Ticker

6/recent/ticker-posts

Hukuncin Mai Yanke Zumunci

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Assalamu alaikum malam Allah ya saka da alkhairi Allah ya biya da gidan aljanna tambayata malam mene ne hukuncin mai yanke zumunci Allah yabada ikon amsawa🙏

𝐀𝐌𝐒𝐀

Wa'alaikum Salaam Warahmatallahi Wabarkatahu

Hadisin Zubair dan Mad'im Allah ya kara yarda a gareshi yace, Hakika Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam Ya ce: Mai yanke zumunci ba zai shiga aljanna ba. (Bukari da Muslim).

Hadisin Abi Bakrata Allah ya kara yadda a gareshi ya ce Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam Ya ce: Babu wani zunubi wanda ya cancanta Allah ya gaggauta yi wa mai shi ukuba tun daga nan duniya bayan wanda ya tanada a lahira kamar mai yanke zumunci (Bukari).

Duk wanda ya yanke Zumunci ga makusantansa raunana (wato Talakawa mabukata) ya kaurace musu, baya sada Zumunci a garesu, baya kyautata musu, alhali yana da iko da wadatar da zai taimaka musu, to wannan haramun ne shiga Aljanna a gareshi, sai dai in ya tuba ga Allah, ya dawo ya kyautata musu.

Mai yanke Zumunci tun daga duniya yan'uwansa baza su sami shakuwa da shi ba, kuma har ma wani lokacin a rika mantawa da shi gaba ɗaya.

Ya zo a cikin Hadisi daga Manzon Allah Salallahu Alaihi wasallam Ya ce: Wanda ya zamo yana da yan'uwa mabukata baya kyautata musu, sai ya juyar da taimakonsa ga wasu daban na nesa, to Allah ba zai karbi wannan aikin nasaba, ba zai yi duba agareshi ranar Alkiyama ba. In kuma shi ma yazamo bashi da hali (wato shi ma mabukacinne) to ya rika ziyartarsu yana karfafar halin da suke ciki Saboda fadinsa Alaihissalam; Ku sadar da Zumunci ko da da Sallamane.

Sada zumunci yana da tarin falala, wanda idan muka ɗauke falalar da za a samu a lahira, zamu ga cewa tun daga duniya idan kaje ka sada zumunci ko da ziyarar abokin ka ne ko wani dan'uwanka na jini, zakaji ka samu nutsuwa da nishadi, shi ma kuma zai ji dadi sosai.

Sada zumunci shi ne kyautatawa da jinkai da bibiyar yan uwa (ma'abota zumunci), ta hanyar sadar da dukkan alheri gare su, da kawar da dukkan sharri daga garesu gwargwadon iko.

Ziyartarsu da amsa kira da gayyatarsu da taimaka musu da dukiya da tausasa magana gare su da kawar da kai daga kura-kuransu da yi musu addu'ar alheri.

Hadisin Nana Aisha Allah ya kara mata yarda tace, Sada zumunci yana rataye ne da Al-Arshi, yana cewa: wanda ya sadar da ni to zan sadar da shi, wanda ya yanke ni to zan yanke shi (Bukari da Muslim).

MA'ANA shi ne zai sadar da shi da Rahmar Allah (SWT) ko ya yanke shi daga samun Rahama.

Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam Ya ce: Ba Sadar da zumunci ba ne in anzo maka kaje, in an baka ka bayar, in an girmamaka ka girmama, Sada Zumunci shi ne wanda ya yanke maka ka Sadar masa ( wato Ka ziyarci wanda baya ziyartarka, ka bawa wanda ya hanaka.)

Malamai sun bayyana Sada zumunci a matsayin ɗaya daga cikin manyan Alhairan da ake gaggauta bayar da lada akai, kamar yadda ya zo a cikin Hadisin Manzon Rahama Annabi Muhammad (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce: Alherin da ake gaggauta bayar da lada a kai shi ne Sadar da zumunci.

Abin da Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) yake kokarin nuna mana shi ne Musulmi ya kasance a ko da yaushe mai tsananin kula da yan'uwansa na jini, dangi gami da yan'uwa na ruhi, wato wadanda addini ya haɗa su.

Duk mai sada zumunci zai kasance masoyi ne ga kowa, yan'uwa da sauran dangi za su so shi, ba don yana ba su kuɗi ko wani abu ba, amma kasancewar yana daga cikin waɗanda suke bibiyar lafiyarsu da kuma matukar nuna tausayawa tare da jinkai gare su.

Ya Allah ka ba mu ikon sada zumunci domin saduwa da dukkanin alkhairan da ke cikinsa na duniya da lahira.

WALLAHU A'ALAM

Auwal Zakari Ayagi

Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance damu cikin wannan group domin Fadakarwa...

ƘARIN BAYANI

MENE NE HUKUNCIN MAI YANKE ZUMUNCI A MUSULUNCI, KUMA MENENE SAKAMAKONSA A DUNIYA DA LAHIRA?

TAMBAYA:

Assalamu alaikum. Malam, don Allah ina neman ƙarin bayani kan hukuncin mutumin da yake yanke zumunci da danginsa ko ƴan'uwansa. Shin menene makomarsa a wurin Allah, kuma ta yaya ya kamata musulmi ya kasance wajen sadar da zumunci koda ƴan'uwan ba sa nufinsa da alheri?

AMSA:

Haɗarin Yanke Zumunci Da Falalar Sadar Da Shi

A cikin shari'ar Musulunci, yanke zumunci (Qati'atur-Rahim) yana ɗaya daga cikin manyan zunubai (Kaba'ir). Zumunci ba kawai ziyara ba ce; wani haƙƙi ne na jini wanda Allah Ya umarci a kiyaye shi. Wanda ya yanke zumunci ya saba wa umarnin Allah, kuma ya buɗe wa kansa ƙofofin tsinuwa da rashin albarka.

1. Tsinuwar Allah Ga Mai Yanke Zumunci

Allah Madaukakin Sarki Ya bayyana a cikin Alƙur'ani cewa waɗanda suke yanke zumunci sun cancanci tsinuwarSa, kuma zai toshe musu kunnuwa da idanu daga ganin gaskiya.

Allah Madaukakin Sarki yana cewa:

فَهَلْ عَسَيْتُمْ إِن تَوَلَّيْتُمْ أَن تُفْسِدُوا فِي الْأَرْضِ وَتُقَطِّعُوا أَرْحَامَكُمْ * أُولَٰئِكَ الَّذِينَ لَعَنَهُمُ اللَّهُ فَأَصَمَّهُمْ وَأَعْمَىٰ أَبْصَارَهُمْ

Hausa: "To, shin kuna fãtan idan kuka juya bãya, zaku yi barna a cikin ƙasa, kuma ku yanke zumunci tsakãninku? Waɗannan su ne waɗanda Allah Ya la'ance su, saboda haka Ya kurantar da su, kuma Ya makantar da gannansu." (Suratu Muhammad: 22-23).

2. Haramcin Shiga Aljanna

Babban hadarin da ke tattare da mai yanke zumunci shi ne korar da za a yi masa daga shiga gidan ni'ima (Aljanna). Wannan yana nuna cewa ko da mutum yana sallah da azumi, matuƙar yana yanke zumunci da gangan, to akwai babban shinge tsakaninsa da Aljanna.

An karbo daga Jubair bin Mut'im (R.A) cewa Manzon Allah (S.A.W) ya ce:

لَا يَدْخُلُ الْجَنَّةَ قَاطِعٌ

Hausa: "Mai yanke zumunci ba zai shiga Aljanna ba." (Buhari da Muslim suka rawaito shi).

