𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu Alaikum malam Yaya ake yin Salaatut Tasbeeh? Mene ne ingancin ta?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
W Alkm Slm W Rhmtul
Laah.
Salaatut-Tasbeehi
wata Sallah ce mai raka’o’i huɗu wadda ake karanta Tasbihi har sau ɗari uku a cikinta.
Lafazin Tasbihin shi ne: ‘SUBHĀNAL LĀH, WAL HAMDU LIL LĀH, WA LĀ ILĀHA ILLAL
LĀH, WAL LĀHU AKBAR’.
Ma’ana: Tsarki ya
tabbata ga Allaah, kuma Godiya ta tabbata ga Allaah, kuma babu abin bautawa da
gaskiya sai Allaah, kuma Allaah ne mai Girma.
Shari’ar Musulunci ta
kwaɗaita wa masu Imāni
yin wannan sallar. Tana jawo wa musulmi gafarar Zunubansa na farko, da
Zunubbansa na ƙarshe, da Zunubbansa daɗaɗɗu, da Zunubbansa sababbi, da Zunubbansa da ya
yi cikin kuskure, da Zunubbansa da ya yi da gangan, da Zunubansa ƙanana da Zunubbansa
manya, da Zunubbansa na ɓoye, da Zunubbansa na
bayyane.
Kuma an so a riƙa yin wannan sallar
sau ɗaya a kowace rana in
da hali, ko sau ɗaya a kowane mako, ko
sau ɗaya a kowane wata, ko
sau ɗaya a kowace shekara.
Idan kuma ba haka ba, to sai ya yi ko da sau ɗaya a cikin rayuwarsa.
Haka mālaman Hadisi
irin su: Al-Imām Muslim, da Al-Imām Abu-Dāwud, da Al-Imām As-Subkiy da Al-Hāfiz
Ibn. As-Salāh, da Al-Hāfiz Ibn. Hajr Al-Asqalāniy, da Al-Mujaddid Al-Albaaniy
(Rahmatul Laahi Alaihim) duk sun kyautata wannan hadisin saboda yawan hanyoyinsa.
Kamar kuma yadda aka
samu wasu malaman irin su: Al-Imām Al-Baihaqiy yana cewa: ‘Abdullāh Bn
Al-Mubārak ya kasance yanā yin Salātut-Tasbihi, kuma sashen mālaman ƙwarai (Sahihai) sun
riƙa
koyonta daga sashensu!’
SIFFAR YADDA AKE YIN
SALAATUT TASBEEH:
1. Da farko musulmi
zai yi shiri irin shirinsa na sallah, ya yi alwala sannan ya fuskanci alƙibla, ya yi niyyar
yin Salātut-Tasbihi a zuciyarsa ba a baki ba, yana
mai furta kabbarar harama da bakinsa.
2. Zai ɗora hannun damarsa a
kan na hagunsa a bisa ƙirjinsa kamar dai yadda tsayuwar mai sallah ta ke, sannan
ya karanta Fātihah da Sūrah bayan ‘Du’ā’ul
Istiftāhi’.
3. Bayan ya kammala
karatun Sūrāh, sai ya ce: ‘SUBHĀNAL LĀH, WAL HAMDU LIL LĀH, WA LĀ ILĀHA ILLAL
LĀH, WAL LĀHU AKBAR’ sau goma sha biyar (15), sannan ya yi kabbara ya yi
ruku’u.
4. A cikin ruku’u
bayan ya ƙare zikirorin da aka saba yi, sai ya sake faɗin ‘SUBHĀNAL LĀH, WAL
HAMDU LIL LĀH, WA LĀ ILĀHA ILLAL LĀH, WAL LĀHU AKBAR’ sau goma (10). Sai kuma
ya ɗago daga Ruku’un.
5. Bayan ya gama
zikirorin ɗagowa da tsayuwa da
bayan ruku’u sai kuma ya ce: ‘SUBHĀNAL LĀH, WAL HAMDU LIL LĀH, WA LĀ ILĀHA
ILLAL LĀH, WAL LĀHU AKBAR’ sau goma (10), sannan ya yi sujada.
6. Bayan ya gama
zikirorin da aka saba yi a cikin sujada sai kuma ya ce: ‘SUBHĀNAL LĀH, WAL
HAMDU LIL LĀH, WA LĀ ILĀHA ILLAL LĀH, WAL LĀHU AKBAR’ sau goma (10). Sai kuma
ya ɗago daga sujadar.
7. A zama tsakānin
sujadu biyu zai karanta zikirorin da aka saba yi a wurin kafin ya ce: ‘SUBHĀNAL
LĀH, WAL HAMDU LIL LĀH, WA LĀ ILĀHA ILLAL LĀH, WAL LĀHU AKBAR’ sau goma (10).
Sannan ya koma ya yi sujada ta biyu.
8. A cikin sujada ta
biyu zai karanta zikirorinsa kamar yadda ya yi a sujada ta farko, sannan ya ce:
‘SUBHĀNAL LĀH, WAL HAMDU LIL LĀH, WA LĀ ILĀHA ILLAL LĀH, WAL LĀHU AKBAR’ sau
goma (10). Sai kuma ya ɗago daga sujadar ta
biyu ya zauna.
9. A cikin wannan
zaman da mālaman Fiƙ-hu suke kira ‘Jilsatul Istirāhah’
babu wani zikiri da ake yi a asali, don haka sai dai kawai ya ce: ‘SUBHĀNAL
LĀH, WAL HAMDU LIL LĀH,
WA LĀ ILĀHA ILLAL LĀH,
WAL LĀHU AKBAR’ sau goma (10). Daga
nan sai kuma ya miƙe tsaye zuwa raka’a ta biyu.
10. A cikin raka’a ta
biyu zai yi kamar yadda ya yi a raka’a ta farko, sai kuma ta uku sannan ta huɗu.
A kowace raka’a, zai
ga ya faɗi ‘SUBHĀNAL LĀH, WAL
HAMDU LIL LĀH, WA LĀ ILĀHA ILLAL LĀH, WAL LĀHU AKBAR’ sau saba’in da biyar (75)
ke nan. A cikin raka’o’in huɗu kuma ya samu faɗi har sau ɗari uku (300) kenan daidai!
Allaah ya ƙara mana taimako da
himma a kan karatun Hadisi da Aiki da Shi.
Ina ga wannan bayani
ya amsa wannan fatawar, in shaa’al Laah.
Wal Laahu A’lam.
Sheikh Muhammad
Abdullaah Assalafiy
Zauren Fatawoyi Bisa
Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance damu cikin wannan group domin Fadakarwa...
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.