Ticker

6/recent/ticker-posts

Fiqihun Azumi (Kashi Na Hudu Da Biyar Da Shida)

FIQHUN AZUMI DAGA MAKARANTAR IBNU TAIMIYYA (4)

Kowa ya sani, saduwa (jima'i) da rana da gangan a watan Ramadhan yana bata Azumin mutum, kuma yana wajabta ramuko da kaffara. To amma idan mutum ya sadu da iyali kusan Asubahi fa, yana zaton da sauran lokaci ashe bai sani ba tun tuni Alfijir ya keto, ko kuma ya manta ya sadu da iyalinsa da rana tsaka, BISA MANTUWA, me ya wajaba a kansa?

To Malamai sun yi sabani a kan haka, daga cikin Malaman Salaf akwai wadanda suka ce: BABU RAMUKO A KANSA, BALLE KAFFARA.

Wannan shi ne abin da Shaikhul Islami Ibnu Taimiyya ya rinjayar, kuma shi ne zabinsa kamar yadda Almajirinsa Ibnu Muflih ya fada a cikin "Al-Furu'u" (5/ 41).

Shaikhul Islami ya ce:

وهذا القول أصح الأقوال وأشبهها بأصول الشريعة ودلالة الكتاب والسنة وهو قياس أصول أحمد وغيره فإن الله رفع المؤاخذة عن الناسي والمخطئ. وهذا مخطئ وقد أباح الله الأكل والوطء حتى يتبين الخيط الأبيض من الخيط الأسود من الفجر واستحب تأخير السحور ومن فعل ما ندب إليه وأبيح له لم يفرط فهذا أولى بالعذر من الناسي.

مجموع الفتاوى (25/ 264)

"Wannar fahimta ta fi sauran inganci, kuma ta fi dacewa da ka'idojin Shari'a da dalilan Alkur'ani da Sunna, kuma kiyasi ne bisa ka'idojin Imam Ahmad da waninsa cikin Malamai. Saboda Allah ba zai kama mai mantuwa da mai kuskure ba. Wannan kuwa mai kuskure ne, Allah ya halasta masa ci da saduwa da iyali har sai farin zare ya bayyana daga bakin zare na Alfijir (sai hasken Alfijir ya bayyana daga duhun dare), kuma an sunnanta jinkirta Suhur, don haka duk wanda ya aikata abin da aka sunnanta masa ko aka halasta masa ba tare da sakaci ba, to wannan shi ya fi cancantar uzuri fiye da mai mantuwa".

Saboda haka, duk wanda ya yi saduwa (jima'i) da rana, wato tsakanin fitowan Alfijir har zuwa faduwar rana, da gangan, da saninsa, Azuminsa ya baci. Kuma ramuko da kaffara sun wajaba a kansa.

Amma wanda hakan ya faru da shi, cikin mantuwa, ko cikin rashin sanin ketowan Alfijir, to babu komai a kansa, kawai zai cigaba da Azuminsa ne, babu ramuko a kansa balle kaffara.

Alal hakika duk wanda ya fahimci Shari'a a dunkulenta, bisa ka'idojinta da gamayyar dalilan Shari'a zai ga cewa; lallai wannar fahimta ita ce mafi inganci kuma mafi karfin dalilai.

Dr Aliyu Muh'd Sani (Hafizahullah)

FIQHUN AZUMI DAGA MAKARANTAR IBNU TAIMIYYA (5)

Malamai sun yi sabani a kan Mai Azumi idan ya ci abinci ko ya sha abin sha da rana a watan Ramadhana a halin mantuwa ko kuskure. Sawa'un wanda ya manta ya ci ko ya sha, ko wanda yana ta ci da sha bisa zaton Alfijir bai keto ba, alhali tun tuni Alfijir ya keto.

Wasu Malaman sun ce: Azuminsa ya baci, sai ya yi ramuko.

Wasu kuma sun ce: Azuminsa yana nan bai baci ba, don haka babu ramuko a kansa.

Wannan shi ne fahimtar da Shaikhul Islami Ibnu Taimiyya ya zaba, saboda karfin dalilansu da dacewarsa ga kiyasi, Al-Imam Ibnul Qayyim da Allama Ibnu Muflih sun hakaito haka daga gare shi. Duba:

إعلام الموقعين (3/ 244)، الفروع (5/ 39)

Shaikhul Islami Ibnu Taimiyya ya ce:

والذين قالوا: لا يفطر في الجميع قالوا: حجتنا أقوى ودلالة الكتاب والسنة على قولنا أظهر؛ فإن الله قال: {ربنا لا تؤاخذنا إن نسينا أو أخطأنا} فجمع بين النسيان والخطأ؛ ولأن من فعل المحظورات الحج والصلاة مخطئا كمن فعلها ناسيا وقد ثبت في الصحيح أنهم أفطروا على عهد النبي صلى الله عليه وسلم ثم طلعت الشمس ولم يذكروا في الحديث أنهم أمروا بالقضاء ولكن هشام بن عروة قال: لا بد من القضاء وأبوه أعلم منه وكان يقول: لا قضاء عليهم. وثبت في الصحيحين أن طائفة من الصحابة {كانوا يأكلون حتى يظهر لأحدهم الخيط الأبيض من الخيط الأسود وقال النبي صلى الله عليه وسلم لأحدهم: إن وسادك لعريض إنما ذلك بياض النهار وسواد الليل} ولم ينقل أنه أمرهم بقضاء وهؤلاء جهلوا الحكم فكانوا مخطئين. وثبت عن عمر بن الخطاب أنه أفطر ثم تبين النهار فقال: لا نقضي فإنا لم نتجانف لإثم. وروي عنه أنه قال: نقضي؛ ولكن إسناد الأول أثبت وصح عنه أنه قال: الخطب يسير. فتأول ذلك من تأوله على أنه أراد خفة أمر القضاء لكن اللفظ لا يدل على ذلك. وفي الجملة فهذا القول أقوى أثرا ونظرا وأشبه بدلالة الكتاب والسنة والقياس وبه يظهر أن القياس في الناسي أنه لا يفطر والأصل الذي دل عليه الكتاب والسنة أن من فعل محظورا ناسيا لم يكن قد فعل منهيا عنه؛ فلا يبطل بذلك شيء من العبادات ولا فرق بين الوطء وغيره سواء كان في إحرام أو صيام.

مجموع الفتاوى (20/ 572 - 573)

"Wadanda suka ce: Azumin mutum ba zai baci ba, a dukkan halayen mantuwa da kuskure, sawa'un a lokacin fitowan Alfijir ko lokacin faduwar rana, suka ce: Hujjarmu ta fi karfi, kuma dalilan Alkur'ani da Sunna suna nuni a kan haka. Saboda Allah ya tabbatar a cikin Ayar Baqara cewa; ba zai kama masu mantuwa da kuskure da laifi ba, a cikin Ayar sai ya hada mantuwa da kuskure. Saboda aikata laifi a aikin Hajji da Sallah a halin kuskure dadai yake da wanda ya aikata cikin mantuwa. Kuma ya tabbata a Hadisi ingantacce; Sahabbai sun sha ruwa a zamanin Annabi (saw) sai rana ta bayyana, kuma babu wanda ya umurce su da ramuko. Haka ya tabbata a Hadisi ingantacce; wasu daga cikin Sahabbai sun kasance suna ci da sha har sai farin zare ya banbanta daga bakin zare, bayan Alfijir ya fito har gari ya yi haske sosai, amma Annabi (saw) bai umurce su da ramuko ba, saboda wadannan jahilai ne masu kuskure. Haka ya tabbata daga Umar bn Khaddab (ra) ya sha ruwa sai rana ta bayyana, sai ya ce: babu ramuko a kanmu, saboda ba mu da zunubi.

A dunkule; wannan fahimta ita ta fi karfi ta hanyar Hadisi da kafa hujja da nazari kuma ta fi dacewa da dalilan Alkur'ani da Sunna da Kiyasi. Da shi zai bayyana cewa; abin da yake kiyasi game da mai mantuwa shi ne; Azuminsa bai baci ba, saboda ka'idar da Alkur'ani da Sunna suka yi nuni a kanta ita ce: duk wanda ya aikata abin da aka yi hani a kansa cikin mantuwa to bai aikata laifi, don haka ibadarsa ba za ta baci ba, kuma babu banbanci tsakanin saduwa da iyali da waninsa na ci da sha, sawa'un a cikin Haramin Hajji ne ko Azumi".

Saboda haka, duk abin da aka yi bisa kuskure ko mantuwa a cikin Azumi, na ci ko sha ba ya bata Azumi, ko da kuwa saduwa da iyali ne, kamar yadda ya gaba a jiya.

Dr Aliyu Muh'd Sani  (Hafizahullah)

FIQHUN AZUMI DAGA MAKARANTAR IBNU TAIMIYYA (6)

Mutane sun kasu kashi biyu wajen karya Azuminsu:

1- Akwai mai ganganci. Wannan dole ya rama Azumin da ya karya, in kuma saduwa ne (jima'i) dole ya yi kaffara bayan ya yi ramuko.

2- Akwai mai kuskure, ko mantuwa, ko rashin sani (jahilin da bai san hukunci ba ko bai san yadda ake yi ba). Wannan babu ramuko in ya karya Azuminsa bisa kuskure, ko mantuwa ko rashin sani balle kuma kaffara.

Wasu Malaman sun banbanta tsakanin mai manyuwa da jahili maras sani wajen karya Azumi. Al-Imam Ibnul Qayyim ya ce:

قستم الجاهل على الناسي في عدة مسائل وفرقتم بينهما في مسائل أخر، ففرقتم بينهما فيمن نسي أنه صائم فأكل أو شرب لم يبطل صومه، ولو جهل فظن وجود الليل فأكل أو شرب فسد صومه، مع أن الشريعة تعذر الجاهل كما تعذر الناسي أو أعظم؟ كما عذر النبي -صلى الله عليه وسلم- المسيء في صلاته بجهله بوجوب الطمأنينة فلم يأمره بإعادة ما مضى...

وعذر عدي بن حاتم بأكله في رمضان حين تبين له الخيطان اللذان جعلهما تحت وسادته ولم يأمره بالإعادة

إعلام الموقعين (3/ 10)

"Kun yi kiyasin jahili maras sani a kan mai mantuwa a mas'aloli da yawa, amma sai kuma kuka raba tsakaninsu a wasu mas'alolin, sai kuka raba tsakaninsu a mas'alar mai Azumi idan ya manta ya ci abinci ko ya sha abin sha, kuka ce: Azuminsa bai baci ba, amma sai kuka ce: idan bai sani ba, sai ya yi zaton akwai sauran dare, sai ya ci ko ya sha Azuminsa ya baci, alhali Shari'a tana yin uzuri ga jahili kamar yadda take yi wa mai mantuwa ko ma fiye da haka, kamar yadda Annabi (saw) ya yi uzuri ga wanda ya munana Sallarsa saboda ya jahilci wajabcin nitsuwa a cikin Sallah, sai bai umurce shi da ramukon Sallolinsa na baya ba...

Haka kuma Annabi (saw) ya yi uzuri ga Adiyyi bn Hatim (ra) a kan cin abinci da ya yi a Ramadhan har sai da gari ya waye wartal, har sai da ya iya banbance tsakanin farin zare daga bakin zare, wadanda ya sanya su a karkashin filonsa, amma Annabi (saw) bai umurce shi da ramuko ba".

Saboda haka jahili mai halin rashin sani dadai yake da mai kuskure ko mantuwa a wajen karya Azumi, duka babu ramuko a kansu. Wannan shi ne zabin Shaikhul Islami Ibnu Taimiyya kamar yadda Almajirinsa Al-Imam Ibnul Qayyim ya hakaito inda ya ce:

تناقضوا كلهم في جعل الناسي في الصوم أولى بالعذر من الجاهل، ففطروا الجاهل دون الناسي، وسوى شيخنا بينهما، وقال: الجاهل أولى بعدم الفطر من الناسي

إعلام الموقعين (5/ 506)

"Masu Qiyasi gaba dayansu sun yi tufka da warwara ta yadda suka sanya mai mantuwa a Azumi shi ya fi cancantar uzuri feye da jahili mai rashin sani, sai suka ce: Azumin jahili ya baci, amma in mai mantuwa ne Azuminsa bai baci ba. Amma Shehinmu (Ibnu Taimiyya) ya daidaita tsakaninsu, ya ce: Jahili shi ya fi cancantar a ce: Azuminsa bai baci ba fiye da mai mantuwa".

Saboda haka duk wanda ya karya Azuminsa saboda mantuwa ko kuskure ko rashin sani to babu ramuko ko kaffara a kansa, kawai zai ci gaba da Azuminsa ne, Azuminsa yana nan bai baci ba. A kan haka Shaikhul Islami ya ce:

قد ثبت بدلالة الكتاب والسنة أن من فعل محظورا مخطئا أو ناسيا لم يؤاخذه الله بذلك وحينئذ يكون بمنزلة من لم يفعله فلا يكون عليه إثم ومن لا إثم عليه لم يكن عاصيا ولا مرتكبا لما نهي عنه وحينئذ فيكون قد فعل ما أمر به ولم يفعل ما نهي عنه. ومثل هذا لا يبطل عبادته إنما يبطل العبادات إذا لم يفعل ما أمر به أو فعل ما حظر عليه.

مجموع الفتاوى (25/ 226)

"Ya tabbata da dalilan Alkur'ani da Sunna cewa; duk wanda ya aikata wani abu da aka hana a halin kuskure ko mantuwa to Allah ba zai kama shi a kan haka ba, a wannan halin zai zama kamar bai aikata laifin ba, don haka babu zunubi a kansa, duk wanda babu zunubi a kansa kuwa to shi ba mai sabo ba ne, ko bai zama wanda ya aikata abin da aka hana ba. To a wannan lokaci sai ya kasance ya aikata abin da aka umurce shi, bai aikata abin da aka hana shi ba. Irin wannan kuwa ibadarsa ba ta baci, kawai ibada tana baci ne ne idan mutum bai aikata abin da aka umurce shi ya aikata ba, ko kuma in ya aikata abin da aka hana shi aikatawa".

Lallai wannar ka'ida ce ta Shari'a mai girma wajen hukunci wa mutane da aiyukansu, rashin sanin irin wannar ka'ida ne yake jefa jahilai da masu guluwwi cikin kuskure wajen hukuncinsu ga mutane ko a kan aiyukansu.

Dr Aliyu Muh'd Sani  (Hafizahullah)

Fiqihun Azumi


Post a Comment

0 Comments