Ticker

6/recent/ticker-posts

Bakin Bunu…

Bashir Adamu (2020). Baƙin Bunu…. Muhalli, Sutura (Labaran Da Suka Samu Nasara a Gasar Gajerun Labarai a Kan Muhalli Ta Arc. Ahmed Musa Dangiwa, 2020). Darma Digital Prints.

BAƘIN BUNU…

Na

Bashir Adamu

15/7/2020 Babbar Kotun Jiha ta Ɗaya

“Duba da shedu da kuma hujojjin da masu ƙara suka gabatar wannan kotu mai daraja ta samu Alhaji Musa wanda aka fi sani da (Kuɗi ƙasa) da laifin da ake zarginsa da aikatawa, saboda haka kotu ta zartar mai da hukuncin ɗaurin shekaru goma a gidan kaso ba tare da zaɓin biyan tara ba, haka kuma…”

Abin da na iya jiyo wa kenan daga bakin alƙalin, sai dai na farka na ganni a gadon asibiti, kusa da ni ga wani jami’in gidan gyaran hali ya ƙura man ido kamar yana tsoron kar na ɓace. A gefe guda kuma lauya na ne tare da Musa abokin aiki na suke tattaunawa, na wurga kallo na ga saitin tagar gadon da nake kwance na hango matata zaune a gindin wata bishiya da ke harabar ɗakin da aka kwantar da ni ta yi tagumi, ƙaramin yarona Sadiƙ na ta faman wasan shi a gefenta.

 Wata ajiyar zuciya na yi, sannan na sake lumshe idona na nutsa a kogin tunanani, wai yau ni ne nan za a zartar wa da hukuncin ɗauri? Wannan kuwa ba mafarki ba ne? Na ƙara buɗe ido na a hankali domin tabbatar da ko dai a mafarki na ke amma duk abubuwan da na gani ɗazu yanzu ma na sake ganinsu a zahiri, lallai ba mafarki ba ne. Zuciyata ta hasko man farkon abin da nake ganin shi ne faruwar matsalar.

 22/1/2019 Da ƙarfe 11:09 na safe

 Ina zaune a ofishina ta shigo cikin sigar rangwaɗa da murmushi a fuskarta tare da yin sallama irin ta wayayyun ‘yan boko waɗanda addini bai ratsa ba, a tsarina ba a shigo wa ofishina kai tsaye, sai mai taimaka man ya sanar da ni, amma na yi mamakin ganin ta haka, ba tare da sanar da ni ba. Na ɗago a hankali na kalleta ban amsa mata sallamar ba, sai dai kawai na ga hannuna na nuni gare ta da ta zauna.

‘Sunana Fatima amma an fi sanina da P.A sakamakon na taba zama P.A ta tsohon kakakin majalissar dokoki ta ƙasar nan, yanzu kuma ina aiki da ma’aikatar walwala da jin daɗin jama’a ta ƙasa a matsayin sakatariyar kuɗi, na zo nan ne domin ka yi man hanya in karɓi bashin bankinku na gina gidaje, ina da kuɗin da zan iya gina gida amma ina so ne na moru da wannan banki naku, sannan kuma ba haka kawai za ka yi aikin ba, kai ma zaka samu rabonka a ciki. Nasan wata ƙila kayi mamaki ta ina? Da farko ina son ka san cewa na san cewa kai ba zaka moru gida ba ko kuɗin gyaran gida daga bankinku, duba da cewa kai ma’aikacin bankin ne, wanda dokar da ta samar da bankin ta haramta maku haka.

Sannan kuma ni yanzu ina da sauran shekaru goma sha biyar a aiki ka ga zan iya biyan kuɗin musamman saboda shekaru biyar ne dama mafi ƙarancin wa’adin, sannan kuma na san cewa ba a bayar da ko sisi kafin a ba mutum wannan lamuni illa iyaka dai ana buƙatar ya zuba kuɗi a asusun sa na tsarin samar da gidaje na ƙasa a ƙalla watanni shida, wanda ni duk na cika wannan sharuɗɗa, amma kuma ni zan biya ka kuɗi ƙasa ne kamar yadda ake kiranka in dai har ka yi man hanyar samun gida a inda zan faɗa maka.’’

Hannu na ɗaga mata alamar ta tsaya, rigarta ta gyara ƙirjinta ya ɗan fito fili ta duƙo gaf da ni ta ce, ‘‘ka sauraran ban gama ba’’ ƙamshin turarenta ya daki hancina, na ji wani juyi a kaina tamkar ba a duniyar nake ba, ban san sadda na fara jin shauƙin ta ba, kamar maganaɗisu ta ɗauke magana ta na yi tsit ina kallonta.

‘‘Na san cewa, bankinku ya fito da tsarin bayar da miliyan ɗaya ne matsayin kuɗin gyaran gida domin bai wa ma’aikata da dama damar amfanuwa da bankin naku, domin ba kowa ne ke iya samun gida ba daga gareku, kuma kai ne babban darakatan da ke kula da wannan ɓangare na raba bashin miliyan ɗayan. Na ga haka ne bayan da na ziyarci shafinku, inda na ga an jero sunayen daraktocinku da ma sauran ma’aikatanku, ganin sunanka kawai ya sa na aminta da cewa zaka iya yi man aikin da nake buƙata, duba da cewa kafin ka dawo wannan bankin mun taɓa yin wata harƙala da kai a lokacin kana aiki a hukumar sifiyo ta jiharku”.

Na ƙura mata ido ina so in tuno harƙalar da muka taɓa yi da ita, amma na kasa, murmushi kawai ta yi ta duban ta ce, ‘‘kar ka wahalar da kan ka tuno harƙalar zuwa gaba zan bayyana maka, amma ganin fuskata ba zai sa ka tuna ba, kuma ba wannan maganar muke ba.’’

Kai tsaye na tambaye ta me kike so wai yanzu? sai faman jawabi kike kamar ke ce babban darakatan wannan bankin, musamman yada kike zayyano wasu dokoki da ƙa’idoji da suka shafi bankin.

‘‘So nake a ba ni gida ɗaya mai ɗaki uku a rukunin gidaje na unguwar Samba da kuka gina a nan birnin Tarayya’’

Na kalleta a zuciyata na ce, anya wannan ba taɓaɓɓa ba ce?

‘‘Da hankali na ras, nasan tunanin da kake ila na haukace ko? To da hankalina zan maka bayanin yadda tsarin zai kasance kai kawai bi za ka yi”

Na rangwanta mata ne kawai saboda na ji ta ambaci aikin da na yi a hukumar Sifiyo wanda kuma ina da wani ɓoyayyen sirri da ba ni so ya fito, amma sai wata dabara ta faɗo man...

“Har yanzu bai tashi ba ne” wani ɗan siririn likita ne ya katse man tunanina da muryarsa mai kama da an busa usur ɗin filin kwallo. Na buɗe ido na a hanlkali ina kalon mutanen wajen ɗaya bayan ɗaya, na yunqura da niyyar tashi sai na ji hannuna ɗaya ɗaure gam da ankwa, ban san sadda na koma na kwanta ba, a daidai lokacin da likitan ya yunƙuro yana ƙoƙarin mayar da ni kar na tashi.

Haka na koma na kwanta ina bin duk wanda ke wajen da kallo ɗaya bayan ɗaya, kamar wani wanda ya ɓata. Likitan ya dube ni cikin natsuwa ya ce, “Sannu Alhaji, ai jikin naka ma da sauƙi, amma ka rage sanya abubuwa a zuciyarka, domin kana iya samun bugun zuciya, kaga kuma hakan ba zai haifar ma da ɗa mai ido ba”.

Ban ce masa kome ba sai saƙe-saƙe nake a zuciyata, haka na hango Musa tare da lauyana sun nufo inda nike kai tsaye da alamar suma jira suke na tashi dama, na yi kamar na sake runtse ido na amma sai naga na yi ido huɗu da matata wadda ita ma ta lura da tashi na shi ya sa ta nufo inda nake, na kawar da kai na daga kallonta cikin jin kunya da nadama, ko shakka babu matata tasha nusar da ni kan abinda zai iya faruwa da ni musamman in ta ji irin wayar da nike a gida dangane da wasu harƙaloli da nake ƙullawa, amma daidai da rana ɗaya ban taɓa nuna mata cewar abinda take faɗa man yana shiga raina ba, asali ma ina mata kallon wata wadda ta zama matsala a rayuwata saboda tsabagen sanya idonta ga harkoki na.

Mun kwashi shekaru kusan ashirin da ita, amma kullum bata taɓa gajiyawa ba wajen nuna man soyayya da ƙauna, ni kuma in ban da tsana babu abinda ke ƙaruwa nata a zuciyata, sau da yawa nasha yin tunanin ko dai hannu aka sa man na tsanarta ne, duk wani abu da zata yi bai burgeni, duk ƙoƙarinta na kyautata man ban gani, ni dai kawai barni da na fita waje na riƙa waya ta hirar waya da mata a waje, duk yadda mace take a waje in tayi man magana zan bata kulawa ta musamman, amma a gida kuwa da zaran na shiga zan murtuke fuska, abu kaɗan za a yi man na fara bambami da hayaniya... “baban Sadiƙ sannu da jiki” muryar matata ce ta ratsa kunnena cikin bazata, a karon farko tun bayan satin amaracinmu da na ji muryarta ta ta yi daɗi kamar busar sarewa, ban iya amsawa ba sai dai ƙura mata ido da na yi cikin nadama da kuma jimami.

Ko kafin na ce wani abu, Musa abokin aiki na ya fara magana, “sannu Master (sunan da yake kirana da shi ke nan saboda ƙwarewata wajen iya tsara abubuwa), kar ka damu mun gama magana da Lauya yanzu zamu ɗaukaka ƙara, saboda wannan hukunci ba mu aminta da shi ba, kuma muna ganin akwai lauje cikin naxi”. Lauyana Aliyu ya kalle ni yace, “Alhaji kasan duk abinda ya kamata ace mun yi kan wannan kes ɗin mun yi shi, amma aka samu akasi, to wannan ba zai hana mu samu nasara a kotun ɗaukaka ƙara ba, mun gama kome game da shirin mu na ɗaukaka ƙara, saboda haka kar ka damu”.

Ba abinda na iya sai gyaɗa kai ba tare da na ce kome ba, idanuna rumtse saboda ina matuƙar jin kunyar in buɗe su mu yi ido huɗu da matata.

Bayan tafiyar su Musa da Lauyana, sai likita ya bayar da umurnin a sallame ni saboda ba wata damuwa a tare da ni, ban samu na yi wata doguwar magana da matata ba, saboda ba na iya haɗa ido da ita a daidai wannan lokaci da ko a safiyar ranar kafin a yanke man hukunci sai da muka yi faɗa kan in gyara ɗabi’una duba da cewa shekaru na sun fara tafiya.

Jami’in gidan gyaran halin da ke tsare da ni ya buga waya ya buƙaci da aka kawo mota domin tafiya da ni inda za a tsare ni kafin takardun ɗaukaka ƙara ta su samu amincewa. Cikin mintina da ba su fi goma ba sai ga mota ta zo aka kwance sarkar da aka ɗaure ni da ita na miƙe tsaye cikin girmamawa jami’in gidan yarin ya kama hannuna kamar abokinsa muka fita daga ɗakin da aka kwantar dani zuwa wajen motar da za ta tafi da ni. Matata na gani a kofar ɗakin tsaye tana kallona hawaye na zuba daga idonta, ban tsaya wajenta ba kawai muka nufi cikin motar kaina sadde a ƙasa. Mota ce ƙarama mai ƙirar shiga ba biya, aka buɗe man gidan baya na shiga na zauna aka mayar aka rufe da kwaɗɗo, na buga tagumi na faɗa cikin tunanin halin da na shiga.

*****

Maganganun Fatima P.A suka riƙa dawo man kamar sabbi.... “ kawai abin da nake buƙata ka aminta da ba ni gidan saboda nasan zaka iya, kuma ma ai na cika sharuɗɗa, sannan zan zuba adadin kuɗin da aka ƙayyade ga mai buƙatar gidan ya zuba, sai dai fa da ka ji na ambaci gida mai ɗaki uku, kar kayi mamaki domin nayi bincike shi kaɗai ne ya rage kuma yana nan kusa da wani makeken fili da aka ware an ce wai kasuwa za a yi wajen da asibiti, to buƙatata a wannan filin take, domin in aka ba ni gidan sai a ƙara shata man daga cikin filin da kuka ce an ware domin yin asibiti da shaguna, duba da cewa gidan liƙe yake da filin a wajen rubutawa nake son a ƙara man haka zan biya ko nawa ne kan wannan aikin”.

Cikin mamaki na ɗaga kaina na kalleta ina al’ajabin wannan abu nata ko shakka babu wannan turo ta aka yi domin ba wanda ya san da wannan gidan sai wasu tsirarun daga ma’aikatan kuma an ware wannan gida shi kaɗai ba a ba da shi ba saboda wannan filin dama, suna kasafta yadda zasu samu wani kaso a cikin filin domin samun kuɗaɗen kashe ƙwalama, kamar yadda suke kiran irin waɗannan kuɗaɗen... “kar ka wahalar da kanka wajen tunanin ya aka yi na san da fili ko kuma manufa ta tayin haka” muryarta ce ta katse ni daga tunanin da na fara, taci gaba da cewa,

 “kamar yadda na faɗa ma a baya ban zo wajenka ba sai da nasan waye kai, lokacin da kana shugaba a hukumar Sifiyo ta jihar ku, na san ka yi abinda ya fi wannan kuma ka wanye lafiya saboda ƙwarewarka da kuma sakin hannunka ga jama’a musamman abokan aiki". lokacin da kana Shugaba a hukumar Sifiyo ta jihar ku, nasan kayi abin da yafi wannan kuma ka wanye lafiya saboda ƙwarewarka da kuma sakin hannunka ga jama’a musamman abokan aiki".

Lokacin da ta tsaya da maganarta ta ƙura man ido kamar tana hangen wani abu a cikin ido na, nima kuma sai na cigaba da kallonta ƙur naƙi ɗauke ido na daga kanta har zuwa wasu ‘yan daƙiƙu, sannan na fara tunanin irin harƙalla da muka yi lokacin ina shugaban hukumar Sifiyo ta jiha, ko shakka babu duk arziƙin da na samu a rayuwa a wannan hukumar na same shi.

Duk da cewa a yanzu idan naje jihar tawa ta haihuwa ina ganin abubuwa da yawa da suka kasance mu ne sanadin faruwarsu, kama daga cinkoson da ake fama da shi a wasu titunan jihar, wanda hakan na da nasaba da yanka duk wani fili da ke bakin hanya ko kuma ya shafi makarantu ko wasu wurare na gwamnati duk mun samu haɗin kan gwamna mun yanka su tare da sayar da su ko ince ba da wa ga manyan muƙarabban gwamnati, wanda yanzu nike ganin illar abun, domin akwai hanyoyin da saboda wannan mugun aiki da muka yi ba zasu faɗaɗu ba.

Ba ma wannan ya fi damuna ba illa yadda muka yanka tare da bayar da duk wasu filaye dake cikin rukunin gidajen da ba gwamnatin da na yi aiki a ƙarƙashinta ta samar da su ba, sakamakon haka, aka rasa filayen asibiti da masallaci da maƙabarta da ma kasuwa a rukunin gidajen, sai an yi tafiyayya sannan aje, kuma abun ƙaddara nima a ɗaya daga cikin waɗannan unguwanni da muka yi wa cin kashi nake da zama.

“kai nake sauraro, ka faɗa man yadda za a yi, kawai me zan bayar bayan kuɗin da zan ajiye na mallakar gidan?” ki je sai gobe ki dawo zan tattauna da waɗanda ke da hannun a wannan gida ɗayan da ya rage, in Allah ya yarda za a san yadda za a yi. Mayar mata da magana kai tsaye ba tare da na ƙara ɗaga kai na kalleta ba.

Bata ƙara cewa kome ba sai dai miƙewa ta yi, ta kallan cikin natsuwa tare da yi man wani murmushi, sanna ta ɗaga ‘yan yatsun hannunta na dama ta kaɗa su alamar bankwana, na bita da kallo kamar wanda aka aikowa da saƙon mutuwa, tana fita daga ofis ɗin na yi wata aciyar zuciya.....

*******

Alamar buɗewar kyauran motar da nake ciki ya tabbatar man da cewa an zo gidan gyaran halin da za a ajiye ni, hankali na ya dawo jikina baki ɗaya, jami’in da ya tsare ni a asibiti ne ya buɗe ƙofar tare da cewa, Alhaji bisimillah fito an zo, ai ta dai haƙuri da rayuwa, kowane ɗan Adam bai wuce ƙaddararsa mu je kanta a yi maka rijista”.

Haka na fito kamar ƙafafuwana ba za su iya ɗauka ta ba na bi bayan wannan jami’i muka shiga cikin gidan, kai tsaye muka nufi wani ofishi, wanda a saman ofishin naga an rubuta “Chief Worder” muka shiga ciki jami’in ya miƙa wa wanda ke zaune a ofishin bayan ya duba takardar sai ya bani umurnin da in zauna, ya fara magan da cewa, “Alhaji kamar yadda yake dokar gidana nan duk wanda aka kawo kafin mu ba shi inda zai zauna sai ya faɗi mana laifin da ya yi aka kawo shi a gidan nan..”

Na ɗago kai na na kalle shi na bayyana masa cewa, yau da gobe ce ta kawo ni wannan gida naku ba wai dan ina so ba, na lura cewa amsar da na bashi bata gamsar da shi ba, amma sai ya kyale kawai, ban kuma san dalilin sa na yin hakan ba.

Wani jami’in ya kira ya ce masa a je a ba ni kaya da ɗaki, na bi bayan jami’in ina kallon taswirar cikin gida, mutane na hanga cinkushe a cikin wasu dogayen ɗakuna da na ga an nufi da ni gabana ya faɗi, na ji ciwon zuciyata ya ƙara tasowa, saboda irin cinkushewar da ya yi. Kallon da wanda nake bi ya yi man na san cewa ya farga da halin da nake ciki. “Alhaji ai wannan kaɗan ma ka gani akwai ɗakin da a gidan nan asali an yi shi saboda mutum ashirin ne, amma yanzu akwai sama da mutane ɗari da goma a cikinsa, ai matsalar muhalin nan ba wai a gidajen cikin gari kawai ta tsaya ba, har a nan ma ya kamata irin hukumominku su kawo ɗauki domin faɗaɗa yanayin zaman da ake a nan, duba da cewa nan ɗin ma mutane ne ke zaune a ciki, kuma ita ƙaddara tana iya kawo kowa nan kamar yadda ta kawo ka”

Na kalle shi kamar zan yi kuka na ce masa yanzu nima a cikinsu za a ajiyeni? “ƙwarai kuwa, amma kai ɗakin da za a kai ka ba za ku wuce ku saba’in ba, amma kuma in kana son a kai ka VIP to sai ka yi wani abu” cikin sauri na ce masa ko nawa ne zan bada a kaini VIP ɗin. Ya yi murmushi yace, “ok biyoni muje na kai ka sai na koma na sanar wa da oga, saboda shi za a ba kuɗin da za ka ba da ɗin”.

Ɗakin da aka kira VIP, za a iya cewa mai kyau ne domin dai fallan ɗaya ne wanda bai wuce girman ƙaramin falo ba, akwai gado biyu masu hawa biyu a cikinsa sannan akwai wani koɗaɗɗen kafet shimfiɗe a tsakiyar ɗakin, kuma akwai kewaye a cikin ɗakin, shi dama an ware shi ne musamman saboda manyan jami’an gwamnati ko kuma waɗanda rikicin siya sa ya kawo gidan, a ɗakin na tarar da wani mutum ɗaya wanda na san shi dama tun a cikin gari, shi ma dai kamar ni wata harƙallar ce ta kawo sa a nan, amma shi ba a ma yanke masa hukunci ba.

Na zauna gefen gadon da aka ba ni na kalli zubin gadon, rabon da na kwanta irin wannan gadon tun lokacin da na yi makarantar kwana, kusan shekaru talatin da biyar da suka shuɗe, hawaye na ji na neman zubo man, amma dole na daure kar su zubo, na ƙara matsawa bisa gadon na jingina da bango zuciyata na hasaso man baya, kan abubuwan da suka faru har na samu kaina a wannan gida.

Na ƙara matsawa bisa gadon na jingina da bangon ina tunanin abubuwa kamar yanzu suke faruwa, na tuna lokacin da shugaba jam’iyya ya kirani yake mai sanar da ni cewa, sun yi magana da gwamna yana so a ba shi wani fili da ke cikin rukunin gidajen Sulluɓawa zai gina gida, ko shakka babu wannan shi ne ɗan mabuɗin duk wata matsala na faɗa.

Na tuna da lokacin da na je gidan sa kai masa taswirar filayen da ke cikin rukunin gidajen, na same shi zaune a falonsa yana kallon labaran ƙasa. Bayan mun gaisa na fara gabatar masa da sauran filayen da suka rage kamar haka; Ranka ya daɗe wannan filin shi ne mafi girma an ware shi ne saboda a gina Islamiyya da shaguna nan gaba, wannan kuma an ware shi ne domin gina asibiti da kuma kasuwa, sai mita hamsin da ta zagaya gidajen baki ɗaya shi kuma an ware shi ne saboda samun filayen wasanni ga yara da kuma shuka ciyawa tare da taimakawa wajen samun iska da yanayi mai kyau, sai kuma sauran filaye da aka rage saboda abubuwan daka iya tasowa nan gaba, kamar dai yadda dokar tsara birane ta tanadar.

Bai ce kome ba sai da na gama sannan ya fara magana da cewa, “Ni yanzu wannan filin da ka ce an ware saboda a gina Islamiyya shi za ka yanka man kuma ka kawo man takardunsa, mun yi magana da sakataren gwamnati da shugaban ma’aikata na gidan gwamnati duk su ma suna son filaye, sannan gwamna ya yi wa ‘yan jarida alƙawarin filaye kuma ya ce na sanar da kai su ma duk a nan za a yankan masu, saboda haka kai kasan yadda zaka yanka filayen kowa ya samu kuma kai ma ka fitar da kason ka.”

Ban tsaya yin musu ba ko gardama na aminta da maganar sa nace gobe in sha Allah zamu zo da ma’aikatanmu a fara yanka filayen takardun filinka kuma zan kawo su gobe in sah Allah.

Tun bayan fitowa ta daga gidan shugaban jam’iyya na fara tsare-tsaren yadda zan samu filaye masu yawa a wannan aikin da za a yi.

Wanshekare muka fita da ma’aikatana muka fara aikin yanka duk wani fili da ya rage a cikin rukunin gidajen Sulluɓawa, a wannan aiki sai da na samu filaye takwas masu kyau bayan kuɗaɗen da na samu na alheri daga shugaban jam’iyya da sauran muƙarabban gwamnatin da aka yanka wa filaye a wajen.

Sai dai ni kaina na san cewa fasalin unguwar ya sauya domin an matse unguwar sosai za a yi gine-gine har wuraren da ba su da ce ba, kuma nasan cewa yanka waɗanann filayen zai kawo wa unguwar matsalar ruwa sosai, domin akwai wuraren da aka ware domin gina manyan rijiyoyi da za su ba unguwar ruwa, duk mun yanke su yanzu sun zama gida.

Haka kuma, babu wani fili da za a iya gina Islamiyya ko Caji ofis ko wasu abubuwa da ka iya taso a unguwa mai gidaje ɗari biyar yanzu kuma na samar da filaye sama da ɗari biyu. Amma ba filin da za a gina shaguna ko kasuwa ko asibiti, sai dai an fita nesa domin samo waɗannan abubuwa, wanda hakan ko shakka babu zai iya haddasa asarar dukiya da rayuka a nan gaba. Ni dai ba wannan ke gabana ba kawai ina duba abin da na samu ne a wannan huɗɗar....

“ƙarar buɗe ɗakin da muke ciki ne ta dawo da ni daga dogon tunanin da na nausa, wani ɗan tsukakken mutum ne ya buɗe ɗakin tare da tsaya wa a ƙofar ɗakin yana kallonmu. Ina Alhaji Musa ka zo ana son ganika kana da baƙi”, kamar na ce ba zan fita ba saboda gajiyar da ke tare da ni kuma duka fa ban wuce awa ɗaya ba da kawowa ba, na ɗaga kaina na kalle shi ba tare da na ce kome ba kawai na tashi na nufi kofar ɗakin, gaba ya sani har muka isa dan tsukaken ɗaki wanda ke da benji ɗaya a tsakiya sa. Taye take a tsakiyar ɗakin ta rungume hannu, kallo ɗaya na yi mata na gane ta Fatima P.A ce.

Cikin zuciya ta na fara tunanin me kuma ya kawo wannan matar a nan? Kar dai ace wani sherin ne kuma ya ta nufo ni da shi, gaskiya wannan matar ta sanya ni tsaka mai wuya....

“Alhaji Musa ashe haka kuma abu ya kasance” siririyar muryarta ce ta karaɗe ɗakin ba tare da na kalleta ba na zauan bisa bancin da ke tsakiyar ɗakin, a zuciyata nace bari dai na nuna dakewa ga wannan mata, koda kau sau ɗayane a rayuwata.

Wane abu kuma? Na mayar mata da ƙarfin zuciya, “abokin aikinka ne ya kirani yake ceman wai an zartar ma da hukumncin ɗaurin shekara goma, ba tare da zabin biyan tara ba”.. da na kashe Wa? Ko kuma da na aikata wane laifi? Da har za a zartar man da wannan hukuncin? Shari’a ce yanzu alka fara na sanya lauyoyi na su ɗaukaka ƙara kuma in sha Allah zuwa gobe ma na bar gidan nan, domin da zaran an karɓi takardar ɗaukaka ƙarar za a bayar da beli na, sai kuma me?

Ta yi murmushi ta ce, “Allah ya baka haƙuri ni ba da wata manufa na zo ba dama na zo ne domin samo hanyoyin da zaka fita daga wannan gida, saboda ba zan manta da taimakon da ka yi man ba, wanda ya sa na mallaki gida, duk da cewa dai kai ma ka fitar da kanka a lokacin amma dai in abokin huɗɗa ya shiga wani hali akwai buƙatar a shiga cikin lamarin domin kawo masa agaji..”

“Lokaci ya yi malama kin san yanzu ba lokacin ziyara ba ne kawai dai an bar ki ne”, wani ɗan tsukakken jami’in gyaran hali ne yake magana a ƙoƙarinsa na shigowa cikin ɗakin. “a matsala ofisa hakan ma da ka yi man na gode, kuma na isar ma da saƙon da na ke son isar wa.” Fatima ta mayar masa da martani tana ƙoƙarin fice wa daga ɗakin.

Tun bayan da aka mayar da ni ɗaki ba abinda nae faman yi sai tunani, da ƙyar na samu na yi sallah azahar da la’asar yanzu kuma da muka kammala sallar magariba, na zauna kamar ina lazimi, amma ba abin da ke faɗo man a rai sai tunanin yadda na shigar da Fatima har ta samu gidan da ta buƙata nima kuma na samu rabona, na tuna cewa a lokacin babu sunan Fatima a waɗanda za a ba gidan amma ta fiya kuɗi da ake buƙata tare da wasu ƙarin kuɗaɗe muka zare wani form muka mayar da nata, bayan an bata gidan kuma ma kuje muka yi shige da fice tsakaninmu da ma’aikata tsara birane da ke da alhakin yanka filaye da taswirar wurare na bankinmu, aka ƙara matra fili mai girma daga cikin filin da aka ware domin gina masallaci a rukunin gidajen.

Mu da muka yi aikin sai da muka tashi da wasu filaye masu girma a wajen, wanda duk wannan abun shugaban mu bai sani ba mu kaɗai ke kidanmu muke rawarmu.... “ƙarar buga ƙofar ɗakin mu ce ta katse man wanna tunani na tashi na nufi baƙi ƙofar ɗakin, wani ne sanye da kayan waɗanda aka tsare ya miƙo man wata roba ta wata ‘yar kafa dake jikin kyauren. “ga abincinka” abin da ya faɗa ke nan kawai ya juya. Na kalli abin da aka ce shi ne abinci na ina juya shi cikin takaici ko almajirin gidana ba za a zuba mashi abinci a wannan robar ba, kuma abin da ke ciki na gaza bambancewa tsakanin tsari da kuma tuwo, wasu hawaye masu zafi suka zubo man a fuska, na yi tsaye na gaza matsawa ki’ina daga bakin ƙofar ɗakin.

Lallai na shiga matsala abin da na iya furtawa ke nan, na tuno da irin tarin dukiyar da na mallaka amma wai nine aka yankewa hukunci ba tare da zaɓin biyan tara ba. Na tuna ranar da aka kawo man sammaci ina zaune a gida wai ana tuhumata da yanka filaye inda bai dace ba ta ɓarauniyar hanaya da amfani da kujerata wajen raba filaye yadda bai kamata ba, wanda a cewar su wai hakan ya haddasa asarar dukiyoyi da rayuka a unguwar Galadima da muka yamnka gab da saukar gwamnatin da ta shuɗe.

A lokacin dariya na yi ina kallon abun matsayin shirme, na ɗauko wayata na kira shugaban jam’iyya duba da cewa duk wasu abubuwa da shi muka shiryasu, amma abin da ya ce man shi ne, “Musa kasan dai ba gwamnatinmu ba ce, kuma kafin mu tafi sai da muka yi ma ƙoƙari muka sa ka koma aiki da gwamnatin tarayya, duk domin mu tseratar da kai, yanzu wannan wutar kai ya kamata kasan yadda zaka kashe ta”.

Duk da haka ban ɗauki abun da muhiummanci ba hakan ya sa na kira lauyana na sanar da shi, amma ranar da aka fara zaman farko a kotun na fusknaci akwai matsala, domin har sabon sakataren gwamnati da manyan jami’an gwamnati mai ci sun halara wajen, na yi mamaki da cewa ni kaɗai ake tuhuma da laifi duk da cewa ba ni kaɗai bane na kitsa abubuwa.

Lauyan masu gabatar da ƙara ya yi bayanin cewa ana tuhuma ta da laifin yin amfani da ofishi na, na sanya mutane cikin matsala, ya bayyana cewa, yadda muka shirya kutuguilar yanka filayen unguwar Galadima ta hanyar saida hanyoyin magudanan ruwa da wasu filaye da aka ware domin gina wasu abubuwa, shi ya haddasa matsalar da aka samu a yankin wanda ruwa ya gaza samun hanya har ya yi wa talakwa ɓanna na rusa gidaje da asarori dama rasa rayuka.

Haka kuma ya gabatar da taswirar zanen unguwa na farko da yadda ya kamata a ce an yanka ta, amma na yi amfani da ofis ɗina na yayyankawa yan uwa da abokan arzuka filaye.

Ƙarshe ya bayyana cewa laifin da ake zargi na farko ya saba dokar aikin gwamnati ta ƙasa sakin layi na takwas cikin ba. Laifi na biyu kuma cin amana ne na ƙasa.

Duk ƙoƙarin da lauya na ya yi na kare ni amma abun ya ci tura sakamakon hujojin da aka riƙa gabatarwa masu nuna cewa lallai na aikata wannan laifin.

Kafin yanke hukuncin sai da alƙalin ya ɗauki tsawon lokaci yana bayyana wa mutane muhimmancin in suka ga an yanka filaye ba bisa ƙa’ida ba da su je kotu su kai ƙara ba wai su tsayaba sai an samu matsala sannan a shiga taraddadi, ya bayyana cewa ba wani mai hurumin yanka filaye ba bisa ƙa’ida ba koda gwamnati ce ta yanka su to zaku iya kawo ƙararta sai a diba masalahar abun domin fitar da mutane daga cikin matsala.......

“Wai Musa tsayuwar me kake a nan tun ɗazu? Ya kamata ace fa ka shigo daga ciki ka zauna domin kana da hurumin da zaka sa a riƙa kawo ma abinci daga gida kamar yadda ake yi man....” maganar abokin zaman ɗakina ne ta dawo da ni cikin hayaci na, cikin rashin ƙwarin guiwa tare da nadama na nufo kan gadona hawaye na kwararo man a ido, ina tunanin duk wannan halin da na shiga Fatima P.A tana da masaniya kuma ita ce inji na faɗa wa ta a wannan hali, sai yanzu na tuno da ita, harƙallar da muka yi da ita kuma ta faɗo man a rai kuru-kuru lallai ban kyauta ba, abin da na cigaba da furtawa ke nan......

Muhalli, Sutura

Post a Comment

0 Comments