Ticker

6/recent/ticker-posts

Gargadi a Cikin Wakar Arewa Jamhuriya Ko Mulukiya: Madogara Daga Wasu Nassoshin Addinin Musulunci

Citation: Ayagi, J. S., Musa, I. I. and Ɗayyabu, A. (2025). “Gargaɗi a cikin Waƙar Arewa Jamhuriya ko Mulukiya: Madogara daga wasu Nassoshin Addinin Musulunci.” in Ɗunɗaye Journal of Hausa Studies, Vol. 03, No. 02, Pp. 144 – 151. www.doi.org/10.36349/djhs.2025.v03i02.018.

GARGAƊI A CIKIN WAƘAR AREWA JAMHURIYA KO MULUKIYA: MADOGARA DAGA WASU NASSOSHIN ADDININ MUSULUNCI

Na

Jibrin Sani Ayagi

Da

Rabi’u Musa Kwamkwaso College of Advanced and Remedial Studies Kano

Department of Linguistics and Nigerian Languages, Alvan Ikoku Fed.University of Edu., Owerri, Imo State

Da

Idris Ibrahim Musa 2 and Abubakar Ɗayyabu 1

Rabi’u Musa Kwamkwaso College of Advanced and Remedial Studies Kano

Tsakure:

Wannan takarda mai taken Gargaɗi a cikin waƙar Arewa Jamhuriyya ko Mulukiyya: Madogara daga wasu Nassoshin Addinin Musulunci, ta yi bayani ne a kan irin dangantakar da take tsakanin tsoratarwa da hani da addini ya yi a kan aikata munanan ɗabiu, da faɗakarwar da jan kunne da marubucin waƙar ya yi wa Hausawa na yankin Arewacin Najeriya a kan wasu ɗabiu marasa kyau da suke aikatawa. Daga cikin munanan ɗabiun da binciken ya gano akwai rashin mai da hankali wajen neman ilimi da taɓarɓarewar tarbiya da kawalci da almubazzaranci da gulma da hassada da baƙin ciki da cin amana da camfi da ƙarya da roƙo da fariya da sauransu. Binciken ya gano cewa tabbas akwai dangantaka mai ƙarfi dangane da shawarar da marubucin waƙar ya ba wa ‘yan arewa a kan wasu ayyuka marasa kyau da suke aikatawa da kuma hani da tsoratarwar da Al’ƙur’ani da Hadisai suka yi a kan aikata aiyuka marasa kyau. Wannan waƙa da aka nazarta an same ta ne a cikin littafin marubucin da ya kira “Waƙoƙin Sa’adu Zungur” (1968) littafi ne da yake ƙunshe da waƙoƙi ciki har da ita wannar waƙar. sannan aka sake rubuta ta domin yin wannan bincike. Haka kuma an karanta ta da yawa domin ƙara fahimtar komai. An yi amfani da Ra’in fanɗarewa daga karɓaɓɓun Aladun Aumma (Deviance theory) aka ɗora takardar a kansa. Rain yana bayani ne a kan yanayi na fanɗarewa daga aladar da alumma ta saba da ita. Mutum na iya fanɗarewa ta hanyar ƙin aikata wasu al’adu ko wuce gona da iri a wajen aikata al’adu ko ma aikata al’adun da ba su yi daidai da dokokin da al’ummar da yake ciki ba. (Otite and Ogionwo 1981:217). 

Gabatarwa

Wannan muƙalar tana bayani ne a kan rubutacciyar waƙar Hausa wadda Malam Ahmad Mahmud Sa’adu Zungur ya wallafa. Masana da dama sun bayyana ma’anar rubutacciyyar waƙar Hausa a cikin nazari kamar Ɗangambo (2007:6) yana cewa “Rubutacciyar waƙa na nufin “wani saƙo da aka gina shi kan tsararraiyar ƙa’ida ta baiti, ɗango, rerawa, kari (bahari), amsa amo da sauran ƙa’idojin da suka shafi daidaita kalmomi, zaɓensu da amfani da su cikin sigogin da ba lallai ne haka suke a maganar baka ba. Bayan haka, an duba wasu nazarce-nazarcen masana da manazarta a kan rubutattun waƙoƙin Hausa na mabambantan marubuta da dama ta sigogi daban-daban. Bello (2002:276) ya nazarci rubutattun waƙoƙin Hausa ta hanyar fito da tasirin da harshen Larabci ya yi a kan rubutattun waƙoƙin Hausa. Shi ma Umar (2002:165) ya nazarci rubutacciyar waƙar Malam Aliyu Namangi inda ya nazarci kwalliya da ma’ana tare da saƙon da ke cikin waƙoƙinsa da suka shafi addini. Har ila yau Aliyu (2011:113) ya yi nazari a kan manufar waƙa a siyasa. A nasa binciken ya nuna yadda rubutatun waƙoƙin siyasa suka haifar da ire-iren jigogi mabambanta a cikin waƙoƙin siyasa na Hausa. Haka kuma Hussaini (2024:299) ya nazarci rubutattun waƙoƙin Hausa a inda ya nazarci salon amfani da nassi a rubutattun waƙoƙin Hausa misalai daga wasu waƙoƙin gwagwarmaya. Wannan ne ya bayar da damar yin wannan binciken, ganin yadda masana da manazarta suke ta nazarin rubutattun waƙoƙin Hausa, amma ba a samu wani nazari wanda ya bibiyi waƙar ‘Arewa Jamhuriya ko Mulukiya ta Malam Sa’adu Zungur ya fito da irin dangantakar da ke tsakanin al’adun Hausawa da na addinin Musulunci da ya sarrafa a ƙananan manufofin cikin waƙar, ta hanyar bincike na ilimi domin daɗa fito da saƙonnin cikin waƙar a fili ba. Shi ya sa ake son cike wannan giɓin da daɗa samar da abin da bitar bicike ba ta samar ba, da kuma daɗa tabbatar da zalaƙar mawaƙin ta hanyar binciken ilimi.

Taƙaitaccen Tarihin Malam Sa’adu Zungur

An haifi Malam Ahmad Mahmud Sa’adu Zungur a cikin garin Bauchi a cikin shekara ta 1914. Ya yi karatun Muhammadiyya. da na littattafai a garin nasu. Ya yi karatunsa na Firamare a garin Bauchi/ Bayan nan, ya halarci makarantar kwaleji ta Yaba da ke garin Legas a shekara ta 1934. Ya zama Malami a wata makaranta a garin Zariya, bayan ya dawo daga garin Legas. Ya kafa wata ƙungiya mai suna Zariya friendly society tare da Malam Abubakar Imam da wasu abokansa na wancan lokacin. Wannan ƙungiyar da suka kafa, daga baya ta zama kamar ƙungiyar siyasa a yankin. Ta sha suka daga wajen wasu sarakunan lokacin. (Ahmad 1968:2).

A shekara ta 1942, ya sake dawowa garin Bauchi inda ya cigaba da harkar karantarwa. Bayan haɗuwa da suka yi da Malam Aminu Kano da Muhammad Baba Halla na yin gwagwarmaya na yadda ake mulkin a yankin Arewa na wancan lokacin, Malam Saadu Zungur Ya kasance sakatare na jamiyyar NCNC a shekara ta 1948. Ya yi rubuce-rubuce da dama a fannin adabin Hausa. Wasu daga cikin waƙoƙin da ya rubuta sun haɗa da waƙar Maraba Da Soja da Waƙar Bidi’a da Waƙar ‘Yan baka da ita wannan waƙar da ake nazari, wato Arewa JUmhuriya Ko Mulukiya da sauransu. Ya kasance abin koyi ga marubuta adabin Hausa kamar irinsu Malam Abubakar Ladan Zariya da sauran marubuta. Ya rasu a shekara ta 1958 a cikin garin Bauchi. (Ahmad: 1968:2).

Wannan waƙa da aka nazarta an same ta ne a cikin littafin marubucin da ya kira “Waƙoƙin Sa’adu Zungur” (1963). Littafi ne da yake ƙunshe da waƙoƙi guda huɗu ciki har da ita wannar waƙar, sai aka sake rubuta ta domin yin wannan bincike. Haka kuma an karanta ta da yawa domin ƙara fahimtar komai.

Babban jigon wannan waƙa shi ne faɗakarwa a kan kaucewa da daina wasu munanan ɗabiu da mutanen Arewa suke aikatawa da kuma yi musu gargaɗi a kan makomar yankin kamar yadda marubucin ya tabbatar a wannan baitin:

Matuƙar yaranmu suna bara,

Allah ba ku mu samu abin miya.

A gidan birni da na ƙauyuka,

Da cikin makarantun tsangaya.

 Sun yafu da fatar bunsuru,

 Babu shakka sai mun sha wuya.

Wannan ya tabbatar gaba ɗayan manufar da ya gina waƙar a kanta dai shi ne faɗakarwa da yin gargaɗi a kan makomar yankin Arewa. Marubucin ya yi amfani da wasu ƙananan manufofi da dama waɗanda kuma su ne suka haɗu suka tabbatar da jigon waƙar.

