Ticker

6/recent/ticker-posts

Mene ne Hukuncin Kaffarar Kisan Kuskure Ga Mutum Fiye Da Guda, Kuma Shin Shekaru Suna Tasiri Ga Hukuncin Shari'a?

Kaffarar Kisan Kai

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

As-Salaam Alaikum Wa Rahmatul Laah. Saurayi ne bai kai shekaru 18 ba yake tuka mota, kuma ya yi hatsari har mutane biyu suka rasu. To, shin zai yi azumi guda 60 ne, ko kuwa 120?

𝐀𝐌𝐒𝐀

Wa Alaikumus Salaam Wa Rahmatul Laah Wa Barakaatuh.

Dokokin shari’a suna hawa kan mutumin da ya zama Musulmi ne baligi mai hankali, ko ya kai 18 ko bai kai ba.

Wanda ya janyo mutuwar wani mutum da gangar, watau: Ya yi nufin kashe shi, kuma ya yi amfani da abin da aka san yana kashewa a al’ada, kamar ya buge shi ko ya take shi da mota da gangar, to hukuncinsa na asali shi ne, shi ma a kashe shi. Amma idan dangin mamacin suka yafe masa ƙisasin, watau suka ce ba sai an kashe shi ba, to sai a biya diyya. A ba na wannan diyyar, kamar yadda Timing Chapter suka bayyana, ta kama naira miliyan hamsin da biyu, da dubu ɗari huɗu da talatin da bakwai, da naira ɗari biyu da shida, da kwabo talatin da bakwai (N52,437,206.37), idan wanda aka kashe ɗin namiji ne Musulmi.

Amma idan mace ce Musulma, ko kuma wani kafirin amana ne to, rabin diyya namiji Musulmi za a biya, watau: N26,218,603.19.

Idan kuma ba da gangar ne direban ya janyo mutuwar mutumin ba, ma’ana: A bisa kuskure ne ba da ganganci ne ya buge shi da motar ba, to a nan akwai abubuwa biyu:

1. Diyya da dangin mai kisan za su biya dangin mamacin, watau N52,437,206.37 cikin gaggawa, idan suna da hali. Idan kuma talakawa ne sai a jinkirta musu su biya a cikin shekaru uku.

2. Azumin watanni guda biyu a jere, da wanda ya yi kisan zai yi a lokacin da ba zai iya ’yanta baiwa guda ɗaya mumina ba. (Surah An-Nisaa’i: 92):

وَمَا كَانَ لِمُؤْمِنٍ أَنْ يَقْتُلَ مُؤْمِنًا إِلَّا خَطَأً ۚ وَمَنْ قَتَلَ مُؤْمِنًا خَطَأً فَتَحْرِيرُ رَقَبَةٍ مُؤْمِنَةٍ وَدِيَةٌ مُسَلَّمَةٌ إِلَىٰ أَهْلِهِ إِلَّا أَنْ يَصَّدَّقُوا ۚ فَإِنْ كَانَ مِنْ قَوْمٍ عَدُوٍّ لَكُمْ وَهُوَ مُؤْمِنٌ فَتَحْرِيرُ رَقَبَةٍ مُؤْمِنَةٍ ۖ وَإِنْ كَانَ مِنْ قَوْمٍ بَيْنَكُمْ وَبَيْنَهُمْ مِيثَاقٌ فَدِيَةٌ مُسَلَّمَةٌ إِلَىٰ أَهْلِهِ وَتَحْرِيرُ رَقَبَةٍ مُؤْمِنَةٍ ۖ فَمَنْ لَمْ يَجِدْ فَصِيَامُ شَهْرَيْنِ مُتَتَابِعَيْنِ تَوْبَةً مِنَ اللَّهِ ۗ وَكَانَ اللَّهُ عَلِيمًا حَكِيمًا

Kuma bã ya kasancwa ga mũmini ya kashe wani mũmini, fãce bisa ga kuskure. Kuma wanda ya kashe mũmini bisa ga kuskure, sai ya 'yanta wuya mũmina tare da mĩƙa diyya ga mutãnensa, ãce idan sun bari sadaka. Sa'an nan idan (wanda aka kashe) ya kasance daga wasu mutãne maƙiya a gare ku, kuma shi mũminine, sai ya 'yanta wuya mũmina. Kuma idan ya kasance daga wasu mutãne ne (waɗanda) a tsakãninku da tsakãninsu akwai alkawari, sai ya bãyar da diyya ga mutãnensa, tare da 'yanta wuya mũmina. To, wanda bai sãmi (wuyan ba) sai azumin watanni biyu jre, dõmin tũba daga Allah. Kuma Allah Yã kasance Masani, Mai hikima.

