𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Kiristoci ne suka yanka Dabba daga Coci Suka kawo mana shin ya halatta mu ci? Shin cin yanke-yanken Kiristoci a wannan zamani namu na yau yana halatta, duk kuwa da cewa hanyoyin yanka a wurinsu sun yawaita, watau kamar yin amfani da injuna, da kuma abubuwa masu daskarar da kwakwalwa a wurin yankan?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗
Cin yanke-yankensu
yana halatta, matukar dai ba a san da cewa an yanka dabbar ne ta hanyar da ba
ta dace da Shari'a ba, saboda asalin lamari shi ne halaccin cin sa, kamar dai
yankan Musulmi, saboda faɗin Allah Maɗaukaki:
وَطَعَامُ
الَّذِينَ أُوتُوا الْكِتَابَ حِلٌّ لَكُمْ وَطَعَامُكُمْ حِلٌّ لَهُمْ
Da abincin waɗannan da aka ba su
littafi halal ne yake a gare ku, kuma abincin ku halal yake gare su. (Surah
Al-Maa’idah: 5).
Ya halatta muci
yankan da Kirista ko Yahudawa suka yanka. Amma da sharadi kamar haka:
1. Ya zamto yankan
basu yishi domin wanin Allah ba. Saboda faɗin Allah (swt):
حُرِّمَتْ
عَلَيْكُمُ الْمَيْتَةُ وَالدَّمُ وَلَحْمُ الْخِنْزِيرِ وَمَا أُهِلَّ لِغَيْرِ
اللَّهِ بِهِ وَالْمُنْخَنِقَةُ وَالْمَوْقُوذَةُ وَالْمُتَرَدِّيَةُ
وَالنَّطِيحَةُ وَمَا أَكَلَ السَّبُعُ إِلَّا مَا ذَكَّيْتُمْ وَمَا ذُبِحَ عَلَى
النُّصُبِ وَأَنْ تَسْتَقْسِمُوا بِالْأَزْلَامِ ۚ ذَٰلِكُمْ فِسْقٌ ۗ الْيَوْمَ
يَئِسَ الَّذِينَ كَفَرُوا مِنْ دِينِكُمْ فَلَا تَخْشَوْهُمْ وَاخْشَوْنِ ۚ
الْيَوْمَ أَكْمَلْتُ لَكُمْ دِينَكُمْ وَأَتْمَمْتُ عَلَيْكُمْ نِعْمَتِي
وَرَضِيتُ لَكُمُ الْإِسْلَامَ دِينًا ۚ فَمَنِ اضْطُرَّ فِي مَخْمَصَةٍ غَيْرَ
مُتَجَانِفٍ لِإِثْمٍ ۙ فَإِنَّ اللَّهَ غَفُورٌ رَحِيمٌ
An haramta muku mũshe
da jini da nãman alade da abin da aka ambaci sũnan wanin Allah a gare shi, da
mãƙararriya
da jefaffiya da mai gangarõwa da sõkakkiya,
da abin da mãsu dãgi suka ci, fãce
abin da kuka yanka, da abin da aka yanka a kan gunki (shĩ
ma an haramta). Kuma kada ku yi rabo da kibiyoyi na cãca
wannan fãsiƙanci ne. A yau waɗanda suka kãfirta sun
yanke ƙauna daga addininku. Sabõda haka kada ku ji tsõronsu
kuma ku ji tsõroNa. A yau Nã kammalã
muku addininku, Kuma Nã cika ni´imaTa a kanku, Kuma Nã
yarda da Musulunci ya zama addini a gare ku. To, wanda aka sanya wa lalũra
a cikin yunwa mai tsanani, bã yana mai karkata
zuwa ga wani zunubi ba, to, lalle ne Allah Mai gãfara ne, Mai jin ƙai. (suratul Ma'idah
aya ta 3).
