Ahmed Adamu Yarma (2023). A Dalilinsa Ne. Ɗaukar Jinka (Labaran Da Suka Samu Nasara A Gasar Gajerun Labarai Ta Arc. Ahmed Musa Dangiwa, 2022). Kangiwa Multimedia and Communication Company LTD
A DALILINSA NE
Na
Ahmed Adamu Yarma
Shaye-shaye na ɗaya daga cikin munanan ɗabi’un da ke
wargaza rayuwar al’umma, musamman a wannan zamanin da zaman banza ta zama
sana’a. A wani ɓangare kuma gurɓatattun matasa ke mayar da
ingantattun magungunan kayan maye ta hanyar amfani da su ba bisa ƙa’ida ba, domin samun kuzari wajen yin aikin ƙarfi, ko donkawai samun nishaɗi da holewa.
Tun
bayan rasuwar mahaifina, kasancewar bani da kowa, ƙanin
mahaifina Baffa Sale ya ɗauke
ni, ya mayar dani gidansa. Ya kasance ba shi
da wata sana’a sai shaye-shaye. Duk lokacin da ya dawo cikin maye sai
ya hau matan gidan da duka, hakan ya sa duk matar da ya auro ba ta zama, saboda mummunar ɗabi’arsa. Har gidan ya zama daga ni sai shi
kaɗai muke rayuwa a
ciki.
A kwana a tashi ya zamana idan yaje ya yi shaye-shayensa ya dawo a buge abu kaɗan sai ya rufeni da duka har ta kai ga yana
haiƙe
mini da ƙarfi
duk da bana so amma ba yadda na iya.
Wasu
lokutan idan cin zarafi da takaicin
rayuwar da nake ciki suka
ishe ni, sai na kwaso ajiyayyun kayan mayensa da yake ajiyewa a gida nima na
sha, ko ya rage mini
raɗaɗi da baƙin cikin da na ke
ciki. Har ta kai ga idan ya haiƙemini sai na sha ƙwaya
sannan nake iya samun barci. Haka nayi ta zama da ƙanin
mahaifina Baffa Sale ya mayar dani
sa ɗaka ba kunya ba
tsoron Allah.
Yau da gobe ya sa idona ya buɗe,
kunya irin na ‘ya
mace ta fice daga idona, na zama tantiriyar ‘yar ƙwaya, a haka nake zuwa makaranta, watarana in je
a buge watarana a hayyacina. Babu wanda ya damu da ni balle rayuwata, ƙawayena duk suka gujeni, ba mai son raɓuwa dani. Na zama kamar ni ɗaya ce nake rayuwa a duniyar, kowa
ya guje ni.
Babu wanda ya fahimceni, ya fahimci rayuwata, kamar Dokta
Rufa’i, malaminmu ne dake ɗaukarmu darasin halayyar ɗan adam, shi kaɗai ne ya fahimci
irin gurɓatacciyar rayuwar da na ke ciki, bai taɓa nuna mini ƙyama ko hantara ba, ya sha kirana yana mini nasiha akan
irin rayuwar da na tsinci kaina a ciki, har ya fara fahimtar ba a son raina
nake shaye-shaye ba, akwai dalilin da ya jefa ni cikin wannan mummunanr ɗabi’a, amma nakan
kasa faɗa masa komai, saboda ina ga idan na faɗa masa na tona
asirin gidanmu ne. Yayi iyakar ƙoƙarinsa domin yaga ya dawo dani kan layi, amma naƙi ba shi fuska har ta kai ga ɗalibai suka fara
zargin ko yana sona ne, da ya fahimci mutane sun fara yiwa abun wata fassara
sai ya saduda ya barni da halina, daga ƙarshe har ta kai ga
an koreni daga makaranta.
A ranar da aka koreni daga makaranta ne, Baffa Sale ya dawo
cikin dare a buge, ya zo zai haiƙe mini, cikin ɓacin rai na rarumi ɗaya daga cikin
kwalaben shaye-shayensa na rusa masa a kansa, wanda hakan yayi sanadiyar
tsiyayewar idonsa guda ɗaya, daga ranar na gudu na bar gidan na koma gararamba a
gari a gari, lungu-lungu, kwararo-kwararo, rashin mafaɗi, rashin abun yi,
da rashin muhalli ya ƙara dulmuya ni cikin shaye-shaye. Na
cire rai daga kyakkaywar rayuwar
duniya.
Duniya
ta yi mini duhu. Na rame na lalace, zazzaɓi mai tsananin zafi ya kama ni, jira kawai
nake mai aukuwa ta auku!
A cikin wannan hali ne kamar daga sama, Allah ya kuma
jefo mini Dokta Rufa’i. Kallo ɗaya na masa, na ji wani irin farin ciki ya lulluɓe ni, na ɗaga kai na kalle
shi; farar fuskarsa ta zamto tamkar hasken farin wata a cikin duhuwar baƙin daji, a karo na farko naji zuciyata tayi fari fat,
zazzaɓin dake jikina lokaci ɗaya naji ya fara
sauka.
Dokta Rufa’i bai tsaya wata-wata ba, ya ɗauke ni, ya kai ni
asibiti, sai da na shafe wata uku ina jinya a can, ya na ɗawainiya da ni ba
dare ba rana. Bayan na murmure, na dawo hayyacina ne, ya ɗauke ni, ya kaini
gidansa, inda yake zaune da mahaifiyarsa wanda ake kira Umma. Daga nan na ci gaba da zama tare da Umma, ta ɗauke ni tamkar ‘yar da ta haifa a cikinta.
Dokta kuwa ya ci gaba da kula da ni, ba tare da gajiya wa
ba, kullum cikin ɗawainiya yake da ni. Nagode wa Allah da ya haɗa ni da waɗannan mutanen kirki. Har ta kai ga irin
kulawan da Dokta yake bani ya fara kulle mini kai, na rasa wannan wane irin mutum ne? Na farko dai ni ba yar uwarsa
ba, kuma bai taɓa
nuna mini wani alamuna soyayya ba, balle in ce sona ya ke yi. Ya ma za a yi mutum mai mutunci irin sa ya so ni, ni da baffana ya lalata mini
rayuwa tun ina ‘yar ƙarama,
idona ya riga ya buɗe, har ta kai ga ba wani kayan maye da na taɓa gani a duniyan da ban taɓa sha ba.
Watarana, ina zaune tare da Umma, muna hira mai daɗi irin na ‘ya da uwa, Dokta Rufa’i ya shigo da takardu a
hannunsa. Ya samu wuri ya zauna kusa da Umma,
ya shaida mini cewa ya sama mini gurbin karatu a ƙasar
Birtaniya. Farin ciki maras misaltuwa ya lulluɓe ni, na rasa ina zan sa kaina saboda murna, murnata ta koma ciki a lokacin da na ga Umma
ta haɗa rai, nan take ƙwalla
suka fara zuba daga idanunta. Dokta ya
hau rarrashinta, ya kai ta ɗaki
ya dawo wurina. Cikin
sanyin jiki na ce masa na ga Umma kamar ba ta son tafiyata, in dai haka ne ni na haƙura.
Dokta
ya yi murmushi ya girgiza kai yace mini, “Kansa’u yanzu kam ina ganin lokaci ya yi da ya kamata in miki bayani tunda za ki
tafi karatu, na san kanki ya
sha kullewa akan irin kulawar da nake ba ki. Ki sani ba ni ɗaya bane Umma ta haifa, mu biyu ne a wurinta, ni da ƙanwanta
Farida.
Farida
ta taso yarinya mai hankali da nutsuwa daidai gwargwado, sai dai kullum
matsalarta ɗaya ce, Farida
ta kasance irin mutanen nan ne masu sa abu a rai, idan ta sa abu a
rai komai ƙanƙantarsa
in ta rasa shi sai ta shiga
tsananin damuwa maras misaltuwa. Ba tare da mun ankara ba ashe ta faɗa soyayya da wani yaro, kafin mu farga, soyayyar ta yi zurfi a zuciyarta. A daidai lokacin da mu ka ankara ne yaron
ya yanke alaƙa da ita, ya bar zuwa wajenta sannan
ya daina kiranta kwata-kwata, ashe mahaifansa ne suka tilasta masa auren wata
daga cikin danginsa.
Tun da abun ya faru Farida ba ta sake jin ɗuriyarsa ba, sai
kawai ta ji labarin yayi aure. Kamar yadda na faɗa miki Farida na da
sanya abu a rai, tun da ta ji labarin auren, ta gagara jure rashinsa, ta zauna
ba ci ba sha, daga ƙarshe abun yayi tsamarin har ta kai
ga ta ɗura wa kanta magunguna da suka wuce kima (overdose) wanda hakan ya yi sanadiyar
ajalinta.
Yau shekara biyu kenan da rasuwar Farida amma har yanzu
Umma ba ta cire ta a rai ba, rashin Farida ya taɓa zuciyar Umma
sosai, duk da tana ɓoye mini amma na jima da fahimtar hakan.”
Ya ɗaga kansa ya kalle ni, ido cikin ido ya cigaba da cewa,
“cikin ikon Allah, tun ranar da na fara ganinki a jami’a na fahimci kuna matuƙar kama da Farida, kusan komanku ɗaya, musamman
muryarku.
Daga
nan ki ka shiga raina duk da kasancewarki ‘yar maye. Na yi bincike a kan ki
na gano cewa ba ki da iyaye, a hannun lalataccen baffanki ki ke, daga nan na
sha alwashin sai na dawo da ke hayyacinki, in son samu ne ma in
dawo dake hannun mahaifiyata ki maye mata gurbin Faridanta.
Yanzu
haka da kika ga ta shiga damuwa fargaba take
kar ki tafi kamar yadda Farida ta tafi ta barta. Burin Farida ne a lokacin da
take raye ta je Birtaniya karatu, shi ne
na cika mata akanki. Don haka ki shirya nan ba da jima wa ba jirginku zai tashi.” Ban san lokacin da
idanuna suka fara zubar da hawaye ba. Na tabbatar masa insha Allahu zan maye wa Umma gurbin
Farida, ya ji daɗin jin haka. Na tashi na je wurin Umma na rarrashe ta, ita ma na tabbatar mata cewa ta ɗauka Faridarta tana nan raye, ba zan taɓa watsa mata ƙasa a ido ba.
Bayan
kwanaki jirginmu ya tashi
sai Birtaniya, na ɗau tsawon shekara shida ina karatu a can. Ba ni
da burin da ya wuce in kammala karatuna
na
dawo gida Nijeriya
in yi tozali da Umma, in kuma yi tozali da Dokta don tunda na tafi babu garin
Allah da zai waye ba tare da nayi tunaninsa ba, tun ina ƙaryata
kaina akan na kamu da sonsa, har na tabbatarwa kaina tabbas na kamu da tsananin
sonsa.
Bayan
na kammala karatuna ne, na
dawo gida Najeriya. Na sa a raina yanzu
ne lokacin da ya kamata in bayyanawa Dokta sirrin da ke cikin zuciyata, na tabbata yadda na sauya yanzu kam zai iya karɓar soyayyata.
Ina shiga gidan na samu ba kowa a ciki, da na fito nayi tambaya ake shaida mini ai Dokta ya haɗu da tsautsayi wani
mashayin matuƙi ya buge shi. Ban tsaya wata wata
ba na garzaya asibitin, na samu Dokta a kwance shame-shame, jikinsa duk
bendeji, ba ya iya ko magana, Umma na zaune a gefensa, tana ganina ta miƙe zumbur kamar wanda aka sokawa allura. Cikin gaggawa naje
na sunkuya a gabansa cikin shessheƙar kuka, ya kalle
ni daga sama har ƙasa ya ga yadda na sauya, duk da
tsananin ciwon da yake fama da shi ya yi murmushin gamsuwa da jin daɗi.
Umma take shaida mini cewa, yau kwana uku kenan wani
direba ya shawo kayan maye ya kaɗe Dokta yayin da ya zo tsallaka titi, a hakan ma abun
yazo da sauƙi, don mashayin direban ma ya rasu.
Ban yi ƙasa a guiwa ba,na ɗauke shi na kai shi babban asibiti a ranar. Da yake ya riga da ya bugu ta ciki ba‘a ankara ba a ranar ya cika, yace ga garinku. Allah
sarki Dokta! Ashe
da rabon za mu sake haɗuwa!
Rashin Dokta ya girgiza
ni ba kaɗan ba, ku san zan iya cewa rasuwarsa ta fi taɓa mini zuciya sama da rashin iyayena!
Na
ci gaba da zama da Umma, baiwar Allah, ta
riƙe ni
a matsayin ‘ya a
lokacin da nake buƙatar
uwa. Na maye mata gurbin ‘ya’yanta,
muka zauna cikin aminci, na riƙe ta kamar uwar da ta tsuguna ta haife ni.
Tun
dawo wa ta
daga karatu, na
samu aikin koyarwa a jami’a mallakar jiha.
An so a riƙe
ni a ƙasar
waje, amma na ƙi
yarda na zauna a can, ni da nake da Umma da Dokta, sai dai kash gashi daga
dawowa ta Allah ya karɓi Dokta.
Tasirin da Dokta yayi a rayuwata yasa na ƙuduri niyar ɗaurawa daga inda ya tsaya, na taimakon mutane musamman waɗanda su ka tsinci
kansu a cikin irin jarrabawar da ta same ni.
Watarana
ina gyaran
takardun jarrabawan ɗalibai, sai na ci karo da takarda wani ɗalibi
mai suna Kamilu Abdullahi, takardar cike
take da abun mamaki, tambayoyi guda uku kacal nace su amsa a cikin biyar, amma Kamilu ya amsa duka, kai
har abin da ban tambaye shi ba sai da ya rubuto, ya cika mini takardu da rubutun da ya wuce hankali. Na yi matuƙar mamaki da ganin
takardan. Ban yarda ba, nace a raina duk yadda aka yi yaron nan
satar amsa ya yi, amma duk da haka kansa
na ja, don haka sai nasa a nemo mini shi.
Yana
shigowa ofishina mamaki ya kama ni,
kasancewar ba yadda nake siffanta shi a zuciyata haka na ganshi ba. Saurayin da ke tsaye a gabana kana ganinsa kaga ɗan ƙwaya, idanunsa jawur kamar garwashin wuta,
bakinsa yayi fari fat bushe, yana sanye da wando ɗamamme kamar mai shirin yin kokuwa. Wannan riƙƙaƙen ɗan ƙwayar fa na tambayi kaina a cikin zuciyata.
Ya
buɗe baki ya gaishe ni,
warin wiwi ya daki hancina. Na kawar da kai gefe, na tambaye shi ya aka yi ya amsa tambayoyi
biyar alhali nace a amsa uku kaɗai.
Ya hau sosa kai, yana magana irin na bugaggu, “kawai naga…” Ya carke sannan ya
cigaba.“Sun mini sauƙi
ne, shi yasa na amsa duka.” Mamaki ya kama ni, na
girgiza kai na masa ishara da ya zauna,
sannan na ɗauko
sabuwar takardan da ba komai a cikinta na miƙa
masa haɗe da
takardan tambayoyin jarrabawa, nace ya sake amsawa a gabana don in ƙure
shi. Ya yi hamma ya yamutsa fuska sannan ya kama
rubutu tiryan
tiryan niko na zubawa sarautar Allah ido. Cikin abin da
bai gaza minti talatin ba ya sake amsa dukkan tambayoyin, ya miƙo man takardan na kalla cikin mamaki. Yanzu kam na
yarda da kansa ya rubuta ba satar amsa ya yi ba. Abin da
ya ɗaure mini kai yanzu
shi ne ya aka yi lalataceccen yaro irin wannan, wanda da ka ganshi kaga riƙaƙƙen ɗan ƙwaya amma yake da wannan baiwa.
Tun
daga ranar na ja Kamilu a jiki, har muka saba duk inda ya ganni ko a buge ya ke zai taho da gudu ya karɓa mini jakata ya kai mini har cikin ofis.
Watarana na kira
shi ofishina, na ke
tambayarsa akan abin da ya jima yana kulle mini kai game da shi,
me yasa yake shaye-shaye
alhali ya kasance ɗalibi
mai fikira da hazaƙa.
Nan take hawaye suka fara kwaranya daga cikin idanunsa, bayan na rarrashe shi,
na kawo masa ruwan sanyi daga cikin firij.
Ya
fara bani labarin dalilin da ya jefa shi cikin wannan ɗabi’a ta shaye-shaye.“Tun ina yaro na taso mai hazaƙa a
makaranta. Kusan duk makarantar ba mai ƙoƙarina. Hedmastanmu ya sha zuwa wurin
mahaifina yana ba shi shawari akan
ya kula da karatuna sosai, ganin
yadda nake da ƙoƙari. Babana bai taɓa ɗaukar
abun da muhimmanci ba, kasancewar irin mutanen nan ne masu mataccen zuciya, ya
tara mata har guda huɗu
amma ba shi da takamammen sana’a sai sayar da ƙwaya
a wata tsohuwar gindin bishiyar durumi dake tsakiyar ungunwanmu.
Gindin
durumin majalisa ne da ya yi ƙaurin
suna waje tara mutane ‘yan
zaman banza da caca da shaye-shayen
miyagun ƙwayoyi.
Mahaifina shi ne Gardi a majalisan wato uban ‘yan caca, ya riga da ya kashe zuciyarsa da zaman
wurin ba dare ba rana, bai damu da cinmu ba balle shanmu.
Kwata-kwata bai damu da baiwar da Allah ya mini na karatu
ba, kullum damuwarsa shi ne mu ‘ya’yansa muje muyi dako ko aikin ƙarfi mu samo kuɗin da za mu kula da iyayenmu mata da
ƙannen mu ƙanana.
Kasancewar ni nake ƙulla masa tabar
wiwi kashi-kashi, yake kuma tura ni kasuwa in saro masa goro, yasa yau da gobe
na fara son ɗanɗana-ɗanɗanon maye. Abokaina da muke dako da su,
suka yi ta zuga ni akan in sato mana kayan maye a ɗakin mahaifina, domin mu sha, mu samu kuzarin
yin aikin ƙarfin da gaske. A haka har suke rinjaye ni, na faɗa
tsundum cikin wannan mummunar ɗabi’ar
shaye-shaye, har ta kai ga ba na
iya aikin komai in ban sha ba.
Baƙin
cikin tsintar kaina a cikin wannan mummunar hali ya sa zuciyar mahaifiyata ta buga, daga ƙarshe
ya yi sanadiyar ajalinta. Har tayi jinya ta koma
zuwa ga mahallincinta a asibiti, mahaifinmu bai taɓa leƙo ta ba, balle ya sayi magani. Ba ta jima da
rasuwa ba, jami’an yaƙi
da sha da fataucin muggan ƙwayoyi suka yi caraf da shi, a yanzu haka da
nake baki labari yana can yana girban abin da ya shuka a magarƙama.
Tunda
na faɗa wannan mummunar ɗabi’a, duniya ta yi mini baƙi,
na saduda da rayuwa, rayuwa kawai nake kamar dabba, aikin karfin ma yafara
neman gagara ta, ya zamana banida aiki sai shaye-shaye da zaman banza, har ta
kai ga na fara ɗauke
ɗauke in na rasa kuɗin da zan sayi kayan maye.
Wata
rana akayi rashin sa’a naje ƙwacen waya, aka kamani aka lakaɗa mi ni duka, daga ƙarshe
aka miƙa ni hannun jami’an tsaro sai gidan yari.
Kafin na ƙarasa
wa’adina ne,
wata ƙungiya
wayar da kan matasa akan illolin shaye-shaye ta yi belin ire-ire na, ta ɗau
nauyin jinyarmu da shirya mana darusan wayar dakai na tsawon lokaci, daga ƙarshe
ta ba wasu jari daga cikinmu, irina masu son karatu ta samar mana guraben karatu a makarantu daban-daban.
A ɗan ƙanƙanin lokaci, na fara dawowa hayyacina, na
fara karatu a jami’ar nan, haɗuwa
da muggan abokai ya sa na ƙara
komawa ruwa, duk da cewa na rage ba kamar can baya ba. Rashin tsayayyen uba da mafaɗi
da talauci da muggan abokai ne suka ƙara jefani cikin wannan mummunar ɗabi’ar ta shaye-shaye.”
Kamilu
na gama bani labarinsa, da
yadda aka yi ya faɗa
cikin wannan mummunar ɗabi’ar
shaye-shaye, na jinjina kai cikin
tausayi, gaskiya na yi matuƙar tausaya ma sa kasancewar yaro mai ilimi irin sa ya faɗa wannan jarrabawa, tabbas da ya samu mai ƙarfafa masa guiwa a karatu da bai faɗa cikin wannan
mummunar ɗabi’a ta shaye-shaye.
Tun
daga ranar na daɗa
jansa a jiki, kasancewar labarin rayuwar mu kusan iri
ɗaya ne, na mayar da shi tamkar ƙanina,
a duk lokacin da na masa wani alheri naga farin ciki a fuskarsa sai na tuna da
Dokta Rufa’i, sai na tuna da lokacin da yake ta faɗi tashi a kaina,
hakan ya kan ƙaramin ƙarfin guiwa don ganin
na ceto wannan saurayi mai fikira daga wannan mummunar ɗabi’a.
Sannu
a hankali har ya watsar da shaye-shaye gaba ɗaya da taimakona da kuma taimakon Umma wanda
ta ɗauke shi, shi ma
tamkar ɗa.
Bayan
ya kammala karatu ya kama aiki a babban asibiti jiha, ƙannensa da suke zaman banza, ya dawo dasu
cikin hayyacinsu, wanda suke makaranta suka watsar ya mayar dasu, masu sana’a
ya ƙara
musu jari, iyayensu mata suka dawo cikin hayyacinsu duk a sanadin Kamilu wanda yanzu ya dawo kamili.
Tasirin
da Dokta Rufa’i yayi a rayuwata yasa na buɗe Gidauniyar mai sunan Dokta Rufa’i foundation wanda ta bayar da muhimmanci
akan zaƙulo
mutanen da suka faɗa
mummunar ɗabi’ar
shaye-shaye, a ƙanƙanin
lokaci muka ɗauki
nauyin mutum
arba’in. Da naje duba mutanen domin ƙarfafa musu guiwa da ba su shawarwari akan yadda za su daina wannan mummunar ɗabi’ar.
Kwatsam
na hango wani dattijo rike da sandar makafi abun ya bani
mamaki, shaye-shaye
har da makafi? Da na matso kusa da shi
sai naga ashe Baffa Sale
ne ƙanin
mahaifina, warin giya ya buleni, na kalli idon da na fasa masa naga baya gani.
Gaba ɗaya ya rame, ya lalacewa,
tsufa ta cimmasa ba abin da ya ke yi sai warin giya da zarni fitsari, na yi masa sannu, nan take ya gane muryata, “Kansa’u,
dama kina raye?” Na
amsa masa, cikin
tsana wata zuciyar tace in sa ayi waje da shi,
tausayinsa ya kamani, yana kakkarwa, ya kuma ce,“nawa
za’a bamu ne da aka kawomu nan wurin?” Hali
zanen dutse, mai hali ba ya sauya
halinsa. Na
girgiza kai cikin takaici na ce masa, “In har ka bar shaye-shaye, ba abin da za ka
nema ka rasa.”
Da yake nasan halin kayana, in ya fahimci ba kuɗi za a ba shi ba guduwa zai yi. Sai na ɗau wasu ‘yan kuɗaɗe na bashi, ashe a hannu yake, yasan yadda yayi ya sulale. Bayan
awanni aka zo aka gaya mana cewa ɗaya daga cikin mutanen da muka killace mota
ta kaɗeshi, muna zuwa mu ka ga Baffa Sale
ne, direban da ya kaɗeshi
da mutanen dake wajen
suka shaida mana
cewa ya sha kayan maye ne ya yi tatul yana ta
tangaɗi akan titi, direban bai Ankara ba ya kaɗeshi, na tsaya akan gawar na kalli Baffa Sale
dake kwance jina-jina
ɗaya idon ma ya fashe, na kalleshi na tuna tun lokacin da nayi wayo kullum a wahale yake a sanadiyar
shaye-shaye da yake yi, yanzu yayi rayuwarsa a
wahale ya tafi a wahale kenan Allah sarki Baffa Sale
ƙarshensa
kenan.
Bayan wani lokaci na ci gaba da rayuwata, daga Umma
sai Kamilu
su kaɗai
ne dangina, lokaci ɗaya na kwanta rashin lafiya mai
tsanani, Kamilu ya ɗaukeni ya kaini
asibitinsu, da aka gwadani akace ina fama da ciwon ƙoda,
dole sai an mini
dashe. A karo na biyu kenan a rayuwata na cire tsammanin da
rayuwa, ni da bani da kowa a duniyarnan wa zai bani ƙoda, ina kwance ga ciwo ga tunani ga
zullumi, Kamilu da Umma suka zo suka zauna a gefena, Kamilu ya hau kwantar mini
da hankali tare da ƙarfafa mini guiwa.
Daga ƙarshe ya tabbatar mini
da cewa ya riga da ya gama cike takardu zai bani ɗaya daga cikin ƙodarsa, hawayen farin ciki suka kwaranyo daga idanuna,
ashe tasirin da nayi a rayuwar Kamilu har ta kai ga zai iya bani ƙoda.
Allah sarki Dokta Rufa’i! A
dalilinsa ne rayuwata, ta sauya na zama mutum, bayan rayuwata ta lalace. Allah sarki Kamilu! A dalilinsa ne yanzu
zan cigaba da rayuwa, bayan na ɗebe tsammani.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.