Ticker

6/recent/ticker-posts

Gudummuwar Umaru Danjuma Katsina Wajen Fadakar Da Al’umma: Wasan Kulba Na Barna A Faifan Nazari

Citation: Abdullahi, B. and Soba, G. M. (2025). “Gudummuwar Umaru Ɗanjuma Katsina wajen Faɗakar da Al’umma: Wasan Kulɓa na Ɓarna a Faifan Nazari.” in Ɗunɗaye Journal of Hausa Studies, Vol. 03, No. 02, Pp. 152 – 159. www.doi.org/10.36349/djhs.2025.v03i02.019.

GUDUMMUWAR UMARU ƊANJUMA KATSINA WAJEN FAƊAKAR DA AL’UMMA: WASAN KULƁA NA ƁARNA A FAIFAN NAZARI

Na

Bala Abdullahi

Sashen Harsunan Nijeriya da Kimiyyar Harshe, Jami’ar Jihar Kaduna, Kaduna

and

Galadima Mubarak Soba

Department of Hausa, Federal University Dustinma

Tsakure:

Ayyukan adabi da dama sukan yi nuni da tsarin siyasa da zamantakewa da addini da falsafar al’umma. Don haka, marubuta adabi kan bayyana manufarsu ta hanyoyi mabambanta ta waɗannan ayyuka na adabi. Wasan kwaikwaiyo dai wani muhimmin reshe ne daga cikin rassa na adabi, kuma ta hanyar wasan kwaikwaiwo akan faɗakar da al’umma game da wasu matsaloli ko halaye mara nagarta da ta yi wa al’umma ɗaurin minti da nufin nusar da su domin a gyara gaba ɗaya. Ta haka ne wannan maƙalar ta mayar da hankali game da rawar da marubuta wasan kwaikwayo kamar Umaru Danjuma Katsina ke takawa don ganin al’umma sun faɗaku game da wasu matsaloli da suka yi musu katutu. Nazarin gundarin saƙon littafinsa na Kulɓa Na Ɓarna (wato Content Analysis) shi ne abin da ya yi jagora wajen fito da rawar da marubuta wasan kwaikwayo ke takawa wajen faɗakar da al’umma game da wasu illoli da ke damfare a cikin al’umma don su guje masu. Daga ƙarshe, an ɗora wannan bincike a kan ra’in gudunmuwar adabi ga al’umma domin nuni da gudummuwar da marubuta adabi ke badawa wajen wayar wa al’umma kai. 

Gabatarwa

Shi dai wasan kwaikwayo ɗaya ne daga cikin rassa uku na adabin Hausa. Sauran biyun su ne waƙa da kuma zube. Wasan kwaikwayo abu ne mai daɗaɗɗen tarihi a duniya, kuma babu wani wanda zai bugi ƙirjinsa ya ce ga haƙiƙanin lokaci ko ranar da aka farasai dai bayanin da aka sani kawai shi ne, wannan ɓangaren adabi ne da ya daɗe sosai. Wannan muƙala ta yi duba ne zuwa ga nau’in rubutaccen wasan kwaikwayo ne, tare da bayyana gudummawar marubuta wasan kwaikwayo wajen faɗakar da al’umma, da yi musu hannun-ka-mai-sanda don su guji aikata wani abu maras kyau, da kuma riƙo da halaye da ɗabi’u kyawawa. An ɗauki wani marubuci mai suna: ‘Umaru Ɗanjuma Katsina da littafinsa na ‘Kulɓa Na Ɓarna’ a matsayin misali.

Ma’anar Wasan Kwaikwayo

Masana da manazarta da dama sun bayyana ma’anar wasan kwaikwayo ta fuskar rarrabe ma’anonin kalmomin guda biyu, ‘wasa’ da kuma ‘kwaikwayo’. Wato dai kalmar wasa ta ƙunshi ma’anar aiwatar da wani abu wanda ba da gaske aka yi ba, don nishaɗantarwa da motsa jiki. Ita kuwa kalmar ‘kwaikwayo’ na nuna yin wani abu don kwatanta wani abu ta hanyar sauya kama kwatankwacin yadda wani yake yi, mutum ne ko dabba. Ga dai abin da wasu masan suka ce kamar haka:

Umar (1987:46-48) ya bayyana wasan kwaikwayo a matsayin kamance ko kwatanta wasu halaye na ɓangarorin rayuwa ta sigar wasa wato abin ya kasance ba gaskiya ba ne. A yayin da Price (1913) ya ce; ‘drama is an imitation of past action through dialogue and other symbols’’. Wato wasan kwaikwayo kamance ne aikin da ya gabata ta hanyar tattaunawa tsakanin ‘yan wasa da kuma yin nuni da wasu alamu.

Shi kuwa Ɗangambo (1984:4), a littafinsa mai suna Rabe-raben Adabin Hausa Da Muhimmancinsa Ga Rayuwar Hausawa, ya ce: “Wasan kwaikwayo kamar yadda sunan ya nuna, wasa ne da ake gina shi a kan kwaikwayon wani labara ko wata matsala da ake son nusarwa ga jama’a. Akan aiwatar da labarin ko matsalar cikin yaƙini, wato zahiri.”

Shi kuma Malumfashi (1985:15), a kundin digirinsa na biyu mai taken “Asali Da Bunƙasar Rubutaccen wasan Kwaikwayo Na Hausa”, ya bayyana wasan kwaikwayo da cewa: “Koyi ne da yadda wani ko wasu ke yin wani abu. A wajen koyin a iya samun canza kama ta magana ko na tufafi.

`Yar’aduwa, (2007:5) kuwa, a littafinsa na Wasan Kwaikwayon Hausa: Nau’o’insa da Sigoginsa, ya ce: “Ana amfani da ilimi ne domin tattara halayen mutane a kuma gudanar das hi a cikin tsarin wasan kwaikwayo cikin annashuwa don cin ma wata manufa.”

Shi kuwa Sulaiman, (2013) cewa ya yi: “A tawa fahimtar, wasan kwaikwayo, kwaikwayon wani abu ne ta fuskar wasa inda harhaɗuwar wasu ayyukan `yan wasa kan samar da cikakken labari don isarwa ga al’umma. Wannan labara mai ɗauke da wata manufa kan iya kasancewa ya faru cikin al’umma ko kuma ƙirƙirarsa aka yi.”

A taƙaice, wasan kwaikwayo wasa ne da ake ƙirƙira don kwaikwayar wani al’amarin da ya faru, ko ake hasashen faruwarsa ta hanyar sauya kama, don kwaɗaitarwa da jawo hankalin al’umma, ko tsoratar da su a kan wani abu kan ɗabi’u ko kuma al’adu ko yanayin sauyawar rayuwar don a nishaɗantar ko a faɗakar cikin wasa.

Ra’in Bincike

Gusau (2015) a littifinsa na Mazhabobin Ra’i da Tarke A Adabi da Al’adu na Hausawa ya kawo bayanai ga yadda adabi take ba da gudummuwa ga al’umma wajen inganta rayuwarsu da zamantewa.Wannan hanya ta nazarin gudunmuwar adabi ga al’umma tana mayar da hankali ne ga rawar da adabi yake takawa a hali na zamantakewa. Haka zalika, tana duba yadda adabi yake tafiya da al’adu da fasahohi na al’umma da suke daɗa inganta rukunonin rayuwa. Don haka wannan maƙala ta zaƙulo wannan ra’i domin yin nuni da yadda wannan wasa na Kulɓa na Ɓarna ke yin nuni da hali na zamantakewar al’umma kamar yadda marubucin ya nuna cikin littafin.

Taƙaitaccen Tarihin Marubucin Wasan ’’Kulɓa Na Ɓarna’’

An haifi Alhaji Umaru Ɗanjuma Katsina a ranar 10 ga Afrilu, 1950 a cikin birnin Katsina, unguwar Ƙofar Soro da ke ƙaramar Hukumar Katsina, ta Jihar Katsina. Mahaifinsa shi ne Muhammadu Ɗanjuma (Tsohon ma'aikacin N.A), sai mahaifiyarsa Hajiya Hadiza Lanso.

Umaru Ɗanjuma Katsina ya fara karatun boko matakin Firamare a Giɗaɗo Primary School Katsina' a shekarar 1966 ya kuma kammala a shekarar 1972. Yaa ci gaba da karutunsa na Sakandare a makarantar 'Goernment Secondary School Katsina' daga shekarar 1972 zuwa 1975. Haka zalika, ya yi ta karatu har ya sami takardar shaida ta kammala karatu na 'West African School Certificate' (WASC) a shekarar 1980. Daga nan sai ya tafi makarantar horo kan fim da Talabijin da ke birnin Landan, inda a nan ne ya sami takardar shaida ta Difloma kaMotion Picture da kuma Difloma kan wasan kwaikwayo da ba da umarni.

Alhaji Umaru Ɗanjuma Katsina ƙwararre ne a fagen aikinsa, a karon farko ya zama ma'aikaci a matsayin ƙaramin jami’in al'adu a ma'aikatar yaɗa labarai ta Arewa ta tsakiya da take Kaduna daga shekarar 1975 zuwa 1978. Daga baya, Umaru Ɗanjuma Katsina ya zama jami'in kula da al'adu, cibiyar nazarin al'adun Najeriya reshen Jami'ar Ahmadu Bello, Zariya. A shekarar 1980 ya zama babban jami'in al'adu a wannan cibiyar. Haka kuma a shekarar 1986 ne, aka mai da shi a matsayin mataimakin mai jan ragamar masu aikin fasaha na wannan Jami'a ta ABU. 

A tsakanin shekarar 1989, Alhaji Umaru Ɗanjuma ya yi aiki a matsayin darakta na al'adun jahar Katsina, daga nan sai ya ajiye aikin gwamnati a shekarar 1991. Daga ƙarshe, ya rasu a watan Oktoba shekarar 2021 a Asibitin Gwamnatin Tarraya da ke Katsina bayan shekaru 71 da haihuwa. Ya rasu ya bar mata biyu da yara da dama. (21st Century Chronicle)

Baiwar Umaru Ɗanjuma Katsina

Babu shakka, Umaru Ɗanjuma Katsina yana da baiwa mai tarin yawa, musamman a fagen wasan kwaikwayo, kasancewarsa marubucin wasan kwaikwayo, kuma ɗan dirama, wannan ya ba shi damar rubuta wasannin kwaikwayo na rediyo masu dogon zango da dama, wanda daga bisani aka buga wasu daga ciki. Kaɗan daga cikin rubuce-rubucensa da aka buga, sun haɗa da:

1. Kulɓa Na Ɓarna 1&2

2. Ai Ga Irinta Nan, NNPC, Zariya

3. Baƙin Bature, NNPC, Zariya.

4. The Agony of Justice, NNPC

Alhaji Umaru Ɗanjuma Katsina ya shirya wasannin kwaikwayo da suka haɗa da:

1. Goggo mai Gyaɗa

2. Kishiya

3. 'Ya'yan Zamani

4. Muna Ji Muna Gani

5. Kowa Da Zaninsa

6. Kaico

7. Dattijo-Babawo

Kasancewarsa gwani a ɓangaren wasan kwaikwayo, wannan ya sa ya taka muhimmiyar rawa har a ɓangaren wasan kwaikwayo na Talabijin da finafinai. Ga wasu daga cikinsu:

1. The Second Circle Produced by Prof. Harry Higher

2. Magana Jari Ce

3. Kasagi

 4. Tambari

5. Karambana

6. Queen Amina

7. Ruwan Bagaja

8. Ga fili-Ga -doki

Bayan waɗannan, Alhaji Umaru Ɗanjuma Katsina ya yi wasu shirye-shirye na musamman da kamfanoni masu zaman kansu, kuma ya zama memba a ƙungiyoyi daban -daban, tare da samun lambobin yabo daga kamfanonin shirya finafinai na gida da na waje.

Tsokaci Kan Wasan ‘’Kulɓa Na Ɓarna’’

Wasan dai an gina shi ne a kan wata yarinya mai suna Zaliha wadda take ƙarƙashin kulawar ƙanin mahaifinta mai suna Malam Inuwa da matarsa Mai Nakada bayan rasuwar mahaifinta. A wannan hali ne take zaune a gidan kawunta da nufin zai aurar da ita da zarar ta kammala makarantar Firamare, amma hakan bai yuwu ba, domin ta samu shiga makarantar gaba da Firamare wato sakandare.

Zaliha ta kasance tana da fara'a shi ya sa ma take da samari masu zuwa wajen ta kamar su Ɗanlondon da Ɗantakarda a yayin da ta zo hutu a gidan kawunta Malan Inuwa. Kodayake, shi Ɗantakarda shi ne tsayayye wanda ake tunanin za a haɗa su aure da Zaliha idan ta kammala karatunta. Ɗantakardar nan kuwa yana da mahaifiya mai suna Goggo wacce ba ta amince da soyayyar da take tsakaninsu ba, don ita a tunaninta duk wata yarinya 'yar makarantar boko ba tagari ba ce. A wannan hali ne ake ta tafiya kafin wani Alhajin birni mai suna Alhaji Ruwan Ido da kawalinsa Zumuɗi suka ci karo da Zaliha a hanya, suka shiga neman bayanai game da ita waɗanda suka jiɓinci gidansu da mahaifinta da kuma makarantarsu.

Alhaji Ruwan Ido dai ya yi nasara domin kuwa da Zaliha ta koma makarantarsu ta kwana, Alhaji da Zumuɗi sukan bi ta makarantar, suna ba da cin hanci ga Baba mai gadi don ya ba su izinin shiga don su gana da Zaliha. Da yake wasu matan suna da alamar kwaɗayi a tattare da su, Zaliha dai ta amince da su tare da amsar kuɗi a hannunsu har ta faɗa musu duba da za su yi don sauƙin ganin ta idan Allah ya sa sun ƙara dawowa, domin da za su tafi Alhaji da Zumuɗi sun yi mata alƙawari da cewa za su dawo don su fita, su je su yi mata sayayya a shago.

Zaliha da Alhaji Ruwan Ido suka shiga yin shagali domin kuwa yakan zo ya ɗauke ta daga makaranta ba tare da izini ba, su je gidan shaƙatawarsa. Hakan ya sa idon Zaliha ya buɗe da kuɗi da shagali. Ba a jima ba, ai sai ta aika wa Ɗantakarda wasiƙa da cewa ai kada ma ya ɓata lokacinsa don jiranta, don kuwa ita babu abin da za ta yi da ƙaramin ma'aikaci, ta ƙara mai da cewa, ai ita yanzu ta sami 'yanci ta zama "Indifenda".

Da yake Allah ba azzalumin kowa ba ne, ya bai wa Ɗantakarda wata yarinya mai suna Amarya a matsayin mata, suna zaman jin daɗi da mutunta juna. Bahaushe dai kan ce; ' Komai nisan jifa dai ƙasa zai dawo'. Zaliha dai ta kasance da ciki, aka kuma kore ta daga makaranta, ta dawo gidan Malan Inuwa da matarsa Mai Nakada su kuma suka zama abin tsegumi a wajen al'umma. Shi kuma Alhaji Ruwan Ido da ya aikata wannan ɗanyan aikin ya ƙaryata shi ya yi, har yake barazanar zai kai Malam Inuwa ƙara wajen alƙali. Ganin hankalin iyayenta ya tashi ya sa Zaliha ta gudu daga gida zuwa can wani gari ta haihu, amma yaron ya rasu. Daga nan ne ta ga ba ta iya haɗa ido da Malan Inuwa, sai kawai ta zarce da zaman kanta abinta a gidan Magajiya da sauran mata masu zaman kansu, abokanan lalata irinsu Fulani da ita kanta Magajiyar.

A wannan hali ne Zaliha ta haɗu da Ɗanlondon tsohon saurayinta da Malam Inuwa ke tunanin irin su ne samarin da suke ɓata yara mata. Ɗanlondon ya kasance yana zaune a garin da Zaliha take karuwanci a matsayin malamin tarbiyya da jin daɗin jama'a. Daga ƙarshe dai Ɗanlondon a matsayinsa na malamin tarbiyya ya shiga yi wa Zaliha da sauran abokan aikinta nasiha don su shiryu, su bar wannan karuwanci. Duk suka yi nadama, ya kuma sako Zaliha a gaba ya mai da ita wajen Malam Inuwa, ya kuma nuna buƙatarsa na ganin cewa an ɗaura musa aure da shi da Zaliha. A nan ya yi wa Malam Inuwa habaici da cewa; " Kulɓa na ɓarna ana cewa jaɓa". Wato shi da ake tunanin yana cikin irin samarin nan masu ɓata yara mata sai ga shi, shi ne sanadin shiriyan Zaliha.

 Gudummawar Umaru Ɗanjuma Katsina Wajen Faɗakar Da Al’umma

Yin la’akari da ra’in gudummuwar adabi ga al’umma, wanda ke mayar da hankali kacokan game da rawar da adabi yake takawa a hali na zamantakewa, an duba yadda Umaru Danjuma Katsina wato murubucin wasan kwaikwayo na Kulɓa Na Ɓarna ya yi amfani da adabi don faɗakar da al’umma game da wasu matsaloli da suka kunno kai da nufin samar da mafita. Dangane da muhimman abubuwa da Umaru Danjuma Katsina ya taɓo, sun haɗa da:

·  Alhazan Birni A Wasan "Kulɓa Na Ɓarna"

Watau Umaru Ɗanjuma Katsina, ya yi ƙoƙarin nuna wa al'ummar iri mummunarɗabi'ar nan ta Alhazzan birni na ɓata yara mata 'yan makaranta. Wani abu muhimmi da ya kamata a yi la'akari da shi, shi ne idan ɓera na da sata, to daddawa ma da warinta. A yayin da Alhaji Ruwan Ido da Zumuɗi suka je ganin Zaliha a makaranta, da ta ga kuɗi kuma suka yi mata alƙawarin fita da ita don su je su yi mata sayayya a kanti, ai kuma sai ta ƙara amincewa da su har tana cewa;

Zaliha:"To na ji mutum ba ya cewa ba ya son mutum ko da yaya yake" shf. 35

Da kuma inda take cewa:

Zaliha:"To sai an jima, don Allah idan ka je gidan Kalima ka ce ina gaishe ta, af, idan za ku zo ne goben ku yi ƙoƙari ku bari sai Baturiya ta fita sannan ku yi wa Baba mai gadi magana sai ya buɗe muku ƙofar. Shf.36

Alhaji Ruwan Ido dai mun ga yadda ya yi amfani da kuɗi da dabaru don ganin ya jawo hankalin Zaliha kamar shafi 35 inda yake ce mata:

Alhji:"Ita maganar zuwa wurin iyaye duk ki manta da ita, ni yanzu abin da nake so da ke shi ne ki yarda ki amince da ni. Ɗan'uwan ki ne, kuma ko da ban aure ki ba, ki sani dai duk abin da na kashe maki ba zan tambaye ki ba". Shf 35

Ai da jin haka ya kamata Zaliha ta san inda shi Alhaji Ruwan Ido ya nufa domin kuwa ga dukkan alamu ba da aure ya zo nemanta ba, amma saboda kwaɗayi sai ta amince da wannan yaudara ta Alhaji. Shi kuma da ya ga ya samu shiga ai sai batun zuwa a shaƙata.

·  Cikin Shege

Marubucin ya ci gaba da nuni da illolin da Alhazan birni ke yi wa yara 'yan makaranta ta hanyar nuni da cewa Zaliha ta samu ciki kuma aka koro ta daga makaranta, ta dawo gida, ta zama abin kunya ga iyayenta.

M. Inuwa: Ciki? Haba ba sai in yanka kafira ba.

Mai-Nakada: ‘To, sai dai ka kashe ta. Amman don ciki, ciki ne! ke Zaliha zo duk wannan kuka ki bar shi. Ba yanzu ne lokacin kuka ba, sai an fara yi maki gori. Yamzu ki gaya mana gaskiya’. Shf.59. A bi rubutun nan kal-kalma a yi gyara

A nan, marubucin ya fito da illa mace ta yi cikin shege, wanda ƙyama da horo wajen a kauce wa aukuwar wannan aiki, ya sa har al’umma suke tsangwamar duk wata mace da ta ɗauko cikin shege. Illar ba a nan ta tsaya ba, don takan gangara ta shafi sauran ɓangarorin rayuwa. Marubucin ya yi nuni kan yadda rayuwar Zaliha ta kasance da yadda karatunta ya zo ƙarshe, amma a sanadiyyar cikin da ta yi mata aka kore ta. Wataƙila ta yiwu sanadin wannan karatu da al'umma da iyayenta da kuma ita kanta sun ci moriyar ilimin da ta samu ta hanyar koyar da yara, musamman ma duba da la'akari da ƙarancin yara mata masu ilimin boko.

Da yake shi Alhajin Birni ne ai tuni ya ƙaryata cewa shi ne ya yi mata ciki tare da barazanar zai kai ƙara wajen alƙali don ana so a ɓata masa suna. Watau a taƙaice ya lalata mata rayuwa gaba ɗaya, tun daga neman iliminta har zuwa mutuncinta da martabarta a idon maƙwabta. A Bahaushiyar al'ada, mafi girman abin kunya da mace za ta aikata shi ne ta yi cikin shege, domin ba ta da wata sauran ƙima a idon al'umma don haka ma maganar aure bai taso ba, sai dai ta bar gari ta koma wani gari da ba a san ta ba.

·  Karuwanci Da illa Ga Yara Mata

A sanadiyyar cikin da Alhaji Ruwan Ido ya yi wa Zaliha ne ya sa ta shiga wannan ƙasƙanci na karuwanci, bayan ta gudu ta bar iyayenta, inda a nan ne ta haɗu da tsohon saurayin nan nata (Ɗanlondon), wanda shi ne ya yi ƙoƙarin jan hankalinta tare da nuna mata illar wannan mummunar hanya da ta shiga, wadda ke ƙunshe da haɗura da dama, kuma zai yi wuya a sami nagari da zai amince da auren karuwa. Misali:

Zaliha: To, Ɗanlondon, ni kaina ba da niyyar zaman kaina ma fito ba, Allah dai ya ƙaddara da sai na yi.

Ɗanlondon: Kin gani fa ko ‘ya’ya kika haifa idan sun girma sun sami muƙami ba su da ikon walawa. Ko me suke yi a ce ai wane ɗan banza ne. Yanzu ina daɗin wannan aiki? Kuma yanzu kina nan kina zaman kanki sai ciwo ya kama ki, ke ba ki da wani ɗan’uwa wanda za shi riƙa kula da ke. Ki je ki mutu kuma wurin jana’izarki sai ‘yan daudu da ‘yan iskan gari…’ shf. 67

Da wannan nasihar ce da Ɗanlondon ya yi wa Zaliha ne ya ja ra’ayinta, wanda ya nuna mata illar karuwanci ga ‘ya’yan da za a iya samu da yadda rayuwarsu za ta kasance a nan gaba. Ya lurar da ita kan makoma ta masu karuwaci, sukan yi mummunan ƙarshe da mafi ƙasƙancin mutane a al’umma su suke jagoranci wajen binne shi.

Saƙon Da Ke Tattare Da Wannan Wasa

A wasan Kulɓa Na Ɓarna, Umaru Ɗanjuma Katsina ya yi nuni da illolin da Alhazan birni ke yi wa yara mata, kuma sai ya ƙara nuna cewa waɗanda ake tunanin su ne ke ɓata yara mata su ne matasa, duba da irin shigar da suke yi da askin banza da kuma irin sunaye na hofi da ake kiran su. Idan muka leƙa cikin wasan "Kulɓa Na Ɓarna" ai za mu ga cewa kawun Zaliha wato Malan Inuwa akwai wata rana da ya tarar da ita da Ɗanlondon a ƙofar gida da Zaliha a tsaye ga abin da ya ce:

"…ke kama hanya ki shiga gida kada na ƙara ganin wani ƙato a ƙofar gidan nan, (Zaliha ta shiga gida) kai kuma malan wuce ka tafi, nan ba ƙofar gidan karuwai ba ne. Haka kawai kuke taruwa ku zo kuna sanya yara a muganyar hanya" shf. 8-9

Sai kuma Ɗanlondon ya mayar da jawabi da cewa:

"Allah ya ba ka haƙuri malam, idan ka raba mu a nan ai ba zaka raba mu a makaranta ba, kuma ka san dai komai rashin kunyata ba zan zo gaban gidanka ba, domin in nemi wata hanyar shegantaka da ɗiyarka, ko zan yi ba nan za mu haɗu ba. Manyan ma'aikata da manyan Alhazai su ke ɓata 'ya'yanku ba mu ɗalibai ba. Mu me ke gare mu da za mu ba su ban da cika takarda da wasiƙa. Allah sarki ƘULƁA NA ƁARNA ANA cewa JAƁA, kuma Allah shi ba ka haƙuri. Idan ni ɗa ne ga iyayena ba za ka ƙara gani na a ƙofar gidanka ba". Shf. 9

Wato da wannan magana ta Ɗanlondon marubucin ya isar da saƙon da ke cikin wasan, duk da dai malam Inuwa ya raba su a wannan lokacin ba zai iya raba su ba a makaranta ba, kuma a tunanina duk wanda zai wanki ƙafa zuwa gidan su budurwa to ko ma akwai rashin kunya to kaɗan ne. Idan ka kwatanta haka da halayyar Alhaji Ruwan Ido, da yake da lalata ya neme ta ai bai je gidansu ba gudun kar a gan su tare, kawai sai ya bi ta makaranta inda daga nan ne suka shirya inda za su riƙa haɗuwa. Shi ko Ɗanlondon da aka yi masa kallon ɗan iska shi ne ya zo gidan don ganin ta.

Har ila yau, inda ya ce da Malan Inuwa Alhazai ne suke ɓata 'ya'yanku ba ɗalibai ba, ya ƙara fito da hikimar da ke cikin maganar nan ta Kulɓa na ɓarna ana cewa jaɓa ce. Don ko ta faru da Ɗanlondon wanda yake ɗalibi ne ɗan makaranta ba shi da komai sai takardu, alhali waɗnda ke ɓarnar su ne Alhazawa da ke gefe a manyan ma'aikatu kamar yadda wannan ya yi wa Zaliha. Ya yi mata ɓarna, Ɗanlondon da ake ganin shi ne lalatacce sai ga shi ya taka muhimmiyar rawa wajen ganin Zaliha ta dawo tafarki madaidaici ta hanyar yi mata nasiha da neman aurenta. Lallai Kulɓa ce ke ɓarna, ana cewa jaɓa

Tsokaci Kan Waɗannan Matsaloli A Yau

Ida muka kalli wannan matsala ta masu hannu da shuni, Alhazai da irin illolin da suke wa yara mata 'yan makaranta a yau sai dai du'a’i, domin kuwa idan mutum ya ga irin shaiɗancin da ake yi a manyan makarantu (Jami'o'i) tsakanin Alhazai da 'yan mata abin da ban takaici. Za ka tambayi kan ka, wai Alhazan ne ba su da imani? Ko ba su da yara mata ne? A ɓangaren matan ko, shin rashin tarbiyya ne? Ko sun fi ƙarfin iyayen su ne? Ko iyayen sun san halin da 'ya'yansu suke ciki, amma sakaci ne? Domin babu yadda za a yi iyaye su riƙa ganin abubuwan kuɗi, kamar suturu masu tsada da takalma da jakunkuna masu tsada, amma ba za a iya tuhumar su daga ina suka samo su ba. Ta yiwu wannan ne ya sa matsalar ta yi ta yaɗuwa har zuwa yau. Taɓarɓarewar tarbiyya ne ya kawo mu inda muke a yau, wanda ba mamaki lokacin da Umaru Ɗanjuma Katsina ya rubuta wannan wasa a cikin shekarar1979, al'ummar gaba ɗaya za su ƙyamaci Alhazan nan na ƙauye kuma iyayen na addu'a ga 'ya'yansu a kowane lokaci don neman kariya daga waɗannan miyagun Alhazai na birni. To amma, a yau da Allah ya kawo mu shekarar 2025, wasu iyaye mata har roƙon Allah suke Allah ya haɗa 'ya'yansu da irin waɗannan Alhazai don kwaɗayi da son abin duniya, musamman ma idan aka yi la'akari da irin ci gaban da aka samu a fagen kiwon lafiya ksantuwar zubar da ciki ba komai ba ne mai wahala, kuma idan yarinya ta tashi aure akwai magunguna na gargajiya da ake haɗawa na musamman don 'yarsu ta kasance kamar ba ta taɓa sanin namiji ba.

Kammalawa

 Marubuta wasan kwaikwayo ko shakka babu suna amfani da fasaharsu wajen ganin al’’umma sun kuɓuta daga wasu matsaloli da kan iya kunno kai a cikin al’umma. Umaru Danjuma Katsina dai ya taka rawar gani a wannan fage musamman idan aka yi la’akari da wasanni daban-daban da ya rubuta ciki har da wasan kwaikwayo na Kulɓa Na Ɓarna. Matsalar ɓata rayuwar mata ‘yan makaranta da Alhazai na birni ke yi kamar yadda Umaru Danjuma Katsina ya nuna a wasan kwaikwayon Kulba Na Barna ya ci gaba da aukuwa don kuwa idan aka ga yadda manyan motoci ke shiga da fita a manyan makarantu kamar jami’o’i domin kwasan ‘yanmata domin lalata da su saboda kuɗi da wasu abubuwa ƙyalƙyali kamar wayar hannu da makamantarsu.

Manazarta

Ahmad, U.B. (1985): “Nau’o’in Wasannin Kwaikwayon Hausawa, Cibiyar Nazarin Al’adun Nijeriya, Zariya: Jami’ar Ahmadu Bello.

Ahmad, U.B. (1985): Taɗonomy Of Hausa Drama, Zaria: ABU Press Limited

Ɗangambo, A. (1984): Rabe-Raben Adabin Hausa Da Muhimmancinsa Ga Rayuwar Hausawa. Kano: Triumph. https://21stCenturychronicle.com

Katsina, U. D, (1979), " Kulɓa Na Ɓarna". Zariya: N.N.P.C

Malumfashi, A. I. (1985): “Asali Da Bunƙasar Rubutaccen wasan Kwaikwayo Na Hausa” Kundin Digiri Na Biyu, Sashen Nazarin Harsunsn Nijeriya Da Na Afrika, Zariya: Jami’ar Ahmadu Bello.

Malumfashi, I.A.M. (1990): “Madubi Ɗaya Fuska Biyu: Nazari Da Sharhi Kan Rubutattun Wasannin Kwaikwayon Hausa”. Takardar da aka gabatar a Sashen Nazarin Harsunan Nijeriya, Sakkwato: Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo.

Price, A. (1913) The Theartre of Promiscuity: Comparatiɓe Study of the Dramatic mWritings of Wole Soyinka and Howard Baker; Ph.D Thesis, School of English. USA: Uniɓersity of Leeds

Sulaiman, I.A (2007): “Raha A Wasannin Ƙasimu Yero: Tarken Wasannin Karambana” Kundin Digiri na Biyu, Sashen Nazarin Harsunan Nijeriya Da Na Afrika, Zariya: Jami’ar Ahmadu Bello.

Sulaiman, I.A. (2013): “Jirwaye Mai Kamar Wanka: Waiwayen Rabe-Raben Wasan Kwaikwayon Hausa” Maƙala a cikin Himma, Mijallar Nazarin Hausa, Juzu’I Na Huɗu, Fitowa ta Ɗaya, Sashen Nazarin Harsunan Nijeriya, Katsina: Jami’ar Ummaru Musa `Yar’aduwa.

Umar, M.B. (1987): Dangantakar Adabin Baka da Al’adun Gargajiya,

Xiameng, S. (2013): Rubutaccen Wasan Kwaikwayo A Rukunan Adabin Hausa: Haɓakarsa Da Muhimmancinsa. Kano: Gidan Dabino Publishers.

Yahaya I.Y da wasu, (2003): Darussan Hausa Don Manyan Makarantun Sakandare Na 1, Ibadan: Uniɓersity Press.

Yahaya, I.Y. da wasu (1983): Jagoran Nazarin Hausa. Zaria: Northern Nigerian Publishing Company (NNPC).

Yahaya, I.Y. (1988): Hausa A Rubuce: Tarihin Rubuce-Rubuce Cikin Hausa. Zaria: Northern Nigerian Publishing Company (NNPC).

`Yar’aduwa, T.M. (2005) “Nazarin Littafin Kulɓa Na Ɓarna Na Ummaru Ɗanjuma Katsina” a cikin FAIS Journal Of Humanities,

`Yar’aduwa, da wasu (2007): Darussan Hausa Don Manyan Makarantun Sakadare Na 3. Ibadan: Univesity Press.

`Yar’aduwa, T.M. (2007): Wasan Kwaikwayon Hausa: Nau’o’insa da Sigoginsa, Kano: Benchmark Publishers Limited.

 Dundaye Journal

Post a Comment

0 Comments