Amma idan waɗanda ya janyo rasuwarsu a cikin motar sun fi mutum guda, to abin da ke wajibi shi ne diyya ga dangin kowane ɗaya daga cikin mutanen, sannan kuma da yin kaffara na azumi a maimakon kowannensu. Watau ke nan a nan, azumman watanni biyu ke nan a jere zai yi har sau biyu.

Amma malamai sun bayar da fatawar cewa, ba dole ne ya jera azumma na dukkan watannin ba. Ma’ana, zai iya yin azumin watanni biyu na mamaci ɗaya, daga baya kuma in ya huta sai ya sake yin na wani mamacin. (Fataawa Al-Lajnah Ad-Daa’imah Lil Buhuuthil Ilmiyyah Wal iftaa’: 21/268; # 4760).

Allaah ya ƙara mana kariya da shiriya.

Wal Laahu A’lam._

Sheikh Muhammad Abdullaah Assalafiy

Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance damu cikin wannan group domin Fadakarwa...

ƘARIN BAYANI

HUKUNCIN KAFFARAR KISAN KUSKURE DA RABON DIYYA A MUSULUNCI

TAMBAYA:

Wani matashi ne wanda bai kai shekaru 18 ba ya yi hatsarin mota wanda ya yi sanadiyyar mutuwar mutane biyu. Shin akwai kaffara a kansa tunda bai kai shekaru 18 ba? Kuma idan har akwai kaffarar, azumin watanni biyu (kwanaki 60) zai yi na mutanen gaba ɗaya, ko kuwa kowane mamaci yana da kaffararsa daban (wato watanni huɗu ke nan)?

AMSA:

A cikin shari’ar Musulunci, nauyin hukunci yana ta’allaka ne da siffar "Balaga" da "Hankali." Idan har matashin nan ya riga ya balaga (ta hanyar alamomin balaga da aka sani a shari’a), to dukkan hukunce-hukuncen shari’a sun hau kansa, komai ƙarancin shekarunsa a lissafin gwamnati. Kisan da ya faru sakamakon hatsarin mota ana kiransa "Kisan Kuskure" (Al-Qatl al-Khata’), domin direban ba shi da nufin kashe mutanen, sai dai rashin kiyaye ƙa'idojin tuki ko tsautsayi ya janyo hakan.

Akwai haƙƙoƙi guda biyu da suka rataya a kan wannan kisa:

1.         Diyya (Haƙƙin Bayi): Wannan dukiyar da ake biya wa dangin mamaci don rarrashin zuciya da maye gurbin rashi.

2.         Kaffara (Haƙƙin Allah): Wannan ibada ce da mai kisan zai yi don neman gafarar Allah kan gangancin da ya kai ga asarar rai.

1. Adadin Kaffara Ga Mutane Da Yawa

Idan mutum ya kashe mutane fiye da guda a kuskure ɗaya (kamar hatsarin mota), malaman fikihu sun yi ittifaƙi cewa kaffara tana ninkuwa ne gwargwadon yawan rayukan da aka rasa. Rayuwar kowane musulmi tana da daraja ta kanta, don haka ba a haɗa kaffararsu a azumi guda. Saboda haka, wannan matashi zai yi azumin watanni biyu a jere (60) ga mamacin farko, sannan ya sake yin wasu watanni biyu a jere (60) ga mamaci na biyu. Jimullar kwanakin azumin zai zama kwanaki 120 (ko watanni huɗu na Musulunci).

Allah Madaukakin Sarki ya bayyana wajibcin kaffara a cikin littafinsa mai tsarki:

وَمَا كَانَ لِمُؤْمِنٍ أَنْ يَقْتُلَ مُؤْمِنًا إِلَّا خَطَأً ۚ وَمَنْ قَتَلَ مُؤْمِنًا خَطَأً فَتَحْرِيرُ رَقَبَةٍ مُؤْمِنَةٍ وَدِيَةٌ مُسَلَّمَةٌ إِلَىٰ أَهْلِهِ إِلَّا أَنْ يَصَّدَّقُوا ۚ فَإِنْ كَانَ مِنْ قَوْمٍ عَدُوٍّ لَكُمْ وَهُوَ مُؤْمِنٌ فَتَحْرِيرُ رَقَبَةٍ مُؤْمِنَةٍ ۖ وَإِنْ كَانَ مِنْ قَوْمٍ بَيْنَكُمْ وَبَيْنَهُمْ مِيثَاقٌ فَدِيَةٌ مُسَلَّمَةٌ إِلَىٰ أَهْلِهِ وَتَحْرِيرُ رَقَبَةٍ مُؤْمِنَةٍ ۖ فَمَنْ لَمْ يَجِدْ فَصِيَامُ شَهْرَيْنِ مُتَتَابِعَيْنِ تَوْبَةً مِنَ اللَّهِ ۗ وَكَانَ اللَّهُ عَلِيمًا حَكِيمًا

Hausa: "Kuma ba ya kasancewa ga muminin ya kashe wani mumini, face bisa ga kuskure. Kuma wanda ya kashe mumini bisa ga kuskure, sai ya 'yanta wuya mumina tare da mika diyya ga mutanensa, face idan sun bari sadaka. To, idan (wanda aka kashe din) ya kasance daga wasu mutane makiya a gare ku, alali shi muminin ne, sai ya 'yanta wuya mumina. Kuma idan ya kasance daga wasu mutane (wadanda) a tsakaninku da tsakanninsu akwai alkawari, sai ya bayar da diyya ga mutanensa tare da 'yanta wuya mumina. To, wanda bai sami (wuyan ba) sai azumin watanni biyu jere, domin tuba daga Allah. Kuma Allah Ya kasance Masani, Mai hikima." (Suratun Nisa'i: 92).

2. Tsarin Yin Azumin

Ba lallai ba ne mutum ya jera dukkan watanni huɗun lokaci guda ba tare da hutu ba. Sharɗin shari'a shi ne kowane mutum ɗaya a jera masa watanni biyu. Bayan ya kammala na mutum na farko, zai iya hutu na wasu kwanaki ko makonni don ya samu ƙarfin jiki, sannan ya fara na biyu. Babban muhimmanci shi ne kada ya yanke azumin a cikin watanni biyun da yake yi wa mutum ɗaya, sai dai in akwai dalili na shari'a kamar rashin lafiya ko tafiya.

3. Batun Diyya (Diyar Kuskure)

Diyyar kisan kuskure ba a wuyan mai motar take ba kai tsaye; tana kan danginsa ne na maza (wato Al-Aqilah). Wannan shi ne tsarin Musulunci don rage wa mutum ɗaya nauyi. Idan dangin ba su da halin biya, sai nauyin ya koma ga baitul-mali ko kuma shi kansa idan yana da hali. Amfanin diyya shi ne rage raɗadin rashi ga iyalan mamaci.

An ruwaito daga Abu Hurairah (R.A) ya ce:

اقْتَتَلَتِ امْرَأَتَانِ مِنْ هُذَيْلٍ، فَرَمَتْ إِحْدَاهُمَا الأُخْرَى بِحَجَرٍ فَقَتَلَتْهَا وَمَا فِي بَطْنِهَا، فَقَضَى رَسُولُ اللَّهِ صلى الله عليه وسلم أَنَّ دِيَةَ جَنِينِهَا غُرَّةٌ عَبْدٌ أَوْ وَلِيدَةٌ، وَقَضَى بِدِيَةِ الْمَرْأَةِ عَلَى عَاقِلَتِهَا

Hausa: "Wasu mata biyu daga ƙabilar Huzail sun yi faɗa, ɗaya ta jifi ɗayar da dutse ta kashe ta da abin da ke cikinta (ciki). Sai Manzon Allah (S.A.W) ya yi hukunci cewa diyar jaririn da ke cikinta bawa ne ko baiwa, sannan ya yi hukuncin diyar matar a kan danginta (maza)." (Buhari da Muslim).

4. Muhimmiyar Fadakarwa Kan Tuki

Wannan hatsari ya zama izina ga iyaye da suke barin yara ƙanana suna tuka mota ba tare da sun kware ba ko ba tare da bin doka ba. Shari'a tana kallon duk wanda ya jawo asarar rai sakamakon sakaci a matsayin wanda zai fuskanci kaffara da diyya. Koda kuwa matashin bai kai shekaru 18 ba, matukar ya balaga, to ya zama mutum mai cikakken nauyi (Mukallaf).

A taƙaice, wannan matashi zai yi azumin watanni huɗu (biyu-biyu a jere ga kowane mamaci), sannan danginsa su biya diyya ga iyalan mamatan, sai dai idan iyalan sun yafe musu. Wannan shi ne zai zama sanadin samun gafarar Allah da kuma tsarkake kansa daga wannan babban laifi na asarar rayuka.

WALLAHU A'ALAMU

 ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

WALLAHU A'ALAM.

https://t.me/TambayaDaAnsa

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments