Ticker

6/recent/ticker-posts

Turken Tauhidi A Wasu Wakokin Husaini Jikan Boka

Citation: Muhammad ADAMU da Ahmed Sulaiman BAFFA da Usman Ibrahim KAOJE (2024). Turken Tauhidi A Wasu Waƙoƙin Husaini Jikan Boka. Yobe Journal of Language, Literature and Culture (YOJOLLAC), Vol. 12, Number 1. Department of African Languages and Linguistics, Yobe State University, Damaturu, Nigeria. ISSN 2449-0660

TURKEN TAUHIDI A WASU WAƘOƘIN HUSAINI JIKAN BOKA

By

Muhammad ADAMU

Da

Ahmed Sulaiman BAFFA

Da

Usman Ibrahim KAOJE

Tsakure

Wannan takarda ce mai taken ‚Turken Tauhidi A Waƙoƙin Hussaini Jikan Boka‛. Hussaini Jikan Boka fitaccen mawaƙi ne da ya shara ga basira da yake ƙulla zaren tunaninsa wajen sako saƙonni masu muhimmanci a cikin waƙoƙinsa. Tauhidi babban batu a cikin rayuwar Musulmi wannan ya sa yawancin mawaƙan baka sukan yi amfani da shi wajen jan hankalin da tunasarwa ga jama’a. Saboda haka, wannan takarda tana ɗauke da bayani kan tauhidi da rabe-rabensa, da kuma fito da misalan kalmomin tauhidi a cikin waƙoƙin wannan mawaƙi Hussaini Jikan Boka. Daga ƙarshe hakan ya nuna irin taka rawar da addinin Musulunci ya yi wajen kawo Allah kusa da al’umma ta sanin tauhidi, mawaƙi Hussaini Jikan Boka ya yi amfani da wannan dabara cikin wasu ɗiyan waƙoƙinsa.

 1.0 Gabatarwa 

Tauhidi shi ne kaɗaita Allah Ta’ala da bauta tare da amincewa da dukkan abin da ya jingina wa kansa na sunaye da siffofi da ayyuka. Tauhidi ne abu na farko da ke tabbatar da kasancewar mutum Musulmi. Kaɗaita Allah

(tauhidi) shi ne ginshiƙi na farko mai ƙarfi da addinin Musulunci yake kansa. Don a kaɗaita shi (Allah) ne ya aiko Annabawa da manzanni masu yawa daga zamanin Annabi Adamu (AS) zuwa Annabi Muhammadu (S A W). Bayan tauhidi sai sauran ayyukan ibada kamar Sallah da Azumi da Zakkah da Hajji da sauran al’amurran zamantakewa, (Umar Aliyu Bunza: 2014).

Al’ummar Hausawa mutane ne waɗanda suka kasance Musulmi, kuma masu riƙo da tauhidi cikin kowane lamari nasu. Wannan ya sa kowane abu ya faru mai kyau ko maras kyau, Bahaushe yakan danganta kasancewar abin daga Allah (S W T). Husaini Jikan Boka yana ɗaya daga cikin mawaƙan Hausa wanda ke da cikakken tasirin musulunci cikin rayuwarsa. Wannan tasirin ya kasance wani muhimmin abu har cikin waƙoƙinsa. Kasancewar tauhidi ginshiƙi ne babba cikin rayuwar Musulmi, ya sa Husaini jikan Boka yake tsarma tauhidi waƙoƙinsa, musamman yayin buɗe wasu daga cikin waƙoƙin. Yana yin haka ne saboda wani lokaci ya yi wa al’umma wa’azi da faɗakarwa. Wani lokaci kuma saboda tasirin Musulunci da ƙarfin imaninsa ga kasancewar Allah mai iko ne kan komai da kowa, kuma mai aikata abin da ya so, da kuma kasancewar Allah abin dogara da neman biyan buƙata da kuma kariya. Manufar wannan takarda ita ce nazari tare da sharhin tauhidi da ke ƙunshe cikin wasu mabuɗan waƙoƙin Husaini Jikan Boka na Hausa.

1.1 Ma’anar Tauhidi

Masana lamuran addinin Musulunci sun dubi matsayin tauhidi a Musulunci a kuma a bin da ya ƙunsa suka fito da ma’anoni daban-daban gwargwadon fahimtarssu. Ga kaɗan daga cikinsu.

A cewar Wazirin Kano (1980:8): Tauhidi shi ne tabbatar da samuwar zati, ƙaduri, mai siffofin kamala, tsarkakakke daga kowace irin tawaya da kowace irin naƙasa wanda bai yi kama da komai ba, kuma babu wani abu da ya yi kama da shi ta kowace fuska da kowane hali.

taƙaice idan aka yi la’akari da wannan ma’ana a iya cewa, tauhidi shi ne tabbatar da samuwar Allah Maɗaukakin sarki mai kowa mai komai tare da bauta masa shi kaɗai ba tare da tarayya da komai ba a cikin kowane nau’a na bauta masa ba, da kuma sakankancewa ga samun sakamako ga yi masa bauta da kuma azaba ga yi masa tarayya a bauta.

1.2 Rabe-Raben Tauhidi A Musulunci

Tauhidi ya mamaye dukkan rayuwar Musulmi wanda hasali ma shi ne ƙofar da ake shiga addinin Musulunci daga gare ta. Wasu malaman Musulunci kamar Asimina (1980) ya karkasa tauhidi zuwa gida uku kamar haka:

a. Tauhidur-Rububiyyat (Kaɗaita Allah da ayyuka) wanda shi ne tauidin kaɗaita Allah da ayyuka misali halitta, da azirtawa da rayawa da kashewa da juyar da al’amurra da kawar da cuta da makamancin waɗannan.

b. Tauhidi-uluhiyyat (kaɗaita Allah da bauta) shi ne na kaɗita Allah da bauta misali, addu’a da yanka da alwashi da neman taimako da neman tsari da wanin waɗannan. Wannan nau’i na tauhidi shi ne wannan da kafurai suka yi musun shi, kuma jayayya ta kasance a cikin shi take tsakanin manzanni da al’ummunsu tun daga Nuhu amincin Allah ya tabbata a gare shi har zuwa ga Annabi Muhammadu sallallahu alaihi wasallam.

c. Tauhidi-Asma’u was-sifft. (kaɗaita Allah da sunaye da siffofi) wannan ana nufin miƙa wuya (Imani) ga dukkan abin da ya tisgo (ya zo) a cikin Alƙur’ani mai girma da hadisai ingantattu na daga sunayen Allah da da siffofinsa waɗannan da ya siffanta kansa da su, ko manzonsa ya siffanta shi da su a kan haƙiƙan (tabbaci). Waɗannan su ne muhimman kasha-kashen tauhidi da malaman Musulumci suka bayyana. 

 1.3 Taƙaitaccen Tarihin Hussaini Jikan Boka

An haifi Hussaini Jikan Boka a ƙauyen Madugu na Ƙaramar Hukumar Misau ta jihar Bauchi a shekarar 1946. Sunan mahaifinsa malam Muhammadu Ɗan Jimeta da mahaifiyarsa Malama Aishatu. Asalin mahaifinsa mutumin ƙauyen Daya Kudu maso Yamma da Potiskum da ke Ƙaramar Hukumar Fika a jihar Yobe. Ita kuma mahaifiyarsa ’yar ƙauyen Gadama ce a Ƙaramar Hukumara Misau, jihar Bauchi. Hussaini Jikan Boka ya samu wannan laƙabi na Jikan Boka ne ta wajen kakarsa ta wajen ubansa, wadda ta kasance Boka ce.

An kai Hussaini Jikan Boka makarantar Allo (Al’ƙur’ani) a garin Kuli wurin Malam Idi lokacin yana ɗan shekara tara. Bayan wasu ’yan shekaru ya koma ƙauyensu. Bayan dawowarsa gida, a wannan lokacin ne ya ga abokinsa mai suna Tintin yana kaɗa kumbi, wannan ya ba shi sha’awa. Dalilin haka ya sa shi haɗa nasa. Cikin wasu watanni ya fara zuwa wasu ƙauyuka yana waƙa. Waƙarsa ta farko ita ce da ya yi da harshen Karekarenci mai taken ’Tansuku Ma Kwarabai, ma’ana ‘A Gaya Masa Ba Ta Nan Ba’, waƙa ce ta soyayya.

Husaini Jikan Boka ya samu karɓuwa da shahara a wajen jama’a musamman ma masu kuɗi da ‘yan siyasa a dukkannin Arewacin Nijeriya da Nijar. Daga cikin mutanen da Jikan Boka ya yi wa waƙa akwai tsohon gwamnan Borno Alhaji Muhammadu Goni da Waziri Ibrahim tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa da Sanata Ahmad Aruwa da Tsoho Abdullahi Zariya da Lawandi Tabako Zariya da Hashimun Tukur Sakkwato da Shata Katsina da sauransu da yawa.

Haka nan yana da alaƙa da mawaƙan Hausa kamar su: Alhaji Mamman Shata da Haruna Uji da Ɗanmaraya Jos da sauransu. Daga bisani Hussaini Jikan Boka ya bar sana’arsa ta waƙa ya koma gida Potiskum da zama, dama a nan iyalansa suke da zama. Ya rasu a shekara ta 2007, yana da shekaru 61. Ya ya bar ‘ya’ya shida, biyar daga ciki mata, ɗaya namiji. Allah ya jikansa ya gafarta masa, amin.

2.0 Ma’anar Turke

 Gusau (2000:369), cewa ya yi‚ “Kalmar turke a lugga a taƙaice tana nufin wurin ɗaure dabba ko maɗaurin dabba ko tauye dabba ko mutum ko wani abu waje ɗaya ta yadda ba zai ɗaga ya tafi ba. Turke a ƙa’idar masu nazarin waƙar baka na nufin saƙon da waƙa take ɗauke da shi”. Ɗangambo (2007:14), ya ce‚ abin da ake nufi da jigo shi ne saƙo, ko manufa, ko abin da waƙa ta ƙunsa, wato abin da take magana a kai’.

Abba da Zulyadaini (2000: 45) sun ce a bisa ga ma’ana, Kalmar Jigo na nufin‚ Saƙon da mawaƙi yake so ya isar cikin waƙarsa ga jama’a.

Yahaya (2001:17) ya ce: “Isar da saƙo a cikin waƙa yana nufin mai sauraro ya fahimci jigon waƙar, ya kuma samu tasiri a cikin halayyarsa daga kalmomin da aka yi amfani da su cikin waƙar”.

Don haka turke yana nufin saƙo ko manufa da mawaƙi ke son isarwa ga mai sauraro, kuma shi babban maƙasudi na yin waƙa. Galibi mawaƙa kan tsara waƙoƙinsu bisa abubuwan da suka shafi rayuwar al’umma na yau da kullum da suka haɗa da; addininsu, da yanayin zamantakewarsu a gidajensu, da sauran al’amuransu na rayuwa. Husaini Jikan Boka ya yi waƙoƙi da dama, kuma bisa manufofi daban-daban daga ciki akwai kaɗaita Allah, wato tauhidi.

Jikan Boka ya yi amfani da waƙoƙinsa wajen nusar da al’umma da karantar da tafarkin muhimmi na addininsu, inda ya bayyana hanyoyin kaɗaita Allah a waƙoƙin nasa ta fuskoki guda uku da ake da su a Musulunci, wato tauhidi rububiyyah da tauhidin uluhiyya da na asma’u wassifa. Kmar yadda wannan takarda ta kawo bayaninsu dalla-dalla.

2.1 Tauhidur-rububiyya (Kaɗaita Allah da ayyukansa)

Wannan shi ne tauhidin kaɗaita Allah da ayyukansa, misali halitta da azurtawa da rayawa da kashewa da jujjuya al’amurra da kawar da cuta da makamancin waɗannan.

 Tauhidin rububiyyi ya bayyana cikin waƙar ‘Yakuba Direba’ kamar haka:

 Jagora: Ya Tabaraka ya Allah.

 : Sarki Jalla buwayi,

 : In ban da Allah sarki,

 : Ba wanda zai ba ka,

 : Yau ya ba ka gobe ya ƙara ma.

A wannan ɗan waƙa Jikan Boka ya yi wa Allah kirari ta hanyar ambaton sunayensa, inda ya ambaci kalmar ‚Tabaraka‛ wadda take nuna yawaituwar albarkar Allah, sannan ya kawo sunan Allah wanda yake nuna shi ne yake da haƙƙin abauta masa shi kaɗai. Bai tsaya a nan ba ya ci gaba har inda ya siffanta shi da Sarki Jallah Buwayi gagara misali. A ƙarshen ɗiyan sai ya bayyana cewa Allah ne kaɗai yake bayarwa yau ya bayar gobe. A dunƙule Jikan Boka yana nufin yau da gobe sai Allah, domin shi ne bai da farko kuma bai da ƙarshe, shi ya azurta halittun farko, shi ke azurta na yanzu kuma shi zai azurta halittun da za su zo nan gaba. Wannan ya nuna cewa Allah ba ya buƙatar kome, amma kowa yana da buƙata a wajensa. 

Ya ci gaba da kawo irin wannan nau’i na tauhidi a waƙarsa ta ‘Gwamna Goni’ kamar haka:

 Jagora: Zuljalali Allah Sarki,

 : Sarkin dare da rana jalla.

 : Gabar da Yamma Kudu da Arewa,

 : To na duba baba ba ya Allah Sarki,

 : Baba Jalla huwallazi mannanu,

 : Sarkin Isai da Musa da Haruna,

 : Bai hana bawa rabo ba Jafaru.

Tauhidi abu ne da ya yi nisa cikin zuciyar Jikan Boka, ta la’akari da yadda a wannan ɗan waƙa ya kawo abubuwa da dama da suka ƙunshi tauhidi. Bayan ya yi wa Allah kirari, sai ya nuna cewa Allah ne kaɗai ke da ikon kawo dare da rana, waɗanda su ne ɓangarori guda biyu da ɗan’adam ke rayuwa a ciki, kuma suna da matuƙar muhimmanci da amfani ga rayuwar tasa. Sannan a ƙarshen ɗan ya kawo Annabawa guda uku wato Annabi Isa da Musa da Haruna, ya nuna Allah ne Ubangijinsu. Lalle waɗannan manzanni ne na Allah waɗanda suka yi kira zuwa ga a bautawa Allah shi kaɗai kar a haɗa shi da kowa. A wannan ɗan waƙa Hussaini Jikan Boka ya kawo bayanai da suka shafi tauhidi na rububiyya da na uluhiyya gaba ɗaya.

2.2 Tauhidi-uluhiyyat (Kaɗaita Allah da bauta) 

Shi ne tauhidi na kaɗaita Allah da ayyukan bayi misali, addu’a da yanka da alwashi da neman taimako da neman tsari da tawakkali da wanin waɗannan. Wannan nau’i na tauhidi shi ne wanda kafurai suka musanta, kuma a nan ne aka samu jayayya tsakanin manzanni da al’ummunsu tun daga Annabi Nuhu amincin Allah ya tabbata a gare shi har zuwa ga Annabi Muhammadu (S.A.W).

Alhaji Husaini Jikan Boka a waƙarsa ta “Allah Sarki” (Bakandamiya) ya tabbatar da cewa, yarda da alƙawarin Allah na daga cikin tauhidi. Haka kuma, yin addu’a da yarda da Wuta da Aljanna gaba ɗayansu tauhidi ne na kaɗaita Allah da bauta kamar haka:

 Jagora: Alƙawarin Allah bai taɓa tashi ba,

 : Ja da baya ga rago dattijo.

 Jagora: Yadda ka yi mini sai Ziljalalu,

 : Jalla shi saka ma shi,

 : Da ma ya ba ka gidan Aljanna,

 : Baba sai in ce amin.

Tauhidi ba zai tabbata ga bawa ba har sai ya yarda da alƙawarin Allah, don haka. Husaini Jikan Boka ke jawo hankalin al’umma da cewa lallai alƙawarin Allah ba ya tashi, wato duk a bin da Allah ya faɗa a littafinsa na sakamako ga bayinsa gaskiya ne. A cikin wannan bayani akwai nusarwa ga jama’a cewa su lizimci ayyukan alkairi, don samun sakamako a lahira. Bayan haka, Husaini Jikan Boka ya yi addu’a ga wanda yake wa yabo, saboda kyautar da ya yi masa da cewa; da ma Allah ya ba shi gidan Aljanna. A nan Husaini Jikan Boka ya tabbatar cewa, yana daga cikin cikar tauhi yin addu’a da kuma yarda da gidan wuta da Aljanna. 

Jikan Boka bai tsaya a nan ba, a waƙarsa ta Ahamad Aruwa ya ci gaba da kawo tauhidi na kaɗaita Allah da ibada ya kawo tawakkali, inda yake cewa:

 Jagora: Uban Jamila ko ba kai ba,

 : Gadon hali kyawun ɗa,

 : Kowa ya bar hali, hali zai bar shi,

 : Mai tawakkali daga Allah,

 : Aikinsa ba ya ɓaci.

ƙarshen wannan ɗan waƙa Husaini Jikan Boka ya ambaci kamar tawakkali ga Allah, wanda yake nufin dogaro da miƙa dukkan al’amura ga Allah (S.W.T). Mawaƙin yana so ya nuna wa jama’a cewa, dole ne dukkan Musulmi ya yi dogaro ga Allah ɗaya, domin shi ne mai ba da kariya daga dukkan sharri, da mugunta, na aljanu, da mutane, da namun daji da sauransu. Ya ci gaba da cewa mai tawakkali da Allah, aikinsa ba ya ɓaci. Mawaƙin ya yi imani da cewa duk wanda ya mai da al’amarinsa ga Allah, zai samu nasara cikin rayuwarsa ta duniya da lahira. A ɓangare guda mawaƙin na ƙoƙarin raba jama’a da bokaye, da masu tsafi, da ‘yan bori, da masu sihiri, domin su yi riƙo da Allah shi kaɗai.

Husaini Jikan Boka a waƙarsa da ya yi wa Ahmad Aruwa ya bayyana tauhidi ta hanyar kawo littattafan da Allah ya saukar ga manzanninsa don a kaɗaita shi da bauta kamar haka:

 Jagora: Mai Linjila mai Dala’ilu,

: Mai Attaura ga Ƙur’ani,

: Ga ma’ana ko ga Tauhidi.

Mawaƙin ya lissafo manya-manyan littattafai da Allah ya saukar waɗanda suka zama wajibi a yi imani da su, domin suna cikin rukunan imani guda shida. Husaini Jikan Boka ya nuna waɗannan littattafai saukakku ne daga Allah, Linjila littafi ne da aka saukar wa Annabi Isa (A.S.), Attaura kuma ga Annabi Musa (A.S), sannan Alƙur’ani an saukar da shi ga Annabi Muhammadu (S.A.W). Dole ne Musulmi ya yi imani da waɗannan littattafai kamar yadda ya yi imani da Allah, da Mala’iku, da Annabawa, da ranar alƙiyama, da ƙaddara mai kyau da maras kyau. Ta hanyar sanin littafin da Allah ya saukar ne ake sanin Allah, da sanin yadda za a bauta masa shi kaɗai ba tare da an haɗa shi da kowa ba.

Idan aka yi la’akari da waɗannan misalai da suka gabata za a fahimci cewa, Husaini Jikan Boka ya ba da gagarumar gudummawa ga al’umma wajen nusar da su hanyar kaɗaita Allah da ayyukan bayi, wato tauhidin uluhiyya. Inda ya kawo addu’a, da tawakkali, da riƙo da littattafan da Allah ya saukar domin a kaɗaita shi da bauta. 

2.3 Tauhidi-Asma’u Was-Siffat. (kaɗaita Allah da sunaye da siffofi) 

Wannan yana nufin miƙa wuya (Imani) ga dukkan abin da ya zo a cikin Alƙur’ani mai girma da Hadisai ingantattu na daga sunayen Allah da siffofinsa, waɗannan da ya siffanta kansa da su, ko manzonsa ya siffanta shi da su, a kan haƙiƙan (tabbaci). Ga misali a cikin waƙarsa ta Shehu Na Shehu, inda ya ambaci wasu daga sunayen Alla kamar haka:

 Jagora: Zuljalali Allah Sarki,

 : Shi za shi ba ka bai ma gori.

 Jagora: Yau ya ba ka gobe shi ƙara,

 : Sai Ziljalalu ya mannanu.

A waɗanan ɗiyoyin Husaini Jikan Boka ya kawo tauhidi na asma’u wassifa da tauhidi na kaɗaita Allah da. Ya Ambato sunayen Allah mai girma huda biyu wato, Zuljalalu da kuma Allah. Waɗanna sunaye ne daga cikin sunayen Allah ɗari ba ɗaya, wanda kalmar Zuljalal na nufin Allah shi ne mai kammalalliyar ɗauka, Alƙur’ani sura ta 55, aya ta 78. Kalmar Allahu kuma na nufin abin bauta Alƙur’ani sura ta 20, aya ta 8. Waɗannan sunaye babu mai amsu sai Allah shi kaɗai, don haka wajibi ne kowane musulmi ya yi Imani da haka. Wannan ya sa Husaini Jikan Boka yake amfani da su musamman, wajen buɗe waƙoƙinsa. Ga su kamar haka: 

 Jagora: Shi za shi ba ka bai ma gori.

 : Yau ya ba ka gobe shi ƙara,

 : Sai Ziljalalu ya mannanu.

 Jagora: In Allah ya ba ka dole a ba ka,

 : In ya hana ka ba mai ba ka.

Sannan mawaƙin ya ci gaba da bayani kan tauhidi na kaɗaita Allah da ayyukansa inda ya nuna, babu wanda zai ba ka yau gobe, ya ƙara maka, sai Ziljalalu. Kuma ya nuna cewa in Allah ya ba ka dole a ba ka, in ya hana ka, babu mai ba ka. A wannan ɗiyoyin waƙa Husaini Jikan Boka yana nufin wajibi ne Musulmi ya yarda da Allah ya yi imani da shi ya dogara da ya nema a wajansa ya bi dokokinsa ya hanu da haninsa, don shi kaɗai ne mai ba shi arziki da lafiya da haihuwa. Kuma shi ne yake jarrabar sa da talauci da rashin lafiya da rashi haihuwa da sauransu.

 Jagora: Kan da rai da rabo,

 : Yau kan babu rai rabo yau babu.

Haka zalika Husaini Jikan Boka ya ci gaba da bayyana kaɗaituwar Allah, inda ya nuna kowane rai da Allah ya halitta ya sanya masa arzikinsa. Dan haka yake cewa in har mai rai yana halin rayuwa to yana tare da rabo, wannan ya ƙunshi duk abin da mutane da tsintsaye da dabbobi da ƙwari suke rayuwa da su, da suka haɗa da; abinci da ruwa da sutura da mahalli da yawan kwanakin rayuwa da duk wani abu da ɗan’adam zai mallaka. Mawaƙin ya bayyana cewa Allaha yakan ba wa halitta rabo ne a yayin da yake halin raye, amma da zarar rai ya yi halinsa to rabo ya ƙare. Abin da mawaƙin ke nufi shi ne, babu wani mai rai da zai mutu, face kafin yam utu sai iya rabon da Allah y a ba shi sun ƙare. Wannan yana karantar da al’umma cewa, su bar baƙin ciki da hassada da ƙyashi da zagon ƙasa da ƙeta a tsakaninsu, domin kowa rabonsa yake ci.

 Jagora: Na Shehu na Shehu,

 : Gobara daga kogi,

 : Ba mai tare ki sai Lillahi,

 : Sai Ziljalalu shi kan tare ta,

: Na shehu ka san daidai. 

A wannan ɗan waƙa Jikan Boaka ya fito da iko da ƙudura da ɗaukar Allah (S.W.A), inda yake cewa gobara daga kogi ba mai tare ta sai Lillahi. Mawaƙin yana nufin duk wani abin da ya gagari ɗan Adam ko fi ƙarfin tunaninsa ba zai gagari Allah ba. Don haka mawaƙin ya yi amfani da misali mai kama hankali inda ya ce, ‘gobara daga kogi’, kowa ya san kogi wuri da yake cike da ruwa, ruwa kuwa shi yake kashe wata, idan aka ce ga wuta daga cikin ruwa lalle zai zama abin mamaki, babu shakka hankalin mutum zai tashi domin abun ya fi ƙarfinsa sai dai Allah. Don haka mawaƙin yana faɗakarwa tare da nusarwa ga al’umma da su kiyaye dokokin Allah su yi masa ɗa’a, lallai shi ne mai taimakonsu cikin abin da ya fi ƙarfinsu. 

3.0 Kammalawa

Mawaƙi Husaini Jikan Boka ya tabbata mutum ne da ya tasirantu da addini kamar yadda aka gini gurare da dama cikin waƙoƙinsa yadda faɗakarwa kan tauhidi ya mamaye da yawa daga cikin waƙoƙin. A wannan takarda an lalumo fannoni na tauhidi guda uku daga cikin waƙoƙin na Husaini Jikan Boka, wato tauhidi na rububiyya (kaɗaita Allah da Ayyukansa) da na uluhiyya (kaɗaita Allah da Ibada) da na Asma’u Was-siffat (kaɗaita Allah da sunayensa).

Manazarta

Altine, H. (1983). “Aliyu Ɗandawo Da Waƙoƙinsa”. Kundin Digiri na Farko, Jami’ar Usman Ɗanfodiyo, Sakkwato.

Asimina, S. M. S. (1989). “Attauhidu Walfiƙhu Wat-tajwid Lil-Faslir Rabi’u Al-Ibtida’iyyat. MahfulzatilWizaratil Ma’arif. Saudi Arabiyya.

Bunza, U. A. (2001). “Taɓa Kiɗi Taɓa Karatu: Tauhidi A Bakin Makaɗan Bakan Hausa”. Kundin Digiri na Farko, Jami’ar Usaman Ɗanfodiyo, Sokkwato.

Bunza, U. A. (2013). “Wa’azi A Bakin Gambo Dogo Mai Kalangu”. Cikin Mujallar Makaɗi A Mahangar Manazarta. Jerin takardun da aka gabatar a taron ƙara wa juna sani kan Tubar Muahammadu GambonMai Kalangu, Sashen Nazarin Harsunan Nijeriya, Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo, Sokoto. ISBN. No: 978-8082-02-5.

Gumel, M. A. (1992). “Tarbiyya Da Dangoginta A Waƙoƙin Makaɗan Baka Na Hausa”. Kundin Digiri na Farko, Jami’ar Bayero, Kano.

Gusau, S. M. (1993). Jagoran Nazarin Waƙar Baka. Fisbas Media Serɓices, Kaduna.

Gusau, S.M. (1996). Makaɗa Da Mawaƙa Na Hausa. Fisbas Media Serɓices, Kaduna. Yobe Journal of Language, Literature and Culture (YOJOLLAC)

Post a Comment

0 Comments