nan zan neme ta,
ta taimaka mini ya sake ni ko a kama shi. Kuka ya ci gaba da rera mini kamar
sabuwar amarya, ni kam ko sauraren sa ban yi ba, sai ma ɗaki
na shige ina sake jaddada masa awa uku kacal na ba shi ya sawwake mini.
Da yake
ba isasshiyar lafiya ce da ni ba, ina nan ina wasikar jaki barci ya sace ni.
Ina farkawa kai tsaye falo na dawo na yi masa tsaye a ka ina sake jadadda masa
bukatata. Sam ban lura da ledojin da suke zube a falo ba sai da ya nuna mini su
yana sanar da ni kayan miya ne ya saro, wayar hannunsa ya sayar, da kuma sauran
suturunsa kusan rabi ya yi gwanjon su ya saro kayan miya. Ko kaɗan
bai birge ni ba, don ya jima da ɓata
rawarsa da tsalle. Sake matsa masa na yi amma bai bi ta kaina ba sai ficewa ya
yi da kayan daga falon, yana kaiwa ƙofar
gida.
Kewar
yayata ta cika mini zuciya, sosai nake buƙatar
ta a kusa da ni. Burina na yi tozali da ita, domin ta share mini hawayena. Na
shafe kwanaki ina nazarin yadda zan neme ta, wata dabara ta faɗo
mini na ari wayar maƙwafciyarmu
na neme ta a fesbuk, Allah da ikonSa na same ta. Cikin kuka nake zayyane mata
abubuwan da suka faru da ni. Ba a ɗauki
lokaci mai tsayi ba ta aiko mini da kuɗi na
tafi asibiti aka duba lafiyata, tare da saka mini haƙora. Kuma ta ba ni jari na kama sana’a.
Rayuwarmu da Habib ta dawo ba yabo ba fallasa. Idan na tuna yadda na biye masa muka nakasa dukiyata, ina jin haushi sosai a raina. Kodayake mun ga ishara da aya ƙarara, don sana’ar da ya ƙi yi da dukiya mai yawa, ita ce yake yi da kuɗi ƙalilan. Lallai Wanda Bai Ji Bari Ba, Zai Ji Hoho!
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.