2. Ya zamto sunan
Allah suka ambata ya yin da za su yanka dabbar. Idan suka yanka da Sunan Jesus
ko Holy spirit ko sunan wani pastor, to ba za a ci ba. Allah (swt) yana cewa:
وَلَا
تَأْكُلُوا مِمَّا لَمْ يُذْكَرِ اسْمُ اللَّهِ عَلَيْهِ
Kada ku ci daga abin
da ba a ambaci sũnan Allah ba a kansa. (suratul An'am ayah ta 121).
3. Ya kasance abin da
suka yanka ɗin baya daga cikin
irin dabbobin da Allah ya haramta mana. Misali, alade ko kare ko jaki ba zai
halatta aci ba ko da sun yanka shi tare da ambaton sunan Allah.
Amma bai halatta Musulmi
ya ci abin da 'yan addinin Buddah ko hindu suka yanka ba. ko da sun ambaci
sunan Allah ya yin da za su yanka dabbar.
Sheik Uthaimeen ya ce
cikin littafinsa Ash-Sharhul Mumtii 12/148:-
ﻓﺎﻟﺤﺎﺻﻞ:
ﺍﻥ ﺍﻟﺬﻱ ﻋﻠﻴﻪ ﺟﻤﻬﻮﺭ ﺍﻫﻞ ﺍﻟﻌﻠﻢ ﺍﻥ ﻣﻦ ﺗﺪﻳﻦ ﺑﺪﻳﻦ ﺍﻫﻞ ﺍﻟﻜﺘﺎﺏ ﻭﺍﻧﺘﺴﺐ ﺍﻟﻴﻬﻢ ﻭﻟﻮ ﻛﺎﻥ ﻳﻘﻮﻝ
ﺑﺎﻟﺘﺜﻠﻴﺚ ﻓﺎﻧﻪ ﺗﺤﻞ ﺫﺑﻴﺤﺘﻪ، ﻭﻳﺤﻞ ﻧﻜﺎﺣﻪ
Ma'ana: ((A takaice
dai: Abin da majoratin masu ilmi suka ce shi ne duk wanda ya yi Addini da
addinin Ahlul kitabi, ya kuma danganta kansa zuwa gare su ko da kuwa yana cewa
Allah uku ne, to lallai ne cin wannan yankan halal ne, kuma auren su halal
ne)).
Sa'annan Al Imamul
Dabarani, Abul Dar'da, wata an yi masa Fatawa akan cin Yankan Kirista, suka ce
masa Kiristoti ne suka yanka Dabba daga Coci Suka kawo mana shin ya halatta mu
ci? sai da ya girgiza kansa ya ce Allah yafe mana, sai ya tambaye su shin su ɗin ba Ahlul-Ƙitabbi ba ne? Sai
suka ce ahlul-ƙitab ne, sai ya ce ai Abincin su halal ne, sabida haka
cewar ba a San ya suka yanka ba a Ina suka yanka, duk wannan ba hujja ba ne na
nuna Haramcin cin sa ba. Kawai in kana Bukata ka ci in ba ka Bukata ka bari, shi
ke nan shin ba Allah ya halatta mana cin abin Yankan su ba? Mun yi bayanin Ayar
jiya a Dayan Fatawar mu, sa'annan Duk Imaninka duk Tsarkinka duk Kyan-Kyaminka,
shin mun Kai Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wa Sallam ne? Duk Ayar da mutum zai
karanta ko ya fassara ka tsaya ka dubi ya rayuwar Annabi (Sallallahu Alaihi
Wasallam) yake?
Har kullum Ahlus
Sunnah wal Jama'ah a duk inda suke suna gina Addinin su ne a kan abin da ya
tabbata daga Alkur'ani Mai girma da kuma ingantattun hadithan Annabi mai tsira
da amincin Allah masu daraja. Amma saɓanin su, su kan gina Addinin su ne kawai a
kan abin da ya dace da son zuciyar su.
WALLAHU A'ALAM
Zauren Fatawoyi Bisa
Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance damu cikin wannan group domin Fadakarwa...
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.