3. Gaggauta Ukuba A Nan Duniya

Mafi yawancin zunubai ana jinkirta sakamakonsu ne har sai ranar Lahira, amma yanke zumunci da zalunci su ne zunubai biyu da Allah Yake gaggauta wa mutum ukuba tun a nan duniya kafin wadda take jiran sa a Lahira. Mai yanke zumunci zai ga kuncin rayuwa, rashin albarkar dukiya, da kuma ƙiyayya daga mutane.

An karbo daga Abu Bakrata (R.A) cewa Manzon Allah (S.A.W) ya ce:

مَا مِنْ ذَنْبٍ أَجْدَرُ أَنْ يُعَجِّلَ اللَّهُ لِصَاحِبِهِ الْعُقُوبَةَ فِي الدُّنْيَا مَعَ مَا يَدَّخِرُ لَهُ فِي الْآخِرَةِ مِنَ الْبَغْيِ وَقَطِيعَةِ الرَّحِمِ

Hausa: "Babu wani zunubi wanda ya cancanci Allah Ya gaggauta wa mai shi uƙuba a nan duniya, tare da abin da Ya adana masa a Lahira, kamar zalunci da yanke zumunci." (Tirmizi da Abu Dauda).

4. Wanene "Mai Sadar Da Zumunci" Na Gaskiya?

Mutane da yawa suna tsammanin sadar da zumunci shi ne ka ziyarci wanda yake ziyartarka. Amma a mahangar Musulunci, gwajin gaskiya na zumunci yana nan lokacin da ƴan'uwanka suka yanke ka, kai kuma ka ƙi yarda ka yanke su.

Manzon Allah (S.A.W) ya ce:

لَيْسَ الْوَاصِلُ بِالْمُكَافِئِ، وَلَكِنِ الْوَاصِلُ الَّذِي إِذَا قُطِعَتْ رَحِمُهُ وَصَلَهَا

Hausa: "Mai sadar da zumunci ba shi ne wanda yake saka alheri da irinsa ba (kana yi mini ina yi maka), a'a, mai sadar da zumunci na gaskiya shi ne wanda idan aka yanke zumuncinsa, shi kuma sai ya sadar da shi." (Buhari).

5. Falalar Sadar Da Zumunci (Albarkar Rayuwa)

Idan mutum yana son Allah Ya buɗa masa hanyoyin samun dukiya kuma Ya tsawaita masa rayuwa mai albarka, to hanyar ita ce sadar da zumunci.

Daga Anas bin Malik (R.A) ya ce: Manzon Allah (S.A.W) ya ce:

مَنْ أَحَبَّ أَنْ يُبْسَطَ لَهُ فِي رِزْقِهِ، وَيُنْسَأَ لَهُ فِي أَثَرِهِ، فَلْيَصِلْ رَحِمَهُ

Hausa: "Duk wanda yake son a yalwata masa a cikin arzikinsa, kuma a jinkirta masa ajalinsa (tsawon rai), to ya sadar da zumuncinsa." (Buhari da Muslim).

Kammalawa Da Shawara

Yanke zumunci yana jawo fushin Allah da tsinuwa. Ya kamata kowane Musulmi ya bincika dangantakarsa da iyayensa, yan'uwansa, da sauran danginsa. Ko da dangi suna da wahalar sha'ani, ka yi haƙuri da su don neman yardar Allah. Sadar da zumunci yana iya kasancewa ta hanyoyi da dama:

Ziyara: Zuwa gida a gaishe su.

Taimako: Ba su abinci ko kuɗi idan suna buƙata.

Saduwa Ta Waya: Kiran su don jin lafiyarsu.

Tausasawa: Yin magana mai daɗi da kau da kai ga kura-kuransu.

Ya Allah Ka ba mu ikon sadar da zumunci, Ka sanya albarka a cikin rayuwarmu, kuma Ka tsare mu daga tsinuwar masu yanke zumunci.

WALLAHU A'ALAMU

 ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

WALLAHU A'ALAM.

https://t.me/TambayaDaAnsa

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments