Ticker

6/recent/ticker-posts

Kaddarata

Ahmad Muhammad Adam (2023). Kaddarata. Ɗaukar Jinka (Labaran Da Suka Samu Nasara A Gasar Gajerun Labarai Ta Arc. Ahmed Musa Dangiwa, 2022). Kangiwa Multimedia and Communication Company LTD

ƘADDARATA

Na

Ahmad Muhammad Adam

Kuka ta ke mai taɓa rai har shiɗewa ta ke ƙoƙarin yi, ta share hawaye ta ce,” Haba Abban Sajida, shaye-shaye ba na ka bane, kana da ‘ya’ya fa, amma ka...”Cikin zafin rai ya ɗauke ta da mari, cikin maye ya ce,”Ba zan de na ba, ki fita daga lamura na na faɗa miki, in ba haka ba wallahi ni ne ajalin ki”. Yasa ƙafa ya fice da ga ɗakin ba tare da sake sauraron ta ba.

Salima mace mai haƙuri, inda sabo ta saba da halin Musa, yadda ya maida shaye-shaye abokin rayuwa, ba dare ba rana, duk da cewa yanzu da ɗan sauƙi tunda ko ya ya ne yana fita yin buga bugarshi, Wata rana in an samu kuɗin a kawo a aci da haƙuri, watarana kuwa abin da ya samo ko gida bai kawo shi, sai dai ya ƙarar da shi a can wurin shaye-shayenshi.

Tabbas da mahaifiyar Salima na raye abubuwa za suyi mata sauƙi, ta san ko ta koma wurin mahaifinta, iya bala’in da matar mahaifin na ta ke da shi ba zai bari a taimaka mata ba, amma kuma dole ta je dan kuwa tun jiya basu ci komai ba, yau ma haka Musa ya fita bai bar mata komai ba sai dan karan duka da ya naɗa mata.

Haka ta nufi gidan su ci ke da fargabar abin da zai je ya zo,da sallama ta fa ɗa cikin gidan, ba ta ƙarasa sallamar ba, su kayi iɗo huɗu da matar babanta, kai tsaye ta fara faɗin “To ‘yar jaraba, yaushe garin ya waye har kin biyo duhun asuba, to maza ja tsummar rayuwarki ki ban wuri, muma yau haka muka tashi malam naira tamanin ya ban ya ce na yi haƙuri da shi kuma...”. Cikin ladabi Salima ta ce, “Baba Attine ina kwana” ta juya kanta can da yatsine ta ce” lafiya” Yadda baba Attine ta yi ne ya sa Salima cewa, “dama wucewa zan yi nace bari nazo mu gaisa”.Tana gama faɗin hakan fita ta yi zuciyar ta kamar ta haɗiyi ruwan dalma.

Fitowa tayi ba tare da sanin inda za ta je ba, zuciyar ta kuwa tunani ta ke, da ace mijin ta ya zama kamar kowane nagartaccen namiji, da bata tsinci kanta cikin wannan yana yin mara daɗi ba, da ya maida hankali sosai a sana’ar shi,da komai yazo mata da sauƙi.Ita ba kanta ta ke dubawa ba, illa yaran ta guda biyu, shin wacce kalar rayuwa za suyi, dukkan tarbiya tana tabbatuwa ne a inda uba ya jajirce a gidansa, ya sauke dukkan haƙƙoƙin da Allah ya ɗora masa, ya tsaya, tsayuwa irin ta daka dan ganin mutuncinsa dana iyalansa basu tagayyara ba, to amma ita bata da zaɓi tunda haka shi ne ƙaddararta, kuma tana fatan Allah ya dube ta ya kawo mata mafita.

Ba ta yi aune ba, wata mota ta shawo kwana kamar zata kifar da ita, matuƙin motar ya fito a sukwane cikin fushi ya kwaɗa mata mari, ya ce, “Ke wacce irin mara hankali ce, Hon biyar na miki amma kin ƙi kaucewa.

Wani da ke kusa da shi yace, “ Tunanin ta na banza da wofi mana, ƙila ma cikin maye take” Salima bata saurare su ba ta wuce, tana faɗin sanadin shaye-shaye ne ya sani cikin wannan ƙaddarar.

Gida ta nufa, tun da ba abin da ya fi dacewa da ita illa ta koma gidan. Ahmad ƙaramin ɗanta ta gani a kwance, yunwa sosai ya ke ji, ta rungume shi tana faɗin, “ Allah ya na tare da masu haƙuri, kuma baya tauyewa masu kyautatawa” Sallama taji ɗan maƙotansu ya ce “wai umman mu ce ta ce na kawowa Ahmad abinci” Da sauri Salima ta fito daga ɗaki ta karɓi abincin tana godiya, a yadda taga yawan abincin tasan bawai Ahmad ake nufin bawa ba, ta ƙara godewa Allah san nan suka ci abincin suka ƙoshi, a ranta tace an gama da wannan sai kuma wani.

Ana magriba Musa ya shigo da baƙar ledar dake hannunsa, taliya ce guda ɗaya dame ɗanɗano, ya faɗa cikin nutsuwa. “Salima ayi haƙuri da wannan”. Murmushi tayi tace “ ba komai Allah ya ƙara buɗi”. Ta tashi ta nufi inda mangal ya ke, dama da sauran gawayin shekaran jiya, ta dafa musu taliya ta kawo musu.

Yana fara cin abincin ta ce, “Kai miji na ne, kuma so da ƙauna ya sa na aure ka, ban da uwa. Kuma kasan halin baba Attine, ka duba yanayina da na yaran nan ka daina shaye-shaye, ba abin da zai anfanar dakai a duniya da kuma lahira, illolin da shaye-shaye ke haifar wa sun fi dukkanin yadda mai tunani zai yi, kana cutar da cikin jikin ka, duk wanda ke kusa da kai yana cutuwa, ga zubewar mutunci, abin haushin masu safarar miyagun ƙwayoyin nan sun killace na su iyalan saboda sun san illar abin, shin me yasa zaka sayi abin da zai juya ma ƙwaƙwalwa da kanka?

Duk wanda ka ganshi ya na hauka, Allah ne ya jarabce shi kuma in san samun sane da dangin sa to Allah ya bashi lafiya, to dan me kai zaka sayi haukan da kanka, wace rib ce a cikin shaye-shaye, miji na ne kai, ina sanka ina san ka dubi rayuwar yaran mu a nan gaba kuma ka...” kuka ya ƙwace mata, jikin shi ya yi sanyi ya kuma mata alkawarim bazai kara shan komai ba.

Sati ɗaya, kullum ya na fita buga bugar sa. Ranar wata alhamis ya dawo gidan cikin maye, Sajida ta tafi da gudu tana oyoyo baba, cikin maye ya kalli ‘yar ta sa ya ce “Ni ki ke zagi?” Ya ɗauke ta da mari ya hankaɗata gefen tsohuwar rijiyar gidan nasu, ji kake dam ta faɗa. Innalillahi wa inna’ilaihi raji’un Salima ta ringa faɗa tun kan ta fito daga ɗaki, shi kuwa gogan naka bai ma san meya aikata ba, dan haka ɗaki ya shiga yana fadin ”ke uwar ki bata koya miki girmama manya ba”

Da matuƙar tashin hankali ta fita tana kiran a taimaka mata, matasan da ke zaune a gaban gidan su suka taso aka shiga har Allah ubangi ya ba su nasarar fito da Sajida daga rijiyar, da sauri Salima ta matso kusa tana faɗin ku bani ‘ya ta. Saurayin da ke kusa da ita yace, ”ai sai dai ki yi haƙuri wannan kam Allah ya ɗauki abar sa, addu’a kawai take buƙata” jiri ne ya ɗauke ta, ta tafi kamar zata faɗi amma ta dake, ta ci gaba da kiran sunan Allah tun da tasan ba abin da ya gagare shi.

Bayan minti ashirin Musa ya farka daga baccin da yake tun bayan da ya rusa gidansa da hannusa, ya ɗan dawo hayyacin sa kaɗan a lokacin da ake ƙoƙarin yiwa Sajida sutura, wani rarraba idanu yake kamar an kwashewa karya ‘ya’ya. Ya zo kusa da gawar da yinƙurin yin magana amma Salima tayi saurin tare shi tare da cewa cikin kuka ”kayi haƙuri abban Sajida haka Allah yaso, kullum ina kiyayewa kar tayi wasa kusa da rijiyar ashe ajalinta ne a ciki”. Musa yana ɗan tuna wani abu da ya faru amma ya basar ya kuma turɓune fuska da kiran Allah ya mata rahama.

“Kai ku duba min kamar yarinyar man motsi take” wata mata ta faɗa, tuni kukan da Salima take ya dauke tamkar ruwan sama, tabbas motsin take, kenan da ranta?” ya kamata kuyi gaggawar kaita asibiti dan ceto rayiwar ta”.

Salima ta tashi a zabure kamar wacce kunama ta harba, ta nufi inda take, suka nufi asibitin dake kusa da su.

Nurse ɗin dake duty ta wani kalleta a yatsine tace “je can kisai kati” Salima ta ɗan noƙe” magana ake miki, in baki da shi kuma ki ɗauki ‘yarki ki ban wuri, l have alot to do” lailai Salima tana ganin masifa yau, kuma ba wanda ya janyo mata ita sai mijinta a sanadin shaye-shayen da ba zai mai rana ba har abada.

Ta kalli nurse ɗin sannan ta nufi wurin siyan katin bakin ta yana ƙara kiran sunan Allah. Layi ta bi har aka zo kanta, ”baiwar Allah ina kuɗinki me ye kuma sunan mara lafiyar”? Me karɓar kuɗin kati ta tambaya.Tace sunan ta Sajida Musa” okay ban kuɗin” ta faɗa tana rubuta suna. Salima tayi narai-narai da ido kawai taji daga bayan ta ance, ”ah ba kece wacce ‘yarki ta fa ɗa rijiya ba? da saurin tace nice tana kuma ƙoƙarin gaida shi, ya amsa mata sannan ya biya kuɗin katin da sauran dukkan abin da ake buƙata a asibitin, tun da ya fahimci ba ta da kuɗi.

Lailai Alhaji Garba yana taimakawa mutane sosai. Da da irin su da yawa da al’umma ba su sha wuya ba,” maƙoci me rana kenan” Salima ta faɗa tana murmushi bayan da ta ga dukkan abin da likitoci ke buƙata an samu, dan haka ta godewa Allah.

Sati ɗaya su kai a asibiti aka sallame su, Musa bai wani basu kulawar da ta dace ba. Haka kuma, bai ɓata wa Salima rai ba, saboda tasan halin mijin nata, a dan haka suna dawowa ba ta ko zauna ba sai da ta shiga gidan Alhaji Garba tayi masa godiya yadda ya temaki rayuwar ‘yarta. Ta yi sa’a yana nan ya kuma ce ba komai, za ta tafi yace in zata iya wanke-wanke ta ringa yi musu. Matar shi tace ba komai dama meyi musu wanke-wanken ta yi tafiya, yace a ringa biyan ta duk wata, sannan a ringa ba su abinci daga cikin wanda ake rabawa na sadaka. Rabon da Salima tayi farin ciki irin na wannan ranar ta manta, ta yi godiya sosai, su kai sallama ta nufi gida cikin farin ciki da godiya ga Allah.

“Wannan baccin asarar ya isa haka, ace yaro matashi wanda ya mallaki hankalin kansa ba zai sallar asuba a jam’i ba sai ƙarfe takwas, a tashe sa yaƙi tashi. Bari ki ga ruwan wankin nan zan kwara masa ja’iri”, ai kuwa ruwan ta kwara masa, firgigit ya tashi yana kiran dala dubu biyar kenan,” Allah yasa riyad ne ,malan tashi kai salla” ta faɗa fuskantar ta bako annuri, wayyo mama wayyo, wallahi wani mafarki nake mai shegen daɗi, wai sarkin Makka yaban dala dubu uku, ya ƙara min biyu suka zama biyar, ina ƙoƙarin karɓa kika tasheni.

‘’Wayyo da ma gaske ne wallahi da saina...” gwaf ta gwaɓe masa baki tare da cewa sallah nace kayi ba zancen banza da wofi ba. Bakin nashi ya rike bai ƙara magana ba ya nufi ban ɗaki yayi alwala yayi salla.

“Mama ina abinci, yinwa na tashi da ita ‘yar gaske, ji nake kamar ana min screenshot a ciki” maman ta turo mai ƙwanon waina da ƙuli tare da faɗin meye kuma sigarishot? Abdul dariya kawai yayi yana faɗin ba zaki gane ba mama, zan miki bayani bari ciki na ya ɗauka.

Kwana ukku kenan bata sa idan ta a nashi ba, tana zaune da farar safiya ya shigo ta gaida shi ya kuma amsa yana murmushi, tare da faɗin da fatan kin tashi lafiya ya jikin Sajida ina kuma Ahmad? “Da sauƙi,duk bacci suke”ta fa ɗa tana kokarin tashi tsaye, tayi masa nuni daya zauna, ya kuwa zauna.

Sauran abincin da suka ci ta ɗakko masa ya karɓa yana faɗin Allah ya jiƙan baba, ta ji daɗin addu’ar da yayiwa mahaifiyarta, gefen gadon ta zauna kanta ƙasa” baban Sajida ina sanka ina ma biyayya, me yasa bazaka dena ta’ammali da miyagun ƙwayoyi ba? Me yasa ba za ka inganta rayuwar ka kamar kowa ba? Ka kalla har kusan salwantar da rayuwar ‘yarmu kayi a sanadin shaye-shaye amma na rufa ma asiri duk duniya ba wanda ya ji, duk dan ka gane gaskiya”

Tana ɗaga kai ta kalle shi idan sa sun fara ƙwalla, tausayin sa duk ya kamata dan haka tayi saurin rufe maganar da wannan abokan naka dole ka yanke alaƙar ka da su, dan suma na fahimci suna taka muhimmiyar rawa wajen ganin baka dena shaye-shaye ba, yanzu kamun alƙawarin ba zaka ƙara ba kaji abin ƙauna ta” ta faɗa tare da murmushi. ”ba zan ƙara ba insha Allah” ya ɗan yi gyara zama yace, ”kin san yanzu babbar matsala ta rashin sana’a, wannan zaman mara tushe ya fara isa ta, jiya fa me abincin bayan layi Ƙaura ya gaggaurawa mari ya karɓe bokitin alalalen ya kawo muka ci, ai Allah ba zai kama niba ko? Tunda bani na sato ba” ya faɗa yana ƙaryar da kai, murmushi ta ƙara yi tare da tanbayar sa ”kayi sallar asuba yau? Ya ɗan kalli sama wai shifa a dole tunani yake yace ”nayi mana tun jiya ma” ta fahimta.

Ruwan alwalar ta ɗebo masa tare da shinfiɗa abin salla tace, ”yi maza kayi salla sahibi na ina da labari mai daɗi” da sauri ya tashi yai alwala ya yi salla a ranta tana faɗin ai salla tana hana saɓawa Allah.

Abdul ya shiga gida yana ɗan cin magani, ɗakin mama ya nufa ya same ta tana ɗan rintsawa, ya kalle ta yace “mamana ta kaina tashi burin ki ya kusa cika” ta bude ido kaɗan, ga dukkan alamu ta fara nisa a baccin ”mama magana nazo miki da ita mai matuƙar muhimmanci da daraja da ɗaukaka da cikar burin ki dama nawa” ta tashi zaune tana fadin “to audu ina jinka. Allah yasa ba shashancin naka ne ya tashi ba” ya kalli maman da shagwaɓa yana faɗin ni fa ba suna na Audu ba. Mama da ɗan fushi a fuskar ta tace” ka tasheni daga bacci, ka faɗi meya kawo ka ko kaban wuri” Ya gyara zama yace”duk duniya ba wanda zai iya fahimta ta sai ke, dan haka nazo wurin ki danki dube ni kuma ki kalli yadda abubuwan suke wakana a rayuwar yau da gobe Kuma ki duba irin...”

Ta katse shi da faɗin” ka faɗi abin da ya kawo ka kawai” ya ƙara gyara zama yace”Mama kinsan ƴar gidan Alhaji Sammani tare mu kai B.U.K da ita, to mun gama daidaitawa auranta zan yi” da sauri ta zaburo”au me kace!!! “ya kalle ta yace auren ta zan yi dan haka waccan sauran gonar da baba ya bari ta ƙauye kawai a saida ita. Kuma fa wataƙila baban nata yai min manager a gidan mansa na ‘yan kaba kuma dam... Ji kake kau!!! ta kaure shi da wani farin mari tare da cewa Allah yasa ba shaye-shayen zamanin nan ka fara ba, kodai kasha giyar wake ne kafin kazo nan, mst ina ga ciwon hauka ne ya fara kama ka, dole na yanko ma kati a dawanau” ai bai ko ƙara sauraron taba fuuu ya fice yana fadin yanzu me degree za’a mara?

Musa kam yanzu sai masha Allah, salla yake sosai har a jam’i. Tabbas ya fara nutsuwa, wannan abokan ya watsar da su, komai ya fara yiwa Salima daɗi, adan haka ne da taje gidan Alhaji Garba ta tanbayi matar tasa inda wani gurbi da za ayi wa mijin ta, ai kuwa tayi sa’a Alh Garba ya bashi mukullin mota dan ya ringa ɗaukar abincin da ake rabawa mabuƙata. A ƙaramin lokaci ya canza, farin sa har ya fara dawowa, shi kanshi yayi mamakin hakan.

Yau wata biyu kenan yana zaune yaro ya shigo wai ana kiran Daguji, ya san ba wanda zai kira shi da wannan sunan sai su Ƙaura, haka yasa ƙafa yabi yaran” Daguji ina ka shiga ne kwana biyu bana ganin ka a eka, akwai fa sababbin eyane ya kamata mu muje mu sheƙe su fa” Musa kam kallo yabi Ƙaura da shi tare da tanbayar sa katin ɗaurin auran waye a hannun sa? Yace “ci dagahi ne zaiyi aure wannan lahadin”ya faɗa yana ɗan wani juyayi.

Musa yace”zan zo, karfe nawa za a ɗaura” ya kalle shi sheƙeƙe yace “yo wama ya sani, kasan gudawa nayi a makaranta, ka karanta mana, kai na wuce zanje wurin Abba taye yanzu” ya faɗa yana ƙoƙarin tsallaka kwatar dake ƙofar gidan, ai kuwa ji kake facal ya fancala ciki, Musa ya zaburo yana faɗin “duk jikin naka ne ba kwari sannu kaji tashi” Yasa hannu da niyyar ya ɗago shi, to shima dai jikin ba wani kwari ya gama ba, ji kake facal shima ya bishi, suka fara iyo kamar wasu kifaye.

Yau lahadi, Musa yayi wanka ya tafi ɗaurin aure, bayan gama ɗaurin auran ne suka koma bayan gari dan suyi murnar auran abokin na su. Ba kalar kayen mayen da ba su haɗa ba, ko a ina suke samu oho, ko Gwamnati ta san ana shigo da irin wannan baƙar annobar, ko akwai matakan da gwamnatin ke ɗauka? ko meye ribar masu safarar ta? Iya kuɗi ne, kuma ba ta yadda za suyi albarka tunda ana sa matasa cikin wani hali ba tare da la’akari da cewa matasa sune ci gaban al’umma ba.

Musa yace musu ba zai sha ba, ƙaura yace ”kai dalla ware yauhe ka zama haka, iya yau dai ai ka henye koma meye, abokin mu zamu taya murnar higewa daga ciki fa” da haka dai Musa ya ɗora daga inda ya tsaya.

Yau kwana hudu kenan bai dawo gida ba wai ana can ana shagalin biki, kowa ya faɗa masa cewa ana farin ciki da shan kayan maye, ai nisantar su shi ne ke tabbatar da farin ciki da nutsuwa. Abin takaicin ma duk kusan matasa ne a wurin bikin, ko taya al’umma za ta ci gaba a yayin da matasan cikin ta ke shaye-shaye? Dole fa akwai matsala,ba al’ummar da zata ci gaba matuƙar matasan cikin ta basu san inda yake musu ciwo ba.

A bige ya shigo gidan anyi biki an gama ya iske Salima bata nan, ya nufi ɗaki yana zuwa ya tadda Sajida kwance tana bacci abinta, ya kalle ta sosai sannan yace,”gaskiya Salima baki da hankali, yanzu na tafi yau kusan wata shida bana nan amma ba oyoyo? Ina san ki Salima nayi kewar ki sosai dan haka dole ki bani haƙƙi na na aure yau kuma yanzu” afka mata yayi, yarinyar da ba ta fi shekara uku ba ,tun tana ihu da motsi har ta dena, ya lalata mata rayuwa duk a dalilin shaye-shaye gashi ya jefa rayuwar ‘yarsa a cikin yanayin da yai sanadiyyar mutuwar ta, lailai wannan ba ƙaramar musiba bace wacce maganin ta sai dai Allah kawai.

Sallamar da Sadeeq ɗan maƙociyar yayi ne ya sa shi dagowa da fushi yana faɗin kai ƙaura nace ka dena shiga rayuwa ta amma kaƙi, shi ne ka biyo ni har gida har ɗakin matata? “Nayi sallama fa, dama cewa akai na ɗakko Sajida ina ta tashi daga bacci” ya faɗa yana kallon Musa. Tuni gogan naka ya finciko shi ya haɗa kansa da bangon ɗakin ,take jini ya fara zuba, wuƙar dake ajiye a cikin kwando ya ɗakko ya fara caka masa, bai ko motsa ba rai yayi halinsa.

Salima ta ji shiru dan haka ta biyo taga yadda akai aka haihu a ragaya, ai kuwa tana zuwa ta iske abin da ya ɗugunzuma mata hankali, ta fice tana faman ihun neman ceto, tuni jikin ta ya kasa ɗaukar ta, ta faɗi ƙasa sumammiya, mutane suka kawo ɗauki inda suka cafke wanda ake zargi zuwa ofishin ‘yan sanda dan a tabbatar da laifin sa kuma ai masa hukumci da irin abin da ya aikata, ko hakan zai iya zamowa izina ga sauran mutane masu hali irin nasa.

Alhaji Garba ya kaɗu sosai da abin ya faru dan haka yaga baiga ta zama ba dole ya haɗa kan al’umma dan a magance dukkan matsalar data taso a cikin al’umma, dan haka kai tsaye gidan Alhaji Sammani ya nufa, sun tattauna sosai akan matsalolin. Bayan kwana ukku suka haɗa duk matasan dake cikin unguwar tasu. Alhaji Garba yayi gyara murya sannan yace.

“Ya ku jama’ar wannan yanki namu me albarka, ku sani gwamnati nada ayyuka da yawa a gaban ta, a dan haka ba zamu bar mata komai ba, dole mu haɗa ƙarfi da ƙarfe mu tallafi yankin mu, amma ku sani hannu ɗaya baya ɗaukar jinka. Ni kaɗai ba zan iya ba, Alhaji Sammani ba zai iya ba, dole sai mun haɗu ni da ku, matasan wannan yankin namu mai albarka, ku sani dole zaman banza ba sana’a ba zai taɓa haifar mana da ɗa me ido ba, ku kama sana’a ku bar shaye-shaye, ku kalli yadda ɗan uwan mu wanda ya taso a cikin mu yadda sanadiyyar shaye-shaye ya dakusar da rayuwar sa, ya tsayar da dukkan burikan sa, ya rasa matar sa ,tun da yanzu kuna gani bayan da aka yanke masa hukumcin ɗaurin rai da rai a gidan ajiya da gyaran hali, a ta dole aka raba auran sa da matar sa.

In har za kusha kayen maye tofa ku sani wallahi ba inda rayuwa za ta kai ku sai tashar wulaƙanci da tozarci kuma daga ƙarshe kuyi dana sani wanda Hausawa sukace ƙeya ce. Duk ƙanƙantar sana’a kuyi ku dai dogara da kanku a sannu a hankali Allah zai buɗa muku,amma indai kuka riƙe hannu kuna jiran sai gwamnati ta baku aiki to zaku zauna kullum gafara sa amma bakuga ƙaho ba,domin kamar yadda na faɗa muku gwamnati nada ayyuka da yawa a gaban ta.

Dan haka dani da Alhaji sammani ga Alhaji Umar zamu bawa duk matashin da yake san yin sana’a dan ya dogara da kansa jari, domin rashin aikin yi na jefa da yawa daga cikin matasa harkar shaye-shaye ko fataucin kayan mayen idan abin yai tsamari”

Yau wata huɗu da kwana goma kenan, unguwar tasu harta dawo hayyacin ta,sace-sacen da ake na waya ko haurawa gidan mutane an dena, balle kuma shaye-shaye da yake ƙoƙarin zama tarihi a yankin gaba ɗaya,matasa maza da mata sun kama sana’a,yaran da iyayen su basu da ƙarfi ana ɗaukar ɗawainiyar karatun su daidai gwargwado.

Ɗaukar Jinka

Post a Comment

0 Comments