Ticker

6/recent/ticker-posts

Shekarar Da Za a Yi Tashin Kiyama

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Assalaamu Alaikum Wa Rahmatul Laah. Malam, da gaske ne cewa wai akwai hadisin da Manzon Allaah (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) ya ce, ba zai yi shekaru dubu biyu (2000) a ƙasa ba za a yi Tashin Ƙiyamah?

TASHIN ƘIYAMAH

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Wa Alaikumus Salaam Wa Rahmatul Laahi Wa Barakaatuh.

A gaskiya ban san wannan hadisin ba, sai dai ko in mun tuntuɓi malamai.

Daga baya an nuna mini kuma na ga:

Al-Imaam As-Suyuutiy (Rahimahul Laah) a cikin Al-Kashfu An Mujaawazati Hazihil Ummatil Alfa ya ambaci cewa:

فَقَدْ كَثُرَ السُّؤَالُ عَنِ الْحَدِيثِ الْمُشْتَهَرِ عَلَى أَلْسِنَةٍ ، أَنَّ النَّبِيَّ - صَلَّى اللهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ - لَا يَمْكُثُ فِي قَبْرِهِ أَلْفَ سَنَةٍ

Haƙiƙa! Tambaya ta yawaita a kan hadisin da ya shahara a kan waɗansu harsuna cewa: Annabi (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) ba zai zauna a cikin ƙabarinsa tsawon shekaru dubu ɗaya ba.

Sai kuma ya bayyana hukuncinsa a kan wannan riwayar, ya ce:

وَأَنَا أَجِيبُ بِأَنَّهُ بَاطِلٌ ، لَا أَصْلَ لَهُ

Kuma ni ina bayar da amsa cewa: Shi lalatacce kuma ɓataccen hadisi ne, ba shi da wani asali.

Kuma Al-Imaam Ibn Al-Qayyim (Rahimahul Laah) a cikin Al-Mannaarul Muneef Fis Saheeh Wad Da’eef ya faɗa, a inda yake bayar da amsa a kan wata fatawa cewa:

وَسُئِلْتُ: هَلْ يُمْكِنُ مَعْرِفَةِ الْحَدِيثِ الْمَوْضَوعِ بِضَابِطٍ مِنْ غَيْرِ أَنْ يُنْظَرَ فِي سَنَدِهِ

Kuma an tambaye ni: Shin ko zai yiwu a iya sanin hadisin ƙarya ƙirƙirarre ta amfani da waɗansu ƙaidoji, ba tare da an kalli isnadinsa ba?

Shi ne a cigaba da bayar da ƙaidojin ya faɗa a shafi: 80 ya ce:

وَمِنْهَا: مُخَالَفَةُ الْحَدِيثِ صَرِيحَ الْقُرْآنِ ، كَحَدِيثِ مِقْدَارِ الدُّنْيَا ، وَأَنَّهَا سَبْعَةُ آلَافِ سَنَةً ، وَنَحْنُ فِي الْأَلْفِ السَّابِعَةِ

Kuma daga cikin su: A samu hadisin yana saɓawa a fili ƙarara da Alqurani, kamar hadisin tsawon shekaru duniya, wai cewa shekaru dubu bakwai ne, kuma wai muna a cikin dubu na bakwai ɗin ne!

Daga nan ne kuma ya ce:

وَهَذَا مِنْ أَبْيَنِ الْكَذِبِ ، لِأَنَّهُ لَوْ كَانَ صَحِيحًا لَكَانَ كُلُّ أَحَدٍ عَالِمًا أَنَّهُ قَدْ بَقِيَ لِلْقِيَامَةِ مِنْ وَقْتِنَا هَذَا مِئتَانِ وَأَحَدَ وَخَمْسُونَ سَنَةً

Kuma wannan yana daga cikin mafiya bayyanar ƙarairayi, domin idan da riwayar ingantacciya ce, to kuwa da kowa ya san cewa abin da ya rage daga lokacin nan namu zuwa Ƙiyama shekaru ɗari biyu ne da hamsin da ɗaya!

Sannan kuma Al-Haafiz Ibn Katheer (Rahimahul Laah) ya faɗa a cikin An-Nihaayah Fil Fitani Wal Malaahim cewa:

لَمْ يَصِحَّ عَنِ الرَّسُولِ أَنَّهُ لَا يَمْكُثُ فِي الْأَرْضِ قَبْلَ السَّاعَةِ أَلْفَ سَنَةٍ ، وَلَمْ يُحَدِّدِ الرَّسُولُ مُدَّةً مُعَيَّنَةً لِقِيَامِ السَّاعَةِ

Bai inganta daga Manzon Allaah (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) ba cewa, shi ba zai zauna a cikin ƙasa kafin Saar Ƙiyama na tsawon shekaru dubu ɗaya ba. Kuma Manzon Allaah (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) bai iyakance wani lokaci ayyananne na tsayuwar Sa’ar ba.

Sai kuma ya ce (shafi na: 6 a lissafin Shaamilah):

فَأَمَّا مَا يُورِدُهُ كَثِيرٌ مِنَ الْعَامَّةِ مِنْ أَنَّ النَّبِيَّ - صَلَّى اللهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ - لَا يُؤَلِّفُ تَحْتَ الْأَرْضِ فَلَيْسَ لَهُ أَصْلٌ . وَلَا ذُكِرَ فِي كُتُبِ الْحَدِيثِ الْمُعْتَمَدَةِ ، وَلَا سَمِعْنَاهُ فِي شَيْءٍ مِنَ الْمَبْسُوطَاتِ ، وَلَا شَيْءٍ مِنَ الْمُخْتَصَرَاتِ ، وَلَا ثَبَتَ فِي حَدِيثٍ عَنِ النَّبِيِّ - صَلَّى اللهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ - أَنَّهُ حَدَّدَ وَقْتَ السَّاعَةِ بِمُدَّةٍ مَحْصُورَةٍ ، وَإِنَّمَا ذَكَرَ شَيْئاً مِنْ أَشْرَاطِهَا وَأَمَارَاتِهَا وَعَلَامَاتِهَا . اهـ

Amma dai abin da masu yawa daga cikin gama-garin mutane suke riwaitowa wai Annabi (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) ba zai yi shekaru dubu a ƙarƙashin ƙasa ba, wannan kam ba shi da wani asali. Kuma ba a ambace shi a cikin littaffan hadisi da ake dogaro da su ba. Kuma ba mu ji shi a cikin wani abu daga cikin manyan littaffai ba, haka ma ko a wani abu daga cikin taƙaitattun littaffan ba. Kuma bai tabbata daga Annabi (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) ba cewa shi ya iyakance lokacin aukuwar Saar Ƙiyama da wani lokaci iyakantacce. Kaɗai, ya ambaci wani abu ne kawai daga cikin alamominta.

Daga waɗannan bayanai za mu gane cewa:

Akwai riwaya da ta shahara a bakunan waɗansu mutanen da ba malaman hadisi ba cewa: Annabi (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) ba zai yi shekaru dubu ɗaya a ƙasa ba Al-Ƙiyama za ta tsaya!

Sai dai wannan riwaya ba ingantacciya ba ce, riwaya ce ƙirƙirarriya, ta ƙarya kawai, kamar yadda Hafizai masana hadisi irin su Ibn Katheer da Ibn Al-Qayyim da As-Suyuutiy (Rahmatul Laahi Alaihim) suka yi bayani.

Me yiwuwa ganin cewa shekaru dubun sun wuce da rasuwar Annabi (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) amma har yanzu Ƙiyamar ba ta tsaya ba, shiyasa waɗansu suka sake ɗauko waccan riwayar kuma suka yi mata kwaskwarima, suka mayar da ita: Shekaru dubu biyu!

Allaah ya kiyaye.

Amma abin da Allaah Subhaanahu Wa Ta’aala ya ce dai shi ne:

یَسۡـَٔلُونَكَ عَنِ ٱلسَّاعَةِ أَیَّانَ مُرۡسَىٰهَاۖ قُلۡ إِنَّمَا عِلۡمُهَا عِندَ رَبِّیۖ لَا یُجَلِّیهَا لِوَقۡتِهَاۤ إِلَّا هُوَۚ ثَقُلَتۡ فِی ٱلسَّمَـٰوَ ٰتِ وَٱلۡأَرۡضِۚ لَا تَأۡتِیكُمۡ إِلَّا بَغۡتَةࣰۗ یَسۡـَٔلُونَكَ كَأَنَّكَ حَفِیٌّ عَنۡهَاۖ قُلۡ إِنَّمَا عِلۡمُهَا عِندَ ٱللَّهِ وَلَـٰكِنَّ أَكۡثَرَ ٱلنَّاسِ لَا یَعۡلَمُونَ

Suna tambayar ka akan Sa’ar Ƙiyama wai yaushe ne lokacin aukuwar ta? Ka ce: Kaɗai, iliminta yana wurin Ubangijina ne. Babu mai iya bayyanar da ita ga lokacinta sai dai shi kawai. Ta yi nauyi a cikin sammai da ƙasa. Ba za ta zo muku ba sai dai afke kawai. Suna tambayar ka kamar dai kai masani ne a kan ta. Ka ce: Iliminta yana wurin Allaah ne, sai dai kuma yawancin mutane ba su sani ba. (Surah Al-Araaf: 187)

Sannan kuma Manzon Allaah (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) ya ce:

« مَا الْمَسْئُولُ عَنْهَا بِأَعْلَمَ مِنَ السَّائِلِ »

Wanda aka tambaye shi a kan ta bai fi wanda ya yi tambayar sani ba. (Sahih Muslim: 102)

Wannan kaɗai ya isa dalili da zai nuna rashin ingancin wancan hadisin.

Allaah ya saka wa malamai da ɗaliban hadisi da alkahiri a duk inda su ke, kuma ya ƙara mana kyakkyawar fahimta a cikin addininmu.

Wal Laahu A’lam.

Sheikh Muhammad Abdullaah Assalafiy

Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance damu cikin wannan group domin Fadakarwa...

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

WALLAHU A'ALAM.

https://t.me/TambayaDaAnsa

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments