Ticker

6/recent/ticker-posts

Kowa Ya Bar Gida

Bello Sambo (2020). Kowa Ya Bar Gida. Muhalli, Sutura (Labaran Da Suka Samu Nasara a Gasar Gajerun Labarai a Kan Muhalli Ta Arc. Ahmed Musa Dangiwa, 2020). Darma Digital Prints.

KOWA YA BAR GIDA

Na

Bello Sambo

Babban zauren taron na Event House, a cike y ke da mahalarta, ta ko’ina ka duba jama’a ne, ya yin da a can saman dandamali kuma manyan baƙi ne, da shugabannin taron a zaune. Daga bayansu kuwa wani babban ƙyalle ne, da ke ɗauke da manyan rubutu kamar haka:

Barka da zuwa bikin bayar da takardar girmamawa ga ƙungiyar Muhallinka Alfarmarka

 Rana: Asabar 21, ga Maris, 2020

 Lokaci: Ƙarfe 10 na safe

 Wuri: Ɗakin taro na Event House

Shugabannin taron sun yi bayanai da dalilan shirya taron domin karramawar ƙungiyar, haka manyan baƙi mahalarta taron, duk sun tofa albarkacin bakunansu. A ƙarshe bayan jama’a da dama sun gama jawabai, sai aka kira shugaban ƙungiyar Malam Hamza Sa’idu, kuma wanda ya ƙirƙiri ƙungiyar, da ya fito ya yi wa mahalartan, bayanin dalilan da suka sa shi ya ƙirƙiri wannan ƙungiyar, da aiyukanta suke da tarin fa’idoji da alfanu, ga al’ummar wannan gari.

 A lokacin da malam Hamza, ya fito ya hau dandalin taron, aka ba shi abin magana, sai aka ɗauki tafi raf!Raf!!Raf!!! Bayan an natsu, sai ya yi gyaran murya sannan ya ce,

 “Iyayen taro, da manyan baƙi da sauran jama’a mahalarta maza da mata, ina ma ku sallama irin ta addinin Musulunci.” Bayan an amsa, sai ya ci gaba, “ Haƙiƙa an yi man babbar tambaya da aka buƙaci in fadi dalilan da suka sa na ƙirƙiri ƙungiyar MUHALLINKA ALFARMARKA. Tabbas mun sani babu wani abu da ke faruwa ba tare da wani dalili na fili, ko na ɓoye ba. Domin bayyana maku dalilin assasa wannan ƙungiyar zan ɗauke ku zuwa shekaru uku baya.

 Sunana Hamza Sa’idu, magidanci mai mata ɗaya da yara biyu, ƙaramin ma’aikacin gwamnati ne ni. Ina zaune ne a gidan haya, kasancewar ban da muhalli nawa na kaina. Sai dai a lokacin ina da fili da nake gina nawa gidan, amma zamowa ta maras nauyin aljihu, da kuma matsalolin da na riƙa fuskanta a gidajen haya, ya sa aikin ke tafiyar hawainiya, har ya ci tsawon lokaci bai kammalu ba.

 Na mallaki filin ne tun kafin aurena, sakamakon shawarar da mahaifina ya ban, cewa a wannan lokaci matashi kamata ya yi kafin ya yi aure, in da hali ya mallaki gidansa, in hakan bai samu ba to a ƙalla ya mallaki ko fili ne, bayan ya yi auren sai ya ci gaba da aikin ginin a hankali, domin ya kauce wa tarnaƙin gidan haya. Saboda haka sai wannan shawarar ta zaburar da ni, na sayi fili a wata sabuwar unguwa da aka yanka filaye. Bayan mallakar filin ne, wani aminina ya ban shawarar, in nemo wani masanin ilimin gine-gine (wato building engineer), ya fitar man da taswirar tsarin ginin da zan yi, dan in gina muhalli mai inganci. Ban yi wasa da wannan shawarar tasa ba, domin muhimmancinta, na nemo wani injiniya, ya fitar man da tsarin ginin (building plan), da zan yi mai inganci, daidai da tattalin arzikina. Bayan ya fitar man ne na ci gaba da bin tsarin da ya fitar, saboda ƙarancin walwalar kuɗi a tattare da ni, da matsalolin da na riƙa fuskanta daga masu gidajen haya, sai ya zama aikin na tafiya a sannu, amma hakan bai dame ni ba sosai, domin na san aikin na tafiya da inganci. Na fara wannan aikin bayan aurena da shekaru biyu, amma sai da aikin ya lashe wasu shekaru uku, sannan ya kai matakin yin rufi. A lokacin da na sayi filin nawa, ba wani gini a wajen, amma a tsakanin waɗannan shekaru, duk kusan filayen da ke rukunin an gine su, sun zama gidaje har mutane sun tare a cikinsu.

 A tsakanin shekaru biyar da na yi da aure, na zauna gidajen haya har guda biyar.

 Gidan farko da na zauna haya, gidan wata mace ce mai mita da yawan binbini. Takurawarta ta kai maƙura, ba ma yin cikakken wata sai ta zo gidan, ta yi ta dube-duben bangwaye da daɓen gidan, wai ta ga ko za mu kashe mata gida. Amma a haka za ta gama dube-duben ta tafi ba tare da ta samu abun yin ƙorafi a kai ba. Sannan idan ya zamana saura kamar wata biyu, kuɗin hayar da na bayar su ƙare, sai ta turo man dillalinta, wai ya yi man tuni. Da kuma ya rage saura wata ɗaya, sai ta zo da kanta tunasar da ni lokacin biyan kuɗi fa ya matso. Duk da cewa tun a farkon kama gidan, sai da aka sanya wannan sharaɗin, a cikin takardar yarjejeniyar kama gidan, cewar da lokaci ya yi zan biya kuɗi, ba ta son jinkiri, wai ba ta son a yi mata wasa da biyan kuɗi. Na kuma amince a hakan, sai dai ga alamu hakan bai gamsar da ita ba, dole sai ta yi tunasarwar take samun gamsuwa. Ga gidan ba wani wadatacce ba, ɗakuna biyu ne kacal sai dan ƙaramin madafar abinci (kitching), da kewaye (bayi), babu wadatar filin tsakar gida, amma a haka muke zaune cikin haƙuri, tun da ba mu da shi, idan ma mun ce mu tashi mu canza wani, ba mu san shi kuma wace irn matsalar za mu tarar a can ba, saboda masu hikimar zance sun ce, “Sanin hali kan sa a ci maganin zama da mutum.” Sai mu ka ci maganin zama da ita.

 Bayan na cika shekaru biyu a gidan, zan sake biyan kuɗin shekara ta uku, aka samu akasin da ya jawo tashina daga gidan. Nakuda ce ta taso wa matata abun ya zo da tangarɗar da har sai da aka kwantar da ita asibiti, aka yi mata aiki aka fiddo jaririn, shi ma kuma ya zo da matsalar da sai da aka kwantar da su. Duk ‘yan kuɗin da na tanada domin wannan haihuwar sai da suka ƙare, ƙarshe dole ta sa na taɓa kuɗin hayar da zan bayar, domin ceto lafiyar iyalaina, wacce a lokacin ta fiye man komai. Bayan iyalina sun shafe kwanaki tara a asibiti, aka sallamo su, ‘yan kuɗin da suka rage man, da gudummuwoyin da na samu daga ‘yan uwa da abokan arzuƙa, na harhaɗa na sawo ragon suna, aka yi sunan yaron. Bayan mako wa’adin biyan kuɗi ya yi, ban bayar ba saboda ban da su.

 Da yammacin ranar sai ga Sadi, dillalin Hajiya ya zo karɓar kuɗin haya, na faɗa masa ya gaya wa Hajiya dan Allah ta yi haƙuri zan kawo mata, ta ɗan ƙara man lokaci, iyalina ce ta haihu kuma abun ya zo da matsala, sai da aka kwantar da su asibiti, duka yau kwanansu bakwai da sallamowa. Washegari misalin shida da rabi na ji ana bugo man gida kamar za a ɓalle ƙyauren, cikin firgici na je, na ce, “kai! Wai waye ke bugo mana gida da ƙarfi haka da sassafe?” Sai na ji an ce, “Ka buɗe mai gidan ce!”

 Ina jin muryar nasan Hajiya ce mai gidan, zuciyata a kiɗime na buɗe gidan, na ce, “Hajiya ke ce da sassafe haka?” Ta bi ni da harara rai a ɓace, na basar na ce Hajiya ki shigo mana, ina kwa... Ban ƙarasa ba ta ɗaga man hannu.

 Ta ce, “dakata ba gaisuwarka ta munafunci ni ke so ba! Da ban kwana ba za ka ganni ne? Ni maganar kuɗin haya ta kawoni, ka ba ni kawai in juya.”

 Na ce, “Hajiya ki yi haƙuri ai jiya da malam Sadi dillali ya zo, na yi masa bayanin matsalar da ta same ni, bai faɗa maki ba ne?”

 Cikin faɗa ta ce, “Ya faɗa man, amma ai wannan matsalarka ce, ina ruwana da ita!”

 Na ce duk da nasan matsalata ce ba taki ba, amma dai dan Allah Hajiya, ki yi haƙuri ki ƙara man lokaci, zan kawo maki. Tun da muke tsawon shekaru biyu, kin sani ba ki taɓa samun matsala da ni ba, wajen kula da gidanki, ko biyan kuɗi”

 Sai ta yi tsaki ta ce,“To na ji yaushe za ka hado man kudina?”

 Na ce ki ban watanni biyu, insha Allahu zan kawo maki zuwa lokacin.

 Ta ce, “Tun da da dukiyar tsohonka na gina gidan ba? Na baka mako ɗaya in ya cika baka haɗo man kuɗina ba, to ka tattara kayanka ka bar man gida, in ba haka ba ko da hukuma zan haɗa ka, ka ji na gaya maka!”

 Sai ta juya ta tafi ba ko bankwana, na yi tsaye ya yin da na bi ta da kallo. Na dawo cikin gida jikina a sanyaye, matata da ke tsaye a tsakar gida tana jin duk sababin da Hajiyar ke yi, ta bi ni da kallo idanunta cike da ƙwalla.

 Duk wunin ranar haka muka zamo ba wani cikakken kuzari a tattare da mu, saboda damuwar wulaƙancin da Hajiya ta yi mana, da abun da zai faru a gaba. A cikin tsawon makon da Hajiya ta ɗibar man, na kunkunga da ƙyar na samu na haɗa rabin kuɗin. A tunanina idan na bata za ta haƙura, kafin in ida haɗo cikon, amma ina fafur ta ƙi yarda, daga ƙarshe ta ce ta ban wata ɗaya na bar mata gidanta.

 Kafin wa’adin da ta ba mu ya cika, na samu wani gidan. Tsohuwa ce ke da gidan, kuma zaune take a ciki. Bayan mun tare, muna murna mun samu gidan dattijuwar kirki, ashe abun ba haka ba ne, farfar ɗin na baƙunta ne. Watanmu biyu a gidan, halayenta suka bayyana gare mu. Haka kawai sai ta ce wai matata ta gyara mata ɗaki, kuma duk wasu aiyukanta, sai ta ce ita za ta yi mata, wani lokacin ma sai ta ce wai ta ɗauko abayarta za ta aike ta, ta sayo wa dabbobinta abinci. Kai tsurfa kala-kala! Tun muna bata uzuri da martaba tsufanta, har muka fara gajiya.

 Wata rana sai ta same ni ta ce wai matata ba ta yi mata biyayya, ba ta gaida ta, kuma in ta sanya ta aiki, ba ta yi sai ta ga dama. Na ce ta yi haƙuri akwai ajizanci na ɗan adam, amma zan mata magana za ta gyara. Kai in taƙaice maku bayani, al’amuran tsohuwar nan sai ya ƙara ta’azzara, har ta kai ni ƙarshe. Rannan sai ta ce wai ta aiki matata, ta sayo mata goro, amma ta ƙi zuwa.

Na ce mata, “ goggo, ya kamata ki sani Zainab, matar aure ce, ba budurwa ba, kuma zaman aure take yi, ba ‘yar aiki ba ce, ni kaina ban aikenta, duk abun da za a yi ni ke fita in yo. Ya kamata duk abun da ki ke buƙata ki fita ki sayo, ko ki ba yaro ya sayo maki.”

Sai ta ce, “Ikon Allah! Yanzu kai Hamza, ni ka ke gaya wa hakan, duk da alfarmar da na yi maku na baku matsugunni a gidana?”

Na ce, “Goggo ai ba kyauta muke zaune ba, biyan ki muke.”

 Bayan kwana biyu da faruwar hakan, ta ban cikon kuɗina, ta ce na tattara tsiyata na bar mata gidanta.

 Gida na uku da na zauna, duka watana uku a cikinsa na tashi. Shi kuma dalilin tashin nawa, muna zaune ne da mai gidan da iyalinsa. Sai ya kasance idan mun je masallaci da asuba mun dawo, nakan zauna yin lazimi ƙofar gida, kuma sun san hakan, amma da sun zo sai su rufe ƙofar da makulli, dole sai dai na zauna a ƙofar gidan har lokacin da suka buɗe, ko kuma in ta bugawa har na tsawon lokaci, saboda ba su ba mu mabuɗi ba. A haka muke zaman haƙuri.

 Wata rana iyalina, ta je unguwa, bayan tafiyarta sai ita ma matar mai gidan ta tafi unguwa, ta bar wa ɗansu makulli, shi kuma sai ya kulle gidan ya yi tafiyarsa. Misalin biyar na maraice na dawo sai na iske gidan a kulle, sai na kira shi ta waya, na ce ya zo ya buɗe man gida, sai ya ce ba makulli a hannunsa. Ina nan zaune Ƙofar gida sai ga matata ta dawo, nan muka ci gaba da tsayuwa a Ƙofar gidan, har uwar yaron ta dawo, tana ganin gidan a kulle sai ta kira shi ta waya, yana zuwa ya sa makulli ya buɗe gidan. Wannan abun ya ɓata man rai, sai na samu mai gidan na ce ya kamata a ba mu makulli, saboda abun da ake mana a gidan nan baya dacewa, na gaya masa duk abun da ya faru, amma madadin ya ɗauki mataki, sai kawai ya kawo cikon kuɗina ya ce, in tashi in nemi wani gidan.

 Daga nan na yanke ban ƙara zama gidan haya tare da mai gidan. Na kama wani gida ni kaɗai sai dai yana maƙwabtaka da na mai gidan. Lokacin da za mu koma gidan ne yayan matata ya sai mata injin markaɗe, domin ta samu sana’ar yi. Allah cikin ikonsa da yake unguwar babu injin sai kasuwa ta buɗe mata. Tana samun markaɗe sosai. Haka muka zauna cikin natsuwa, komai na tafiya ba wani tashin hankali, har ma mun fara mantawa da matsalolin da muka baro a baya. Bayan cikar mu wata bakwai a gidan, sai matar mai gidan nan, ta sayo injin markaɗe. Amma saboda an saba da gidana, sai ya zamana ba ta samun niƙan sosai. Sai ta faɗa wa mijinta, ya zo ya same ni ya ce, matarsa ta sayi injin markaɗe, kuma gidana ma akwai injin. Na ce masa, ai ba matsala kowa rabonsa ya ke ci. Sai ya ce a’a, wai matata ta daina tada injinta, ko ta sayar da shi.

 Maganar ta ɓata man rai, in ban da raini, ya zai faɗa man haka? Sai na ba shi amsa da cewa, “ai Alhaji Nura, sai dai matarka ta saida nata, domin ita ce ta sayo daga baya.”

 Ya ce, Haka ma za ka ce?”

 Na ce, “Ƙwarai kuwa.”

 Ya ce, “To shikenan.”

 Daga wannan lokacin, komai ya wuce, muka ci gaba da gaisuwar mutunci. Ashe ni ban sani ba ta ciki na ciki. Da lokacin biyan kuɗin haya ya yi, na kai masa, sai ya ce a’a wai ya ba ni wa’adi in tashi, tun da ina baƙin ciki da ci gaban iyalinsa.

 A haka na sake neman wani gidan hayar na kama. Saboda irin wannan uzurawar ne, ya sa nake aikin ginina ka’in da na’in, ba ƙaƙƙautawa, amma matsalar rashin hatiman nasara, sun ja aikin ya ƙi kammaluwa da wuri. Duk wasu halastattun hanyoyi da zan bi in sanu ƙarin kuɗaɗen shiga, dan aikin ya kammalu ina bi. Lokacin da na ga aikin ya kawo daidai rufi, sai farin cikina ya ƙaru, domin na yanke shawarar da na rufe shi, zan gyara wani ɓangare ne kawai in koma cikinsa, alabashi koda ina ciki ne, sai in kammala sauran abun da ba a ida ba. Murnata ta koma ciki ne, a ranar wata laraba da ba zan manta da ita ba, wacce ita ce ta zamo mabuɗin duk abun da ya faru.

 Al’amarin ya faro ne da misalin sha biyun dare, ya yin da aka haɗa wani hadari mai duhu, haɗe da iska da walkiya, da tsawa mai ƙarfi. Hadarin ya ci gaba da haɗuwa, yana mamaye sararin samaniya, har na tsawon kusan mintuna arba’in, sannan aka kece da ruwa mai ƙarfi, haɗe da iska da tsawa mai rikitarwa. Hausawa na cewa, ruwan dare gamagari.” Tabbas a ranar an shimfiɗa ruwa na tsawon awoyi shida, sai shida da hamsin na safiya aka ɗauke.

 Da ƙarfe bakwai da rabi daidai, wayata ta ɗauki ƙarar alamun shigowar kira. Ina dubawa, sai na ga ashe wani aminina ne malam Haruna, cike da mamakin kiran nashi, da sanyin safiya na ɗaga kiran. Abun da ya faɗa man, ya tada man hankali, ya dugunzuma ni. Ya faɗa man cewa unguwar da nake ginin gidana, labari ya iske shi yanzu cewa ruwan da aka yi, ya rusa gidaje da yawa tare da ambaliya, saboda haka ya kamata na je na ga halin da nawa yake ciki, shi ma ga ya nan zai fito mun haɗu a can. Wata ƙara cikina ya riƙa yi ƙululu!!! Cikin sanyin murya na ce, “Inna lillahi wa inna ilaihi raji’un!” Na ce masa na gode yanzun nan zan tafi. Mai ɗakina da ta miƙe tsaye cikin firgici, ya yin da ta ji ina sallallami, ta kalle ni a tsorace ta ce,

 “Abban Sultan, lafiya me ke faruwa?”

 Na faɗa mata abun da malam Haruna ya sanar da ni.

 Ta ce, “Ya salam, innalillahi wa inna ilaihi raji’un! Allah ya sa mu ji, kuma mu ga alkhairi.”

 Na amsa da amin Ummar Sultan! Na ɗauki makullin babur ɗina, na fita na tada, na nufi unguwar, zuciyata cike da fargabar abun da zan tarar.

*************

 Daga inda nake tsaye daga kan layir da za ta sada ni da gidan nawa, ina iya hango irin yadda ruwan saman da aka kwarara a daren jiya mai tsananin ƙarfi da iska, ya yi wa da dama daga ɗaukacin gidajen layin. Ya yin da a bisa layin ba abin da idonka zai hango maka sai ruwan da ke kwance, wanda ya malalu ko ina.

Zuciyata ta firgice, ya yin da idanuna suka hango man gidan da ke jingine da nawa ta ɓangaren gabas a zube, duk da cewa daga inda nake tsaye ina iya hango fuskar gidana ba abun da ta yi, amma hakan bai sa zuciyata samun natsuwa ba. Sakamakon yadda na ga kusan ɗaukacin gidajen layin, sun samu nasu kason gyaran ruwan. Ganin hakan ya sa zuciyata ta kasa samun yarda, da gamsuwar ba abun da ya samu nawa.

 Ina hangen da dama daga magidantan layin cikin ruwan, suna ta ƙoƙarin tsamo kayayyakin amfaninsu, daga ciki, domin kuɓutar da su daga salwanta. Haƙiƙa a wannan yanayi dole in ka ga yadda suke hanƙoron kuɓutar da kayayyakin nasu, gami da irin halin da gidajensu ke ciki, ka tausaya masu. Tun lokacin da na ɗauko hanya, zuwa ganin halin da nawa gidan yake, babu abun da nake nanatawa sai, INNA LILLAHI WA INNA ILAIHI RAJI’UN. A yanzu ma da nake tsaye, zuciyata cike da saƙe-saƙe, da wasi-wasin rashin sanin takamaiman abin yi, ina ƙara nanata faɗarta.

 Shin tsayawa zan yi, har sai ruwan da ya mamaye layir ya janye, sannan in je in duba, ko kuwa ratsa ruwan kawai zan yi, in dubo halin da gidan yake ciki? A irin yadda zuciyata ke cikin taraddadi, bana jin zan iya jiran. Dan haka sai na duƙa, na naɗe ƙafafun wandona yadda zan ji daɗin ratsa ruwan, to a daidai lokacin ne, na ji an dafa kafaɗata ta baya.

A hankali na miƙe, tare da juyawa dan ganin wanda ya dafa ni, take na yi tozali da aminina malam Haruna, wanda ya kira ni ta waya ya sanar da ni abun da ke faruwa.

 Malam Haruna, barka da zuwa na ce, “Ka ga yadda ruwa ya maida layin ko?”

 Ya ce, “E malam Hamza, na gani wannan abu dai ba abun da za mu ce, sai Innalillahi wa inna ilaihi raji’un.”

 Na ce, “Gaskiya ne malam, muna fatan Allah ya sauƙaƙa mana al’amarin.

 Ya ce, “Amin, malam”. Muka yi shiru jim, na ɗan lokaci. Sannan ya ce, “na ga gidan naka ma ga alamu ba abin da ya yi?”

 Na ce, “E to ba na ce ba, don ban kai ga dubawa ba, ina shirin ratsa ruwan dan zuwa in dubo kenan, sai ga ka.

 Ya ce, “To, ai sai mu je mu duba tare.”

 Ya duƙa ya tattare ƙafafun wandonsa. Muka ratsa ruwan, muka doshi gidan, a lokacin da bugun zuciyata ke ƙaruwa. Na sa makulli na buɗe gidan, muka shiga, da dama daga magidantan da ke hanƙoron tsamo kayansu, daga cikin ruwan, suka bi mu da kallo. Sai dai a wannan lokacin, bana cikin yanayin tsayawa yin gaishe-gaishe da jaje, ba tare da na san halin da nawa gidan ke ciki ba.

 Innalillahi wa inna ilaihi raji’un! Abin da muka samu kawunanmu, muna faɗa kenan, a lokacin da muka ga abun da ya faru a cikin gidan. Bangon katangar gidan maƙwabcina ne, ya faɗo kan ginin ɗakunan gidan, wanda hakan ya yi sanadiyar zubowar ɓangarori da dama na ɗakunan, tare da karya lintarsu. Kasantuwar wannan taɓuwa da lintar ta yi, ya yi sanadin tsagewar bangon arewa na gidan. Ganin wannan abu, ya sa na ji kamar kafafuna, ba za su iya ɗauka ta ba, dan haka, sai na jingi na da bango, ya yin da zuciyata ke cikin hargitsi da ɗimuwa, saboda babu wani magidanci, dake hanƙoran gina muhallin da yake fatan tarewa a cikinsa, kuma ya gan shi cikin irin wannan yanayi, ba tare da ya gigita ba, musamman ma ga irina mai ƙaramin ƙarfi, da na shafe tsawon lokaci ina aikin. Tabbas wannan shi ne, ‘Ta leƙo ta koma.’ Ko kuma in ce, ‘Murna ta koma ciki.’ Haka dai muka duba sauran sassan gidan, bayan mun gama, na ƙiyasta a ƙalla gyaran wannan aikin, zai iya lashe kimanin naira dubu ɗari uku, dan mayar da shi yadda yake.

 Bayan mun fito na ce, “To ni yanzu ina zan samu kuɗin da zan gyara gidan nan, cikin ƙanƙanin lokaci? Saboda barin sa cikin wannan yanayin, na tsawon lokaci, zai iya jawo ƙarin wata matsalar, da ta fi wannan.”

 Malam Haruna, ya ce, Malam Hamza, gyaran wannan matsalar kaɗai, ba ita ce mafita ba.

 Na ce, “Malam, me kake nufi da wannan maganar?”

Ya ce, “In ka lura matsalar da wannan layin yake ciki, har da ta rashin fitar da ingantattun hanyoyin ruwa, za ka lura da hakan, in kai la’akari da yadda ruwan ke kwance a kan layir, hakan kuma alama ce, me nuna ruwan bai da wadatacciyar hanyar wucewa.”

Na ce, “Gaskiya ne, to yanzu me ye abun yi?”

Ya ce, “Ina da shawara.”

Na ce, ina sauraren ka malam.

Ya ce, “Me zai hana ku nemi bashin gyaran gida, da bankin bada lamuni na Federal Mortgage Bank.”

Na kalle shi cike da mamaki, na ce, “Daman suna ba da bashin gyaran gidaje ne ga ma’aikata, na yi tunanin bashin gidaje kawai suke bayarwa?”

Ya ce, “Ina, ai suna ba da tun daga naira dubu ɗari biyar, har zuwa miliyan ɗaya, ga duk ma’aikacin da ya nemi hakan.”

 Wata doguwar ajiyar zuciya na yi, tare da jin wani daddaɗan sanyi ya ratsa zuciyata. Sai na samu kaina ina mai cewa, ‘Alhamdulillah’ Na ce, “to malam, ya ake neman wannan bashin?”

 Ya ce, “Yanzu kuwa zan baka bayanin, duk yadda tsare-tsarensu yake.”

 Na ce, To, ina saurarenka.”

Ya ce, “Kamar yadda yake a bisa tsari, bankin lamuni na Federal Mortgage Bank, yana bayar da lamuni kan abun da ya shafi muhalli har kusan kalla huɗu, akwai, tsarin bayar da gidajen kai tsaye bashi, wato (home loan), akwai kuma tsarin da za a baka gidan matsayin haya, kuma ka mallake shi wato (rent to own), akwai kuma tsarin bayar da bashin lamuni kuɗin gina gida da kanka, wato (home construction loan), sai kuma akwai tsarin bayar da lamunin gyaran gida wato (home renovetion loan), kuma wannan tsarin shi ne ya kamata ka ɗauka, domin ka samu isassun kuɗin gyarawa da kammala gidanka.”

 Na ce to malam ya ake bin shi wannan tsarin har a samu kuɗin?

 Ya ce, “ Da farko dai za ka fara zuwa a buɗe maka asusun da zai tabbatar da kana ba da kason kuɗinka duk wata, idan an buɗe za a baka ɗan littafi, wanda ke ɗauke da sunanka, da hotonka, da ma’aikatarka, da ɓangaren da ka ke, da lambarka ta NHF, wacce take da matuƙar muhimmanci wajen amsar lamunin, domin dole ne sai kana da ita. To idan ka samu wannan littafin, sai ka nemi takardar neman bashin (form) a bankin. Idan ka samu, sai ka bi duk ƙa’idojin da aka sharɗanta, ka cike, ka mayar. Daga nan sai ka jira, idan an bi an tabbatar da ka cike kowace ƙa’ida, kuma abun da ka buƙata bai zarce idan an kasa shi watanni sittin (60), a ɗauki kashi ɗaya cikin uku na albashinka ba, idan kuma ya zarta, za su rage su baka abun da ya yi daidai da abun da ke shigo maka a wata. In kuma aka samu wata matsala kamar, ba ka cike wasu ƙa’idojin yanda ake buƙata ba, ko mutum biyun da suka tsaya maka (guarantors), akwai wanda zai aje aiki, ƙasa da shekaru biyar da za ka biya bashin, ko kuma matsayin albashinsa bai kai ya tsaya wa wanda ya buƙaci adadin kuɗin da ka nema ba, za a kira ka, ka gyara. A ƙarƙashin wannan tsarin, za a ba ka daga naira dubu ɗari biyar, har zuwa miliyan na gyaran gida. Sannan za ka biya su ne cikin shekaru biyar, ko abun da ya rage daga shekarun aikinka. Da zarar ka cike komai kan ƙa’ida, za ka jira zuwa wasu watanni, kafin takardar (offer) amincewar ba ka lamunin ta fito.

Wannan jinkirin yana dangantuwa ne, da matsala ko rashin matsalar da rukuninku ya samu, saboda suna tsara abun ne rukuni-rukuni (Batch), kowanne mutum goma ne da suka buƙaci adadin kuɗi iri ɗaya, to in mutum ɗaya ya samu matsala a rukunin, duka za a maido su har sai ya gyara a mayar. Bayan an baka ofa komai ya ƙare, sai kawai jiran shigowar kuɗin da ka buƙata.”

 Bayan malam Haruana ya gama yi man bayanin tsarin banki ba da lamuni, sai na tambaye shi to ina zan zamu ita takardar da za a buɗe man asusun? Ya faɗa man ai a bankin zan je na amso na cike. Sannan ya ƙara man da shawarar ya kamata in zauna da mutanen layinmu, mu tattauna yadda za mu gyara layin, mu fitar da hanyoyin ruwa, ta yadda ko a gaba ba za mu sake fuskantar matsalar ambaliya ba, bare ta kai ga rushewar gidajenmu. Na yi masa godiya muka yi bankwana.

 Na yi amfani da shawarar aminina malam Haruna, na bi duk ƙa’idoji na buɗe asusuna a federal mortgage bank, na kuma samu fom na bashin gyaran muhalli, na cike na mayar. A lokacin da nake bibiyar yadda zan samu lamunin ne, muka yi zama na musamman da maƙwabtana, muka tatatauna matsalolin da suka haddasa mana wannan ambaliyar, da ta yi sanadiyar jawo mana asara. A ƙarshe muka cimma matsayar haɗa kai, mu fitar da ingantattun hanyoyin ruwa. Mun yarda cewar, matsalolin da wasunmu ke fuskanta a gidajen haya, na matsi da takura ne, ke jawowa muke aikin gaggawa, domin mu tare a namu gidajen, ba tare da la’akari da abun da ka je ya komo ba, wanda hakan ke koma mana dana sani.

*****************

 A ƙarshe mun gyara layinmu, mun fitar da hanyoyin ruwa masu inganci, mun yi ciko, layin ya koma gwanin kyau. Bayan watanni biyar, banki lamuni suka ban kuɗin da na nema, na kammala aikin gidana muka tare cikin farin ciki.

 Ire-iren matsalolin da na fuskanta da waɗanda na ga wasu sun fuskanta, ya sa na yi tunanin bayar da tawa gudummuwar, domin bai kamata abar abun ya ci gaba da faruwa a cikin al’ummarmu ba. Da farko na fara ƙoƙarin yin aikin wayar wa al’umma kai ni ɗaya, sai na fuskanci ba mai saurare na, ballantana ya yi amfani da shawarar da na bayar. Wata rana muna tattauna matsalolin da mai ɗakina, sai ta ban shawarar in samu wasu, masu irin wannan tunani, da kishin nawa, mu kafa ƙungiya, wataƙila hakan zai fi tasiri, idan abun ya fito a ƙungiyance, domin al’umma sun fi girmama hakan, kuma yin komai a ƙungiyancen, zai fi bada damar a cimma manufar da ake fata.

 Na yi amfani da shawararta, na tuntuɓi wasu daga abokaina, da makwabtana, muka tattauna muhimmanci yin hakan, suka amince. Daga nan muka kafa wannan ƙungiyar. Bayan kafuwar ƙungiyar, sai muka duƙufa wajen ganin mun cimma ƙudurorin samar da ita. Muka ci gaba da wayar wa da al’umma kai, a kan muhimmancin mallakar muhalli, tare da gina muhallai masu inganci, da fitar da ingantattun hanyoyin ruwa, da samar da ingantattun hanyoyin zubar da shara, domin kare kai daga ambaliyar ruwa, ko asarar dukiya, da salwantar muhallai. Daga lokaci kuma zuwa lokaci, ƙungiyar tana shirya bita dan ƙara wayar wa da al’umma kai, a kan abun da ya shafi muhallinsu, da irin muhimmancin da muhalli mai inganci yake da shi. Cikin shekaru biyu da kafuwar ƙungiyar, ta mamaye faɗin garin nan, domin a yanzu da nake baku wannan labari, ƙungiyar na da mambobi dubu biyu da ɗari bakwai. Sannan akwai asusu na musamman da ƙungiyar ta buɗe, wanda mu ‘ya’yanta zalla kawai, muke bada gudummuwoyinmu na abun da ya sauwaƙ a, da kuɗin muke amfani wajen sayen kayayyakin aikin gayya, kamar na gyaran kwatoci, da na kwasar shara, da kuma tone wasu magudanan ruwan, da suka toshe na cikin unguwanni. To wannan dai shi ne dalilin da ya ja na kafa wannan ƙungiya da kuma ayyukan da take yi.

 Gaba ɗaya aka ɗauki tafi raf raf raf!!! Bayan malam Hamza ya kammala jawabinsa, sai ya koma ya zauna. Mai gabatarwa ya ce an ce daman waƙa a bakin mai ita tafi daɗi, yanzu mun ji abin da ya yi sanadin samar da ƙungiyar MUHALLINKA ALFARMARKA, daga bakin shugabanta. A yanzu za mu kira babban baƙonmu domin ya fito ya bayar da wannan kambun girmamawar ga wannan ƙungiya. Jama’a suka sake tafawa, a lokacin da baban baƙon, ke miƙa wa malam Hamza kambun ƙarramawar, wanda aka rubuta sunan ƙungiyar da rubutu mai ruwan gwal.

 Bayan kammala bikin ba da kyaututtukan ne, aka rufe taron da addu’a, kowa ya nufi in da ya fito. Wani ɗan jarida ya fara yi wa malam Hamza, tambayoyi;

 Yallaɓai, me za ka ce game da wannan karramawar da aka yi wa ƙungiyarka?

 Ba abun da zan ce sai godiya ga mahallincimu, domin da ikonsa ne da kuma iyawarsa, ƙungiyar ta taka wannan matsayin.

 Ana iya cewa, wannan nasarar ta samu ne bisa ga jajircewarka?

 Wannan nasarar ba tawa ba ce, kuma ba ƙoƙari na ba ne, ta dukkan mambobin ƙungiyar ce, domin da jajircewa da sadaukarwarsu ne, ƙungiyar ta kai inda take a yau.

 A yanzu kana ganin ƙungiyar ta cimma duk wasu ƙudurorin da aka kafata domin su?

 Alhamdulillah! Mun cimma dai kashi tamanin da biyar cikin ɗari.

 To ranka ya daɗe mun gode.

 Nima na gode.

 ƘARSHE

Muhalli, Sutura

Post a Comment

0 Comments