Addinin Musulunci, kasancewarsa addinin gaskiya, ya shiga saƙo da lungu cikin al’adu da ɗabiun alummar Hausawa. Ba kasafai ake iya rarrabe da yawa daga cikin aladu da ɗabiun Hausawa da na addinin ba. Marubucin a cikin waƙar ya faɗakar, ya kuma tsawatar da yan arewa a kan wasu munanan ɗabiu da suke aikatawa, da su nutsu, su daina tun kafin yankin nasu ya lalace. A sabo da haka ne, ya ƙarfafi wannan magana da marubucin ya yi a kan al’ummar Arewa ta hanyar hani da tsawatarwa. Wannan takarda ta yi bayani ne a kan irin dangantakar da ke tsakanin tsoratarwa da hani da addini ya yi a kan aikata munanan ɗabiu, sannan da faɗakarwar da jan kunne da marubucin waƙar ya yi wa ‘yan Arewa a kan wasu ɗabiu marasa kyau da suke aikatawa. .

Dangantakar Al’adun Hausawa da na Addini a cikin waƙar Arewa Jamhuriyya ko Mulukiyya

-Dangantaka na nufin “’yan uwantaka” (CNHN: 2006:95).

-Ɗabi’a na nufin ‘halim mutum ko al’adarsa’ (CNHN: 2006:116).

Gargaɗi shi ne kashedi ko horo (CNHN: 2006:159).

-Faɗakarwa ita ce zaburar da faɗakar da a sa mutum ya fahimta, a sanya mutum ya gano wani abu na haƙiƙa wanda aka rigaya aka mance (Bargery 1934:288).

Kamar yadda maubucin ya bayyana cewa ‘yan Arewa ya kamata su farka ganin irin matsalolin da ke tattare da yankin , shi ne ya gargaɗe su da su shiga taitayinsu, domin su daina. Wannan gargaɗi da faɗakarwa da marubucin ya yi, sai ya yi daidai da tsoratarwa da hani da addinin Musulunci ya yi a kan aikata munanan ayyuka. Kusan dukkan matsalolin da marubucin ya bayyana a cikin waƙar tun a wancan lokacin game da ‘yan Arewa, yana kusan daidai da halin da yankin ya tsinci kansa a ciki a yau. Matsalolin da malamin ya kawo sun haɗa da jahilci da karuwanci da bara da cin amana. Misali ya yi Magana a kan halin ko in kula na rashin neman ilimi da yan arewa ba sa yi da rashin nuna hikima wajen zamantakewar rayuwa da kuma riƙon sakainar kashi da suke yi wa addinin musulunci. Wannan ya sa abokanan zaman mu ‘yan kudu, suke yi mana kallon wawaye.

Jahilci

Jahilci shi ne rashin sani ko kuma rashin iya karatu da rubutu (CNHN 2006:211)

Akwai wasu karin maganar Hausawa da suka yi nuni a kan illolin jahilci domin a zaburar da jama’a su shiga neman ilimi, su kuma yaƙi jahilcin. Misali, jailci ya fi hauka wuyar magani da kuma wanda ake cewa ƙaramin sani ƙuƙumi, sai kuma mai nuna fa’idar ilimi da yake cewa, ilimi, gishirin zaman duniya. Malam Sa’adu Zungur ya yi amfani da hikimarsa ya faɗakarda alummar Arewa kan illolin jahilci a cikin wasu baitukan waƙarsa kamar haka:

4. Jahilci ya ci lakarmu duk,

Ya sa mana sarƙa har wuya.

5. Ya sa mana ankwa hannuwa,

Ya ɗaure ƙafarmu da tsarkiya.

 6. Bakunanmu ya sa takukumi,

Ba zalaƙa sai sharholiya.

7. Ya Allah kai mana agaji,

Don mu kauce kunyar duniya.

8. Ilimi mai amfani duka,

Inda addinmu ya rataya.

9. In fa addinmu ya raunana,

Babu alheri nan duniya.

10. Mu dai ilimi muka tambaya,

Ko a London ko a Arabiya.

Addinin musulunci, ya kwaɗaitar a kan neman ilimi da kuma yaƙar jahilci. Misali Allah ya ce “Ka ce shin waɗanda suke da ilimi da waɗanda ba su da ilimi za su kasance daidai ?” (Alƙur’ani 39:9) (Muhammad 2021:231)

Sannan Annabi (SAW) ya ce “Neman ilimi wajibi ne ga kowane Musulmi” Ibn Majah, Hadisi na 224

A wani hadisin Annabi (SAW) ya ce “ Duk wanda ya bi hanya domin neman ilimi, Allah zai sauƙaƙa masa hanya zuwa Aljanna” ( Muslim Hadisi na 2699).

Idan aka yi la’akari da waɗannan nassoshi sun nuna abin da Malam Saadu Zungur ya yi gargaɗi kansa, daidai yake da yadda addinin Musulunci ya nuna. Ba a son Musulmi ya zauna da jahilci domin zai iya auka kansa cikin fitina mai girma kamar yadda yau yankin Areawa yake ciki.

Karuwanci

Karuwanci shi ne zaman mace maras miji da saduwa da maza don neman kuɗi (CNHN 2006:236). Karuwanci yana ɗaya daga cikin muhimman matsalolin da Saadu Zungur ya gargaɗi alummar Arewa a kansa. Karuwanci yake haifar da samuwar wani rukuni na mutane marasa kunya a cikin gari kamar ɗan daudu da magajiya da samari masu ruwan kuɗi da maroƙa da gidajen barasa. Idan waɗannan abubuwa suna cikin Arewa, babu shakka ɓacin rai da damuwa ba zai bar mu ba, sannan zancen jagoranci ƙasa, sai dai mu ga ana yi. Ga abin da Malam Sa’adu yake cewa a cikin waɗannan baitoci:

11.Matuƙar arewa da karuwai,

Wallahi za mu ji kunyar duniya.

12. Matuƙar ‘yan iska na gari,

Ɗan daudu da shi da magajiya.

13. Da samari masu ruwan kuɗi,

Ga maroƙa can a gidan giya.

14. Babu shakka ‘yan kudu za su hau,

Dokin mulkin Najeriya.

A shekarun baya da suka wuce, karuwai ba mutanen gari ba ne, baƙi ne suke zuwa, su kama wuri a sabon gari, wato inda ƙabilu baƙi suke zaune, can waɗanda suke lalata da su suke zuwa. Yanzu lamarin sai ya canza salo, ya zama yayan gari daga gidajen iyayensu, suke zuwa wurare daban-daban ake yin lalata da su, kuma su dawo gidajen iyayen nasu, a wasu lokutan ma da sanin iyayen nasu.

Akwai ayoyin Alƙur’ani da hadisan Annabi (SAW) masu yawa da suka yi tir da al’amarin zina. An yi hani Musulmi ko namiji ko mace da kada ya kusantar zina. Allah ya ce “kuma kada ku kusanci zina. Lallai ne ita ta kasance alfasha ce kuma ta munana ga zama hanya” Sura isra’I aya 32. Annabi SAW yana cewa “ Mazinaci ba zai yi zina ba a lokacin da yake mumini ba….Muslim ne ya rawaito. Hadisi na 2342.

A yau tare da dukkan nassoshin Alƙur’ani da hadisai na Annabi (SAW), ‘yan iska sun yi yawa a yankin Arewa. Wannan ba ya rasa nasaba da sakacin iyaye na halin ko in kula a kan ‘ya’yansu da sakacin hukumomin Arewa da sauran al’umma baki ɗaya. Sanadiyar haka, a Arewa aka sami yara matasa masu yawa masu ƙwacen waya da garkuwa da mutane da shaye-shaye da harkar daba da sace-sace wanda hakan ya janyo rasa rayuka da dama da koma baya ga yankunan Arewa. Annabi (SAW) yana cewa “Dukkaninku masu kiwo ne kuma kowa sai an tambaye ku abin da aka ba ku kiwo” Muslim ne ya rawaito Sahih Muslim. Hadisi na 2134

Kawalci ya zama ruwan dare game duniya a ma fi yawan yankuna na Arewa. Kawali shi ne mutumin da yake haɗa mace da namiji ko namiji da namiji don su yi aikin assha. (CNHN 2006:241) yan siyasa da masu kuɗi da masu riƙe da madafun iko, suna amfani da kawalai su kawo musu yara maza da mata su lalata, wanda wannan shi ma naƙasu ne ga yankin Arewa. Allah yana cewa “ Ku yi temakekeniya wajen aikin alhairi da kuma aikin tsoran Allah, kada ku yi taimakekeniya a cikin aikin saɓo da kuma aikin ƙetare iyaka” Ma’ida: Aya ta 2. Annabi (SAW) yana cewa “Wanda yake nuni a kan aikin alhairi kamar ya aikata ne haka wanda yake nuni ga aikin sharri shi ma wannan kamar ya aikata ne” Tirmizi Sunan Tirmizi, hadisi na 34.

Daga nan, sai magana a kan almubazzaranci wato ɓarnar dukiya (CNHN 2006:15) Mafi yawan masu hannu da shunin yankin Arewa ba su cika yin taimako ta hanyar samar da abin yi ga masu rauni da talakawa da yara da suka kammala karatu ko ɗaukar nauyin su yi karatu ko taimakon yan uwa da sauransu. Baya ga haka, a wasu lokutan, sukan yi abin da ba shi da muhimmanci sosai domin neman suna ko neman burgewa. Hakan ya sa ɓarna da matsaloli sun yi yawa a yankin. Allah yana cewa a cikin suratul IsraI “kada ka yi almubazzaranci, lallai masu almubazzaranci sun kasance ‘yan uwan shaiɗan ne Aya ta 26

Annabi SAW ya yi hani a kan almubazzaranci ko da yana gaban ƙorama ne mai gudana to kada ya yi almubazzaranci” Buhari, hadisi na 2345

Ga matsalar roƙo wanda yake nufin neman kyauta daga wani (CNHN 2006:374) Yankin Arewa, kusan ya fi na ko’ina yankin ƙasar Nijeriya matsalar roƙo. Roƙo a al’ummar Arewa ta zama ruwan dare da ya game duniya. Manya da yara, maza da kuma mata. Wannan abu ya sa wasu mutane da yawa zuciyarsu ta mutu, sun rasa wadatar zuci da tawakkali. A Masallaci roƙo, a kasuwa roƙo, a kan hanya roƙo ba ga yara ba, ba kuma ga manya ba. Wannan kaɗai ta isa ta zama babbar masifar da Arewa za ta shiga halin ni ya su. Annabi SAW yana cewa “Dayanku ba zai gushe ba yana roƙo, har sai ya gamu da Allah Maɗaukakin Sarki babu gutsiran nama a fuskarsa” Buhari da Muslim suka rawaito. Sahih Muslim, hadisi na 275

Bara

Bara na nufin neman sadaka daga wurin mutane (CNHN 2006:37. Bara na ɗaya daga cikin manyan matsalolin da suka dabaibaye yankin Arewa. Wasu daga cikin mutanen Arewa sun mayar da bara wani abu na addini wanda ya sa suke tura yaransu ƙanana zuwa wasu garuruwa da sunan karatu ba tare da guzuri ba. Waɗannan yara sai ya zama sukan ware da bara gida-gida, wasu kuma su tsinci kansu a sace-sace da sauran miyagun ayyuka. Haka kuma bara ya haddasa faruwar wasu matsaloli a cikin yankin Arewa da suka haɗa da yawaitar masakai da malaman duba da tsafi da camfe-camfe da alfahari da girman kai da ƙarya da kuma rashin sada zumunci a tsakanin ‘yan uwa da maƙota. Malam Zungur ya ambaci waɗannan matsaloli kamar haka::

1. Matuƙar yaranmu suna bara,

Allah ba ku mu samu abin miya.

2. A gidan birni da na ƙauyuka,

Da cikin makarantun tsangaya.

3. Sun yafu da fatar bunsuru,

Babu shakka sai mun sha wuya.

4. Matuƙar da masakai barkatai,

Da makaho ko da makauniya.

5. Birni ƙauye da garuruwa,

Duk suna yawo Najeriya.

6. Kai bahaushe ba shi da zuciya,

Za ya sha kunya nan duniya.

7. In ko in kudu sun ka hau,

Babu sauran daɗi daɗa kowa zai sha wuya.

Bara ita ce neman sadaka daga wurin mutane (CNHN: 2006:37) A nan marubucin yana so ya bayyana illar tura yara da iyaye suke yi da sunan karatu daga ƙarshe su yaran su ɓuge da yin barace-barace da sauran abubuwa na ƙasƙanci a wuraren da aka tura su karatun. Wannan nau’i na bara ya canza salo, ma fi ya yawan makafi da guragu ko kutare da suke yankin Arewa zuciyoyisu sun mutu. Nakasa ba ta kai a yi bara basai su fara, Mata tsofaffi daga karkara su ma bara daga nan har kudancin ƙasar, wani lokacin a kan yi amfani da su wajen tsafi ko kuma a kashe su idan rigimar ƙabilanci ta ɓarke ko wasu dalilai mabambamta. Haka kuma, a cikin alummar mu da yawa daga cikinmu zuciaya ta mutu, za ka ga mutum da ƙarfinsa amma yana bara a masallatai da kasuwanni da wuraren shaƙatawa da sauransu, tabbas ba ƙaramin ƙasƙanci ba ne ga yankin mu arewa ba, Musulunci ya tsawatar a kan illar yin bara, Misali Annabi SAW yana cewa “Ya fi kyau ga mutum ya saɓi gatari, ya hau kan dutse ya yi wo itace, ya ɗauka ya sayar, da ya tsaya wajen mutane ya roƙe su sun bashi ko sun hana shi.Muslim (1425/2004: 1042) Babin ƙin roƙon Mutane.A wani hadisin yana cewa” ɗayanku ba zai gushe ba yana roƙo, har sai ya gamu da Allah maɗaukakin sarki babu gutsiran nama a fuskarsa.Buhari da Muslim suka rawaito

Wata matsalar kuma ita ce ta yawaitai malaman duba a yankin na Arewa, ya yi sanadiyar ko ya haifar da tsafe-tsafe da camfe-camfe a yankin, shi ma wannan babbar matsala ce a yankin, musammaan wajen rashin dogaro da Allah. Hadisin Anas Annabi SAW yana cewa” Babu kamuwa da cuta, haka nan babu camfi a cikin musulunci. Wato wani ya shafawa wani cuta. Kakkyawar fata yana ƙayatar da ni. Sai sahabbai suka tambaya menene kyakkkyawan fata? Sai ya ce kyakkyawar Magana” Buhari da Muslumu suka rawaito. A wani hadisin Annabi SAW yana cewa” ku kiyayi abubuwa guda bakwai masu hallakarwa. Sai sahabbabi suka tambayi Annabi ko menesu? Sai ya ce Na farko shirka da Allah, da kuma tsafi da kashe ran da Allah ya haramta a kashe ta da cin riba da cin dukiyar maraya da juya baya a ranar gumurzu da yi wa mumina katangaggiya rafkananniya daga aikata alfasha yi mata ƙazafi. Buhari da Muslumi suka rawaito hadisi na 3452

Dangane da malamin duba kuwa, Annabi SAW ya ce “Duk wanda ya je wajen malamin duba kuma ya gasgata shi a kan abin da yake faɗa, haƙiƙa ya kaficewa abin da aka saukarwa Annabi Muhammad. Muslumu ne ya rawaito (Sahih Muslim:342)

Rashin Zumunta

Zumnta tana nufin kyakkyawar dangantaka ta jinni ko ta aure ko kuma ta abota tsakanin mutum da mutum (CNHN 2006:496). Zumunta na ɗaya daga cikin muhimman abubuwa da ba a son mutane su yanke. Zumunta a ƙafa take in ji Bahaushe. A al’ummar Hausawa ana son mutane su riƙa ziyartar juna, suna duba lafiyar junansu. Haka kuma, zumunta tana ƙara danƙon so da ƙauna da tausaya wa juna. Idan mutane suka daina ziyartar junansu domin zumnuci, suka yanke ta, al’amurransu za su lalace, ƙiyayya ta ƙaru tsakaninsu. Malam Sa’adu Zungur ya gargaɗi alummar Arewa kan sakaci da suka yi suka kashe zumunta da take tsakaninsu. Ga abin da yake cewa da kuma abin da hakan ya haddasa 

1. Arewa zumunta ta mutu,

Sai nishaɗi sai sharholiya.

2. Sai alfahari da yawan kwafe,

Girman kai sai ƙwambom tsiya.

3. Camfe-camfe da tsubace-tsubbace,

Malaman ƙarya ‘yan damfara.

Sai ƙarya sai kwambon tsiya, Sai hula mai annakiyada.Matsalar rashin sada zumunci a tsakanin ‘yan uwa da maƙota, ya zama ruwan dare a cikin al’ummar Arewa, abin da ya haifar da rashin tausayi da taimakon junaAnnabi (SAW) yana cewa” Duk wanda yake so a yalwata masa a cikin arzikinsa, a jinkirta masa a cikin gurbinsa, ya sadar da zumuncinsa. Buhari da Muslim. Buhari: 2211

Wasu matsaloli da suke tare da rashin sada zumunta su ne alfahari da girman kai da kuma ƙarya kamar yadda marubucin ya bayyana a cikin waƙar. Dukkan waɗannan abubuwa da aka ambata, Musulunci ya tsawatar da waɗanda suke aikata su. Misali, Annabi (SAW) yana cewa “Abubuwa guda huɗu duk wanda ya kasance a cikinsu, to tabbas ya kasance tataccen munafiki. Wanda kuma yake da wata ɗabia daga cikinsu, ya kasance yana da wata ɗabia ta munafunci. Na farko idan ya yi zance sai ya yi ƙarya, idan aka amince masa sai ya yi ha’inci, idan ya yi alƙawari sai ya yi yaudara, idan aka yi husuma da shi, sai ya yi fajirci. Bauhari da Muslim ne suka rawaito. (Sahih Buhari: 3452).

Dangane da girman kai kuwa, Annabi SAW yana cewa” Duk wanda ya kasance a zuciyarsa akwai misalin ƙwayar zarra na girman kai, ba zai shiga Ajanna ba. Sai wani mutun yake cewa, ya Rasulillahi aiko mutum yakan so tufafinsa mai kyau da takalminsa ma mai kyau, sai Annabi ya ce Allah kyakkyawa ne, kuma yana son abu mai kyau. Girman kai shi ne ƙin gaskiya da raina mutane” Buhari da Muslim. (Sahih Buhari : 2312)

Cin Amana

Cin amana a wannan takarda yana nufin ka yarda da mutum ta hanyar ba shi ko faɗa masa wani abu na sirri, amma ya karya. Cin amana abu ne mai muni a zamantakewar jamaa, kuma mai haddasa rashin jituwa da naƙasa cigaban ƙasa. Malam Sa’adu Zungur domin ya ƙara fito da jigonsa na faɗakarwa da gargaɗi ga aikata munanan aiyuka da yan Arewa suke aikatawa, ya ƙara fito da mummunan ɗabiar nan ta cin amana abin da yake haddasa ayyukan riya da ƙarya da yawan rantse-rantse da zalunci da zamba da kuma gulma. Misali kamar yadda ya ambata a cikin waƙarsa:

1. Cin amana kuma da yawan riya, 

Ga hula mai anakiya.

2. Babu mai aiki bisa hankali,

Da basira don ya ga gaskiya.

3. Rantse-rantse da Allah yai yawa,

Ga ƙarya ga zambar tsiya.

4. Sai kinibibi sai kwarmato,

Ga gulma da son ƙullalliya.

Tun a wancan lokacin, cin amana ya zama ruwan dare a tsakanini al’ummar yankin Arewa, wannan ne ya sa marubucin yake gargaɗinsu da su daina saboda ba ɗabia ce mai kyau ba. Annabi SAW yana cewa “Alamomin munafukai uku ne idan ya yi zance sai ya yi ƙarya, idan ya yi alƙawari sai ya saɓa, idan aka amince masa sai ya yi ha’inci” Buhari da Muslimu ne suka rawaito. Buhari:1234. A wani hadisin Annabi SAW yana cewa “Dukkaninku masu kiyo ne kuma kowa sai an tambaye shi abin da aka ba shi kiwo” Buhari da Muslim. Buhari:354.

Haka kuma, cin amana tana haifar da riya wato yin abu ba domin Allah ba, sai domin a yabi mutum. Annabi (SAW) yana cewa” Ma fi tsoron abin da na ke jin tsoro ga al’ummata shi ne ƙaramar shirka. Sahabbai suka ce mene ƙaramar shirka ya Rasulilla? Sai Annabi yace riya” Imam Ahmad da Imam Tirmizi suka rawaito. Littafin Tirmizi 234

Bayan wannan kuma sai yawan rantse-rantse da babu gaira, babu dalili da kuma yawan ƙarya a kowane lokaci. Allah ya ce “Kada ka bi dukkan mai yawan rantsuwa, wulaƙantacce” (Suratul Ƙalam aya ta 10). Annabi (SAW) yana cewa “ Mutum uku Allah ba zai magana da su ba ranar ƙiyama, ba zai kalle su ba kuma ba zai tsarkake su ba kuma suna da azaba mai raɗaɗi. Annabi SAW ya maimaita haka sau uku, Sai Abu Zarril Gifari ya ce su wanene waɗannan ya Rasulillahi? Sai Annabii SAW ya ce mai jan tufafinsa a ƙasa da mai yin gori da kuma mai ɗaga farashin kadararsa ta hanyar rantse-rantse. Muslim da Tirmizi da NisaI sun rwaito wannan hadisi. Muslim:432.

Baya ga haka da yawa daga cikin mutanen Arewa, sun lalace wajen yin ha’inci da zamba da zalunci. Annabi (SAW) yana cewa” Duk wanda yake mana zamba to ba ya daga cikinmu” Muslimu ne ya rawaito. Muslim:233

Sannan, ya yi musu gargaɗi wajen haɗa husuma a tsakanin alummaa. Babu mai son haɗa rigima saboda son zuciya, sai shaiɗani A wani hadisin yana cewa

Ku kiyayi son kanku, domin shi ne ya halakar da waɗanda suka zo gabaninku . Muslim ne rawaito (Muslim : 2984) Babin haramcin zalunci.

Kammalawa

Daga ƙarshe babban jigon wannan waƙa mai suna ‘Arewa Jumhuriyya ko Mulukiyya ta Sa’adu Zungur shi ne faɗakarwa. Takardar ta yi tsokaci ne a kan irin dangantakar da ke tsakanin tsoratarwa da hani da addini ya yi a kan aikata munanan ɗabiu, da faɗakarwar da jan kunne da marubucin waƙar ya yi wa Hausawa na yankin Arewacin Najeriya a kan wasu ɗabiu marasa kyau da suke aikatawa. Daga cikin munanan ɗabiun da binciken ya gano akwai rashin mai da hankali wajen neman ilimi da taɓarɓarewar tarbiya da kawalci da almubazzaranci da gulma da hassada da baƙin ciki da cin amana da camfi da ƙarya da roƙo da fariya da sauransu. Wannan dalili ne ya sa marubucin waƙar ya faɗakar da yan Arewa tare da jan kunne ta lisssafo irin illolin da suke tattare cikin halin da suka tsinci kansu tun a wancan lokacin, wato kamar ma dai a wannan lokacin ya wallafa waƙar

Manazarta

Abdulƙadir, Ɗ. (1979) Zaɓaɓɓun waƙoƙi na da da na yanzu. Kano Thomas Nelson Nigeria Limited

Aliyu, I. F. (2011) Manufar Waƙa a Siyasa: Ire-iren Jigogin Waƙoƙin Siyasa na Hausa. Algaita Journal of Current Research in Hausa Studies, Depatment of Nierian Languages and Linguistics Bayero University, Kano.

Bargery, G. P. (1934) Hausa- English Dictionary and English-Hausa Vocabulary. London. Oɗford University press.

Muhammad, S.U.R. (2021) Fayyataccen Bayani na Ma’anoni da Shiriyar Alƙur’ani Ɗab’I na 1-6. kano. Markaz Imam Buhari

Bello, S. (2002) Tasirin Larabci a kan Rubutattun Waƙoƙin Hausa. Hausa language. Literature and Culture. The fifth Hausa International Conference. Centre For the Study of Nigerian Languages, Bayero University. Kano.

C.N.H.N. (2006) Ƙamusun Hausa. Zaria: Ahmadu Bello University Press. CSLN kuma. Ba haka aka rubuta cikin takarda ba. Bah aka yake ba. A ƙara dubawa

C.S.N.L. (1977) Sabon ƙamus na Hausa zuwa Turanci. Ibadan University Press PLC CSNL a duba bayanan sama

Ɗangambo, A. (2007) Ɗaurayar Gadon Feɗe waƙa [sabon tsari] KanoK.D.G. Publishers

Gusau, S. M. (1983) Waƙoƙin Noma na Baka: Yanaye-Yanayensu da Sigoginsu. Algaita Journal of current Research in Hausa. Deparment of Nigerian Languages. Bayero University Kano. Vol. 1, No 1

Otite, O. and Ogionwo, W. (1981) An Introduction to Sociological Studies. New York: noatrand

Husaini, H. (2024) Salon Amfani da Nassi a Waƙoƙin Hausa: Misalai daga wasu Waƙoƙin Gwagwarmaya. Festschrift in Honour of Professor Salisu Ishaƙ Ja’afar (1964-2022) Department of African Languages, College of Humanities, Alƙalam Uniersity, Katsina.

Newman, R. M. (1997) An English Hausa Dictionary. Lagos: Nelag Press Ltd.

Newman. P. and Roɗana, M. N. (2020) Hausa Dictionary (Ƙamusun Hausa) Kano, Bayrro University Press, Main Library Building.

Umar, A. (2002) Metaphor, Meaning and Message in the Religious Poetry of Aliyu Namangi. Hausa language. Literature and Culture. The fifth Hausa International Conference. Centre For the Study of Nigerian Languages, Bayero University. Kano.

Yahaya, A. B. (1997) Jigon nazarin waƙa. Kaduna. Fisbas Media Services.

Bargery, G. P. (1934) Hausa- English Dictionary and English-Hausa Vocabulary. London. Oɗford University press.

 C.S.N.L. (2006) “Ƙamusun Hausa” Ahmadu Bello University Press, Zaria.

Tijjani, S. A (2011) Jigon Faɗakarwa da Ban dariya cikin waƙoƙin Tashe. Algaita Journal of current Research in Hausa Studies. Department of Nigerian Languages and Linguistics. Bayero University Kano, vol 2, No 1, series vii.

Ahmad. M.S. (1976) Waƙoƙin Sa’adu Zungur, Zaria.Ahmadu Bello University Press.

(2007) Ɗaurayar Gadon Feɗe Waƙa [Sabon Tsari]. K.D.G. Publishers Kano.

Yahaya, A. B. (1997) Jigom nazarin waƙa. Kaduna. Fisbas Media Services.

OxfordAdvanced Learner’s Dictionary (2015) New York, OxfordUniversity Press.

Ahmad, M. S. (1968) Waƙoƙin Sa’adu Zungur, Zaria, NNPC

Buhari, I. (1426/2005) “Sahih Buhari” Darul kutbul Ilmiyya Bairut Lubnan.

Muslim, I. (1425/2004) “Sahih Muslim” Maktabatu Nizaru Masɗafal Baz.

Abu Dawud, I. (1424/2003) “Sunan Abu Dawud” Darul Fikr.

Tirmizi, I. (1430/2009) “Sunan Tirmizi” Darul Fikr.

Ibn Majah, I. (1432/2011) “Sunan Ibn Majah” Maktabatu Nizarul Musɗafal Baz.

Naisaburi H. (2003) “Almustadraku alal Sahihaini” Maktabatu Sham’iyya. Lebenon.

 Dundaye Journal

Post a Comment

0 Comments