Ticker

6/recent/ticker-posts

Sanadi

Khadija Lawan Daura (2023). Sanadi. Ɗaukar Jinka (Labaran Da Suka Samu Nasara A Gasar Gajerun Labarai Ta Arc. Ahmed Musa Dangiwa, 2022). Kangiwa Multimedia and Communication Company LTD

SANADI

Na

Khadija Lawan Daura

Daka mata dukan da aka yi ne ya farkar da ita daga baccinta. “Sannu Zainab, kin sani ba bacci ba ne a gabanmu ba, ko baki ji abin da Oga Bala ya ce ba? Lallai-lallai tara na safe ta yi mana a filin jirgi, don Allah ta shi ki shirya.” Tsaki Zainab ta ja ta miƙe tana sosa idanuwanta. cikin muryar jin bacci ta ce, “Saddiƙa ki na da matsala, kin san me nake a cikin mafarkin nan kuwa?” A yatsine Saddiƙan ta kalleta. Ban sani ba. Ta faɗa da gatse.

“Hmmm, ina tunanin akwai gagarumar nasara a wannan tafiyar tamu, tabbas burina yana gab da cika Saddiƙa, mafarki na yi na ci nasara sanye cikin kakin soja yayin da sauran sojijin da suke ƙasa da ni suke mini biyayya, abin mamakin ma Yusuf ne ɗaure cikin ankwa, babu abinda suke jira sai umarnina na ya za a yi da maciyi amana? Harbesa za su yi ko kuma uƙuba za su gana masa. Bata bari ta kai ƙarshe ba ta zauna tare da kai hannunta kan kafaɗunta.

“Zainab, ki kwantar da hankalinki ɗaukan fansa ba abu ne da yake kara zube ba, abu ne mai buƙatar nazari sannan da aiki tuƙuru, kamar yanda na faɗa miki hanyar safarar kayan harka ce kaɗai zata sa ki cimma burinki, wallahi idan yau aka ce aljihunki a cike yake da sulalla to tabbas za ki juya kowa ki taka kowa ki yi abin da ranki ya ke so ciki har da ɗaukar fansar abin da Yusuf ya yi miki.” Cike da gamsuwa da kuma jin daɗi Zainab ta saki murmushi. “Zan iya yin komai akan hakan, saboda Yusuf ya kashe mini rayuwa, ya azabtar da ruhina ya kuma wulakanta mutumcina, ya hana jama’a ganin ƙimata a cikin idanuwansu..

Hawaye ya ciko mata ido. “Ni fa wannan sakarcin naki ne bana so.” Saddiƙa ta faɗa tana bata rai. “Ke har yanzu baki bar kuka ba, izuwa yanzu ko darom ɗin hawaye ne a cikin idanuwanki ya ci ace sun kafe, Yusuf ɗin me? Ai yanzu kin fi ƙarfin zubarwa da wannan mahaukacin hawaye.Ƙwafa Zainab ta yi. Ban taɓa baki labarina cikakke ba ne, na faɗa miki wani, wasu kuma na boye saboda ni kaɗai nasan su na kuma sha alwashin babu mai jin su har sai na cimma gaci……..”

Katseta ta yi. “Kin ga ta shi don Allah ki shirya mu tafi ba a bori da sanyin jiki, yau ne fa rana ta farko da zamu fara harkan nan, kuma ayau ɗin aka tabbatar mana da cewa tsallakewarmu tamkar raba mu da baƙin talaucin da ya yi mana rumfa ne. Da sauri Zainab ta tashi ta fita tana mita akan abin da take fama da shi. “Wallahi shi ne na farko da zan fara azabtarwa fiye da yanda ya azabce ni, sai na wulaƙanta rayuwarsa na ɗaiɗaita farin cikinsa.” Tana mitar ta shirya. Cikin kulawa Saddiƙa ta miko mata wasu ƙwayoyi guda tara.

“Oga ya ce musha wannan guda uku, saboda yau zamu fara kada rashin gaskiya ya sa mu zama shege a rabon gado.” Dariya ta yi duk da zuciyarta na yi mata wasu muggan saƙe-saƙen, tunaninta akan gagarumin aikin tsallaka ƙasa jikinsu cike da kayan maye. Hmmmm, wai kina nufin shan wannan zai ƙara mana kuzarin riƙe tsoro da fargaba? Taɓe baki Saddiƙa ta yi. Haka dai oga ya ce mini wai fatauci sai da gagarumin shiri, ciki sai ka yi ƙoƙarin fatauce duk wata hanya da zata sa aga wata alama a tare da kai.” Ajiyar zuciya ta yi tare da kallon Saddiƙa cikin saddaƙarwa.

“Kina ganin za mu yi nasara kuwa? Karfa garin neman gira mu rasa ido.” Dariyar ƙarfin hali ta yi. E, to, amma ina da tabbacin za mu nemi girar ba tare da mun rasa ido ba, a cikin matan da ya yi mana kwatance babu wacca bata haye ba, wai ma banda abinki wanne mahaluƙi ne ya isa ya gano inda kayan suke a jikinmu?” Dariya suka yi dukkansu. “Kuma fa haka ne, ni kaina sanin hakan ke karfafa mini gwiwa Saddiƙa.

Bata zaci haka ba sam, ba tasan abun babba ba ne sai da ta tsinci kanta cikin filin jirgi wanda zuwanta wajan shi ne na farko a tarihin rayuwarta, kallo ɗaya zaka yi mata ka fahimci gazawarta da tsoron da ya hanata sukuni. “Saddiƙa na shiga uku! Ita kanta Saddiƙan a cikin yanayin take don kar ta sagarwa da Zainab ɗin gwiwa ta ce, “Wai kin sha ƙwayar nan kuwa?” Goge gumin goshinta ta yi wanda take jin zubar wasu cikin jikinta tamkar an bude famfo. “Na sha mana ko ba a gabanki na sha ba, ni dai da-na-sani ma ban sha ba don babu abin da ya ƙara min. Kalli wa’yancan ‘yansandan ji fa yanda suke zare ido kamar su ci babu.” Hankalin Saddiƙa ya tashi. Ni kaina Zainab abun ya fara damuna babban baƙin cikina ko an kama mu ba mu isa mun ce Oga ba, ni kam ban san abin yi ba an ya ba za mu koma wajan Oga ba?

Da mamaki Zainab ta kalle ta. “Kin manta sharaɗin kenan? Tun farko me ya ce mana.” Bakin Saddika na rawa ta ce, “Ce wa ya yi dawowarka tamkar mutuwarka ne, idan mun dawo ma babu wanda zai taimaka ya raba mu da kayan mayen nan, Innalillahi.” Daidai lokacin da layi ya iso kansu. Cikinsu ya ɗuri ruwa hankalinsu ya yi mummunan ta shi. Kwatsam ba zato su ka ga wani kakkauran ɗansanda ya tsura musu ido yana kallonsu cike da nazari. “Shi kenan ta faru ta ƙare Saddiƙa.

Zainab ta faɗa hankalinta a tashe. Wani kuka ne ya taho mata wanda ta kasa tsayar da shi. Wanda ke gaban Saddika ne ya isa kusa da ‘yansanda da suke bincike tana kallon ɗansandan da ya kara masa na’ura nan da nan ta hau ƙarar da ke nuna akwai wani abu ajikinsa wanda ba a so. Da sauri ta ja baya tana kallonsu cikin rawar jiki ɗansandan da ke kallonta tun ɗazu ya ƙura mata ido yana son gano gaskiyar da take ƙoƙarin ɓoyewa da sauri ya yo kanta hakan ya hautsina mata hankali ta kwasa aguje tana ihun akawo mata ɗauki wallahi saka ta aka yi.

Ƙura masa ido ta yi tana kallonsa. Wai shin ina burinta yake? Kakkausar muryarsa ta doki kunnanta. Ta ji abin da yake tambayarta sai dai amsar sa tamkar neman allura ne a cikin ruwa. Wai tambayarta yake waya ƙunsa musu kayan maye a cikinsu? Sake daka mata tsawan ya yi wacca sai da ta razana don da sauri ta ɗago kai tana kallonsa a firgice. “Don Allah ku kashe ni na huta! Wannan rayuwar ta ishe ni na gaji da ita! Allah ya isa Yusuf! Duk kai ne sanadiyyar jefa rayuwata cikin masifa gashi a ƙarshe ka zamar min ajalina!

Zafin marin da ɗansandan ya yi mata ne ya sa ta dawo hayyacinta. Ta kalli ɗansandan, taga wani irin kallo da yake mata wanda ta kasa tantance na menene? Tsawar da ya kuma yi mata ce tasa ta cure kanta cikin cinyoyinta. Ta yarda a kasheta ta huta amma ba za ta taɓa magana ba. Rashin maganarta ya fusata ɗansandan ya fice tare da aiko mata wa su ‘yansanda biyu mata suna zuwa suka rufeta da duka. Tun tana ihu har ta kai bata iya wa saboda muryarta ta dushe.

Da-na-sanin fallasa kanta a filin jirgi ya ziyarceta. Sai da suka yi mata lilis sannan suka barta kwance cikin mugun yanayi, Ta kasa ko motsi sai idonta kawai take juyawa hakan ya bata damar ƙura wa bangon ɗakin ido tana tuna rayuwarta.

Ita kaɗai mahaifiyarta ta haifa ta rasu, ta tashi wajan kishiyar mahaifiyarta wacca ta yi mata riƙon sakainar kashi. Rayuwarta abar shaawa a wajan mutane don tana yinta ne a sanyaye bata cika shiga jamaa ba duk da tana sanaar ƙunshi, sai dai bata samun mutane da yawa don ba a barinta yi, a haka take rayuwarta wacca take ganin tamkar akan ƙaya take don girmanta ya sa Inna kishiyar mamanta ɗora mata duk wani aikin wahala ko na ƙarfi ita ke yinsa da karatunta kawai ta tsira saboda babanta ya dage akan yana son ya ilimantar da ‘ya’yansa, a haka ta gama secondary ta samu sakamako mai kyau, babansu ya ba ta damar cigaba da karatu. Yusuf ya shigo rayuwarta ne kwatsam duk yanda ta so yakice shi abun ya faskara don Yusuf saurayi ne mai matuƙar surutu da son saka mutane a nishaɗi, bata san ya a ka yi ba sai tsintar kanta cikin tsananin soyayyarsa don har gidansu ya tura iyayansa aka tsayar da maganar aure kan yana kammala karatu sai aure saboda shi a lokacin yana aji uku ita kuma tana aji ɗaya gab da shiga aji na biyu.

Soyayyarsu mai tsabta suke yi, don sosai Yusuf ya sake a gidansu saboda daƙin zaure aka ba su inda suke hirarsu a nan, sau tari suna tsaka da hira idan aka yi abin dariya sai ya kai hannu cinyarta tun tana ɓata rai da nuna masa bata so, sai ya nemi afuwarta da cewar ya saba hira da abokanansa ne ya manta, ta amshi uzirinsa don tasan shi mutum ne mai hira da abokai. Da haka ya fara zarcewa har yana kai hannu duk inda ya ga dama da ta nuna ranta ya ɓaci sai ya nuna na shi ya fi nata ɓacin saboda tana ƙoƙarin mayar da shi ɗan iska wani zubin har tafiyarsa yake ya barta a nan sai ta nemo shi ta ba shi hakuri saboda tana son shi, har ta kai yana yanda ya so bata isa ta yi magana ba saboda kada ransa ya ɓaci ya tafi ya barta. Abinda yake yi mata yana ci mata tuwo a ƙwarya amma ya ta iya, son shi take kamar ta cire ranta ta ba shi sau tari idan ya yi yanda ya so da ita sai dai ta shiga ɗaki ta yi ta rusa kukan baƙin cikin abun, babban takaicinta yanda ta zama kamar wata raƙumi da akala wato sai yanda yaga dama da ita, har takai ta kawo ma kiranta yake wasu keɓaɓɓun waje ta je ta same shi, ba kuma isa ta ƙi zuwa ba, hakan da yake mata ko alama baya gudunta don wata soyayya yake nuna mata kamar babu wata mace a duniya sai ita, sau tari ya kan faɗa mata yana kallon mata ne tamkar yan’uwansa maza don idanuwansa da ita kaɗai suke kallo a mace don ita ta mallaki dukkan abin da yake nema a wajan mace. Yana yawan faɗa mata akanta babu abin da ba zai iya yi ba, kuma zai iya komai don ya mallaketa don haka ta kwantar da hankalinta ta saki jiki ita ce mace ɗaya tilo da ta sarƙafe masa zuciya kuma ita ce kawai yake kallo ta dace da zama uwar ‘ya’yansa. Waɗannan kalamai nasa sun taɓa mata zuciya kwarai kuma sun yi tasirin da ta mayar da kanta tamkar mallakinsa.

A haka suka kwashe shekara ɗaya tare suna gudanar da wannan rayuwar wadda ta zame mata matsala, kwatsam wata ƙawarta ta kawo mata katin ɗaurin aurensa. Tun daga ranar lafiyarta ta yi mata hijira kira babu wanda bata yi masa ba ya ƙi biyo sahu duk inda yake kiranta ta je nemansa babu shi babu alamarsa ga tsananin rashin lafiyar da ke addabarta, mahaifinta da kan shi yake rarrashinta akan ta haƙura da shi tunda ba shi kaɗai ba ne namiji tana da manema ta barshi ta fauwalawa Allah tabbas ubangiji zai karɓi addu’arta.

Tun tana ƙunci da baƙin ciki akan hakan har ta kai yanzu ta lafiyarta take. Ta je kemis tasha magani kala-kala amma sauƙi babu a haka mahaifinta ya gaji ya kaita babbar asibiti gwaji, aka tabbatar masa da tana da cikin wata biyu. Da kyar Baba ya tambayeta cikin waye, Cikin kuka ta sanar da shi.

Ya rufe ta da wani irin duka, duk abin da ya ɗauko maka mata yake da kyar aka kwaceta, sai da Inna taga bata motsi ta yi kururuwar akawo mata ɗauki, yana gama dukan ya yanke jiki ya faɗi. Labarin cikin Zainab har makaranta, ‘yan unguwa kuwa suka samu abin yi yara da manya na tururuwar zuwa ganinta. Baba kam ya shiga tashin hankali mara misaltuwa don cikin fitar hayyacin yake jerawa Zainab munanan maganganu marasa daɗi. Irin kalaman mahaifinta ya fi komai ɗaga mata hankali.

Shi Yusuf da ya ji labarin ya yi tsalle ya dire ya ce sharri take yi masa su je can su nemi uban da ya yi wa ‘yarsu ciki. Abu ta kai har da ‘yansanda sai da ya ji matsi ya amsa. Ko da suka dawo gida hawaye baba ya yi ta yi har da furta mata kalmar ina ma ban haife ki ba Zainab. Wannan maganar ta shi ce tasa ta yanke shawarar barin duniyar don ta huta. Yana fita sallar la’asar ta fito da gudu ta zunduma kanta a rijiyar gidan.

An yi nasarar fitar da ita sai dai cikin nata ya fice duk da baƙar wuyar da tasha a asibiti hakan bai sa babanta tausaya mata ba, ita kaɗai ta san ciwon maganganun da babanta ke yi wanda take ganin Inna ce take ƙara zuga shi. Inna na sane take aikenta waje duk da bata da lafiya duk ta fita, haka mutanen unguwar za su rakata da idanuwa suna nunata har ta dawo. Ta rame ta jeme. Ita kam tuni kome na duniya ya fita kanta, babban abinda ke ci mata tuwo a ƙwarya wata ƙara take ji a kunnanta da kuma rashin bacci don yanda taga dare haka take ganin rana sai bayan sallar asuba baccin ke surarta shi ma tana farawa Inna ke tashinta da faɗan tsiya akan ta tashi ta gyara gida.

Baba lamarinsa sai ta’zzara yake faɗan yau dabam da na gobe, haka faɗan Inna yaƙi tsayawa, tsegumin mutane da rashin bacci da wannan ƙarar ya taru ya cukurkuɗe mata rayuwa ba shiri ta yanke hukuncin tattarawa ta bar gidansu ba tare da sanin kowa ba, ta tafi can Kaduna wajan ƙanwar mahaifiyarta, zuwanta gidan ta amshe ta don dama tun tana yarinya suka so amsarta baban ya ƙi duk kuma suna da labarin abin da ya faru da ita.

Ƙanwar mamanta da take kiranta da Anty ita ta yi ta tausar ta tana kwantar mata da hankali a haka har ta saki jiki uwa-uba unguwar babu wanda ke yi mata kallon tara saura biyu, matsala ɗaya mijin Anty talaka ne don da kyar ake iya cin abinci sau ɗaya a gidan, ganin zata shiga mummunan yanayi yasa ta dawo da sana’arta ta ƙunshi cikin hukuncin Allah ta samu karɓuwa.

A sanadin ƙunshi ta haɗu da Saddika wacce kowa a unguwar yake yi wa kallon ‘yar bariki ta su ta zo ɗaya sosai don duk Saddika ta zauna tana bata labarin irin wahalhalun da ta sha wanda ciki har da rashin bacci cikin mamaki Zainab ta katse ta “Kina nufin kema kina fama da wannan lalurar?” Cikin mamakin ita ma Saddika ta amshe da “Sosai ma kuwa Zainab don kin ganni nan aurena biyu a ‘yan ƙananan shekaruna dukkan mazajen nan babu na arziƙi dole ce ta sani zawarci, tsangwama da kuma ƙunci ne yasa na kamu da cutar baƙin ciki har na daina barci da na je naga likita ta ce mini ya zama dole na daina tunani na kuma daina damuwa idan ba haka ba kuwa tabbas cutar zata iya haihuwa ta zame min babba da zan iya rasa hankalina.

 Bayan na dawo gida hankalina ya tashi dole na nema wa kaina mafita yanzu ai labarin rashin barci ya zama tarihi a rayuwata Zainab, don ko yanzu na so yin barci zan yi abina.” Cikin jin daɗi Zainab ta ce, “Na ji daɗi wataƙila nima warakata ta zo.” Cikin hikima da hilata ta ware mata zare da abawa ta so yin gardama, Saddika ta yaudareta da cewar wai babu mai sani kuma ai su dole ce ta sa ba wai don sun so ba.

Alaƙarsu ta yi ƙauri sosai don sanadiyyar Saddika, Zainab ta san mutane, gidan Anty kullum cike yake da mutane masu zuwa lalle.

“Ina son baki shawara ƙawata.” Zainab ta kalleta. “Ke fa yanzu kin zama hajiya manyan yara na zuwa wajanki lalle mai zai hana ki jefi tsuntsu biyu da tarko ɗaya? Ma’ana da wannan gantalin da muke zuwa siyan kayan harka ki saro mana kawai a wajan su Muntari ki rinƙa sayarwa ko ya kika gani?”

Da wannan ta zama dila a harkar, sun raina mutanen unguwar don da sana’ar ƙunshi ta fake take siyar da kayan maye ga mata, ta yi ƙaurin suna ga abokanan harka don sosai take ciniki. Dalilin sana’ar ta zama ita ce take faɗa a ji a gidan don ita ke ciyar da su. Musamman Saddika ta haɗata da manyan mata da ‘ya’yan masu kuɗi wanda suke shaye-shaye. Ita kam ta zama hajiyar kanta ta manta da wani ƙuncin sai dai har gobe baƙin cikin Yusuf ya ƙi barinta tana yawan binciken halin da yake ciki. Mahaifinta sai da ta kwashe shekara ya neme ta duk da hakan cewa ya yi ta zauna a can shi bai son ganinta. Babban burinta shi ne ta ji yau rayuwar Yusuf ta lalace don duk ta tuna shi a ranta sai ta jefe shi da baƙar addu’ar Allah ya yi kaca-kaca da rayuwarsa. Babban burinta shi ne ta zama babbar hajiya ko ta halin ƙaƙa ba don komai ba sai don ta ɗaiɗaita rayuwarsa. Cikin hakan Saddika ta kawo mata shawarar ta samo musu hanyar safarar kayan maye.

Azabar dukan da aka ka yi wa cikinta ne ya dawo da ita daga dogon tunanin da take yi, Cikin jin azaba da murƙususun take jin masifar wacca ta shigo wai ashe tambayarta take yi ta ƙi bata amsa hakan ya tunzirata dukan nata, tana cikin shafa cikin don ji ta yi tamkar an fasa mata shi saboda azabar zafi cikin jin zafi ta sake jin wani dukan hakan ya tunzirata yin ƙara tare da sumewa don bata ƙara sanin me ya faru ba.

An yi nasarar yi mata aiki ita da Saddika don tun a filin jirgi bata san a wanne irin hali Saddikan take ciki ba, an cire kayan mayan da Oga ya sa musu an kuma tallatasu a duniya duk yanda aka so su yi magana sun ƙi duk da cewa an raba su da kayan mayen sai dai gargaɗin oga na bibiyasu don ya tabbatar musu da cewa tona masa asiri tamkar ƙarewar zuri’arsu ne a doron duniya wai sai ya sa an kashe dukkan iyayensu da ƙannansu da danginsu, a yanda suke ji ƙwara su su mutu da su yi sanadiyyar mutuwar danginsu saboda Oga ya faɗa musu shi ba ƙaramin mutum ba ne yana da rassa kala-kala a duniya sannan kafin ka shiga harkar sai an sanka an san iyayanka da adireshinka, da shi zai fara yi maka barazana.

Tambayoyi da azaba babu wanda ba ta sha ba ta ƙi magana don asalima bata san cikakken sunan Ogan ba, sannan bata san inane gidansa ba don duk haɗuwar da za su yi a otel suke haɗuwa. Sau tari idan ‘yansanda suka shigo, abin da suke tambayarta dabam da amsar da take ba su, su da kansu suka fuskanci lallai akwai matsala.

Ta ƙurawa likitan da ke tambayarta ido tana kallonsa tamkar Yusuf don fuskarsa take gani. Cikin zubar hawaye ta ce, “Ka ci riba ko Yusuf? Menene babban laifin da na yi maka? .” Ta tashi cikin wani irin kwarin gwiwa ta shaƙo shi da kyar ‘yansandan dake gadinta suka kwace shi, tuburan ta haukace musu tana ihun a bata shi ta kashe shi.

Bata san ya aka yi ba, sai farkawa ta yi ta ga likita a kusa da ita tana jera mata sannu. “Likita na sani an yi mini aiki an cire mini kayan mayen amma bayan nan ina jin surutai a kunnuwana sannan ina ganin maƙiyina Yusuf na ƙoƙarin sake cutar da rayuwata, kuma ina ganin wasu mutane a kusa da ni suna kallona don jiya ma wata tsohuwa a cikinsu ta ce mini wai zata taimaka mini.” Ta ƙarasa maganar cikin jin jiki. Gyaɗa kanta likitar ta yi. “Kada ki damu Zainab nima abin da ya kawo ni kenan na yi miki wasu tambayoyi wanda nake son ki amsa mini su don su za su taimaka mini wajan gano ainahin abin da ke damunki.” Girgiza kai Zainab ta yi cike da gamsuwa.

“Tun yaushe kika fara jin surutan?”

“Tun da aka kama ni ne don a ranar ma sai da na ji muryar wani yaro yana faɗa mini wai na gudu.” “A da can baya kafin a kamaki kin taɓa jin makamancin haka? Ko ki ji surutu ko ƙarar wani abu a kunnanki?” Cikin sauri Zainab ta ɗaga kai. “E, lokacin da bana bacci na kan ji kamar ƙarar ƙarafa a cikin kunnena.” “Kin taɓa lalurar rashin bacci kenan?” Cikin tabbatarwa ta ce, “Sosai ma kuwa don na jima bana barci,” “Ya aka yi kika samu lafiya, ma’ana magani kika sha kika dawo yin barcin?” Hawaye ya sauko mata. “Na sha kayan maye ne.” Tsura mata ido likitar ta yi, “Bayan kin sha kayan mayen baki ƙara jin wannan ƙarar da kike yawan ji ba?” “Ina ji. Likita don Allah me ke damuna.”

Ajiyar zuciya likitar ta yi. “Kina fama da severe depression. (cutar baƙin ciki).” Kuka ta fashe da shi.”Ba dole na kamu da cutar baƙin ciki ba likita kin san wahalar da na sha a rayuwata kuwa?” Girgiza mata kai likitar ta yi. “Amma kuma ke da kanki kika yi sanadiyyar hauhawar cutar zuwa matsayin da zaki rasa hankalinki gaba ɗaya.” Mamakin Zainab ne ya hanata kukan sai kallon likita da ta yi. “Ni kuma likita ta yaya?” “Ta dalilin shan kayan maye da kika yi, a tunaninki wannan kayan mayen sauƙi ya baki, to shi ɗin ne sanadin rasa hankalinki.

Depression yana ɗaya daga cikin cutukan da muke kira da sunan non communicable diseases wato cutukan da ba a ɗaukarsu a wajan kowa sannan su waɗannan cutukan babu wanda ya san causes dinsu ma’ana abin da ke kawo su sai dai wasu dalilan kan saka su hauhawa a jikin ɗan adam wanda drugs abuse wato shaye-shaye na ɗaya daga cikin abin da ke hauhawar da cutukan, su kaisu kan babban matakin da ba a so, lokacin da ƙunci yasa kika kamu da cutar maimakon ki zo asibiti a dora ki akan anti depression drugs, maganin cutar sai kika gwammace shan maganin maye don yaye miki rashin barci kinga ƙilu ce ta ja miki bau, amma kada ki damu in sha Allahu idan aka ɗoraki akan magani kuma kika kiyaye tabbas zaki warke.” Kuka ta fashe da shi da ƙarfi.

“Shi kenan yanzu haka zan ƙare a rayuwata! Haka zan dauwama! Wallahi Saddika kin cuce ni da ace ban sha kayan mayen nan ba ban kuma yarda da safararsu ba tabbas da yanzu ina nan da hankalina, wayyo wannan rayuwa!” Kanta ta fara bugawa jikin bango tana sambatu. “Na tashi a tutar babu kenan? Bayan taɓin hankali ga hukuma na jirana don shukar abinda na girba! Tabbas ba zan wahalta ba ni kaɗai zan fallasa Oga idan ya so a yi mutuwar kasko! Zan kuma faɗawa ‘yansanda abin da ya ce akan dangina!”

Ta fallasa sirrinsa don ta sanar da su komai babu abin da ta sani akansa illa tana da wani hoto a wayarta da ta ɗauki selfie (hoton kai da kai) cikin kuskure ya fito a ciki shi ma hoton ta ɗauka ne saboda kayatuwar otel ɗin da suka je wajansa, in da suka keɓe shi da ainahin wanda ya kawo su wajan a nan ta ɗaga wayar ta yi hoton.

Da wannan kaɗai ‘yansanda suka yi nasarar kama shi. Ita kam Zainab sai hamdala don tuni suka ajiyeta asibitin masu taɓin hankali, da kyar ta samu labarin wai Saddika ta rasu bayan an yi musu aikin cire kayan maye mutuwarta ta girgizata ta kuma ƙara shiga taitayinta.

Ƙarshe!  

Ɗaukar Jinka

Post a Comment

0 Comments