FIQHUN AZUMI DAGA
MAKARANTAR IBNU TAIMIYYA (7)
Shari'a ta yi sauki ga wasu nau'in mutane guda hudu, ta ba su daman shan Azumi matukar suna cikin halin da ya sa aka yi musu rangwamen. Wadannan nau'ukan mutane kuwa su ne:
1- Matafiyi.
2- Maras lafiya.
3- Mai ciki ko mai
shayarwa.
4- Gajiyayyen tsoho.
Kowanne akwai bayanai
da za su zo nan gaba a kansa insha Allahu.
Na farko a cikinsu
shi ne: Matafiyi.
Shi Matafiyi an ba
shi daman ya sha Azumi a watan Ramadhan, sai bayan Sallah ya rama Azumin da ya
sha.
Shaikhul Islami ya
ce:
الفطر
للمسافر جائز باتفاق المسلمين سواء كان سفر حج أو جهاد أو تجارة أو نحو ذلك من
الأسفار التي لا يكرهها الله ورسوله. وتنازعوا في سفر المعصية كالذي يسافر ليقطع
الطريق ونحو ذلك على قولين مشهورين...
ويجوز
الفطر للمسافر باتفاق الأمة سواء كان قادرا على الصيام أو عاجزا وسواء شق عليه
الصوم أو لم يشق بحيث لو كان مسافرا في الظل والماء ومعه من يخدمه جاز له الفطر
والقصر.
مجموع الفتاوى
(25/ 209 - 210)
"Shan ruwa ga
Matafiyi ya halasta bisa Ittifaqin Musulmai, sawa'un tafiya ce ta Hajji ko
Jihadi ko kasuwanci ko makamancinsu cikin tafiye-tafiye da Allah da Manzonsa ba
sa kinsu. Amma Malamai sun yi sabani a kan shan Azumi a tafiya ta sabon Allah,
kamar fashi da makami da makamancinsa zuwa shahararrun maganganu guda biyu...
Saboda haka ya
halasta Matafiyi ya sha Azumi bisa Ittifaqin Al'umma, sawa'un zai iya yin
Azumin ko ba zai iya yi ba, sawa'un Azumin zai wahalar da shi ko ba zai wahalar
da shi ba, ta yadda a ce: tafiyar tasa a cikin inuwa ce ko cikin ruwa, kuma a
tare da shi akwai mai yi masa hidima, to ya halasta ya sha Azuminsa, kuma ya yi
Sallar Kasaru".
Kuma shan Azumin shi
ya fi falala a kan yin Azumin.
Shaikhul Islami ya
ce:
أما
المسافر فيفطر باتفاق المسلمين وإن لم يكن عليه مشقة والفطر له أفضل. وإن صام جاز
عند أكثر العلماء. ومنهم من يقول لا يجزئه.
مجموع
الفتاوى (25/ 214)
"Amma shi
Matafiyi zai sha Azumi bisa Ittifaqin Musulmai, ko da kuwa ba zai sha wahala ba
shan Azumin shi ya fi falala. In kuma ya ce: zai yi Azumin to ya halasta gare
shi wajen mafi yawan Malamai. Amma akwai wadanda suke ganin yin Azumin bai isar
masa ba".
Saboda haka duk wanda
zai yi tafiya ta da'a ma Allah, kamar tafiya aikin Hajji ko Umra ko Jihadi, ko
tafiya ta halas kamar tafiya kasuwanci to abin da ya fi masa falala ya sha
Azuminsa, bayan Sallah sai ya rama. Kuma sawa'un tafiyar a jirgi ne ko mota, duka
ya halasta ya sha Azumin, kuma hakan shi ya fi falala.
Wannan shi yake nuna
mana saukin Shari'ar Muslunci da rahamar Allah ga bayinsa.
Dr Aliyu Muh'd Sani
(Hafizahullah)
FIQHUN AZUMI DAGA
MAKARANTAR IBNU TAIMIYYA (8)
Da Nassin Alkur'ani
Allah ya saukaka wa Matafiyi da Maras lafiya yin Azumin Ramadhana a halin
tafiya ko rashin lafiya. Don haka ya halasta su sha Azumi sai su rama Azumin da
suka sha bayan Ramadhan, in uzurin nasu ya gushe. A kan wannan Musulmai suka yi
Ijma'i.
Don haka Maras lafiya
da ake nufi shi ne wanda ba zai iya yin Azumin ba saboda rashin lafiya ko kuma
in ya yi rashin lafiyan nasa zai karu.
Shaikhul Islami ya
ce:
المريض
الذي لا يطيق الصيام أو الذي يزيد الصوم في مرضه؛ له أن يفطر، وإن تحمل وصام
وأجزأه
شرح
العمدة لابن تيمية (1/ 208)
"Maras lafiya
shi ne wanda ba zai iya yin Azumi ba, ko wanda Azumin zai kara masa rashin
lafiyan nasa. Amma idan ya jure ya yi Azumin to ya isar masa ba sai ya rama
ba".
To a kan samu wasu
masu lafiya amma kuma in sun yi Azumin za su kamu da rashin lafiya, to su ma
ana kiyasinsu a kan marasa lafiya, saboda haduwarsu cikin illarn hukuncin, wato
samun shan wahala.
Shaikhul Islam ya ce:
وفي
معنى المريض الصحيح الذي يخاف من الصوم مرضا أو جهدا شديدا، مثل من به عطاش لا
يقدر في الحر على الصوم، وهو يقدر عليه في الشتاء، أو امرأة قد حاضت والصوم يجهدها.
شرح
العمدة لابن تيمية (1/ 209)
"Mai lafiyan da
yake tsoron kamuwa da rashin lafiya, ko yake tsoron wahala mai tsanani shi ma
zai shiga cikin ma'anar maras lafiya, misalin wanda yake da jin kishin ruwan da
ya kai ba zai iya yin Azumi a zafi ba, sai a lokacin sanyi ne kawai zai iya yi,
ko matar da bayan ta yi al'ada Azumin yana wahalar da ita".
Saboda haka hukuncin
Maras lafiya ko wanda yake tsoron kamuwa da rashin lafiya in ya yi Azumi shi ne
ana so kar ya yi Azumin, kuma ba a so ya yi, wato yin nasa Makruhi ne.
Shaikhul Islam ya ce:
إن
المريض يستحب له الفطر، ويكره له الصوم، فإن صام أجزأه.
شرح
العمدة لابن تيمية (1/ 209)
"Maras lafiya
ana so ya sha Azumi, ba a son ya yi Azumin, amma in ya yi Azumin ya isar masa
ba zai yi ramuko ba".
Wannan sauki ne na
Shari'a, saboda Allah yana son bayinsa da sauki ne, ba ya so su shiga tsanani
da wahala. Allah ya ce:
{يُرِيدُ اللَّهُ بِكُمُ الْيُسْرَ وَلَا يُرِيدُ بِكُمُ الْعُسْرَ
} [البقرة: 185]
Dr Aliyu Muh'd Sani
(Hafizahullah)
FIQHUN AZUMI DAGA
MAKARANTAR IBNU TAIMIYYA (9)
Shin Gulma da Giba da
Annamimanci da Zagin mutane suna karya Azumi?
Ya tabbata cikin
Hadisin da Imamul Bukhari ya riwaito da isnadinsa:
عن
أبي هريرة رضي الله عنه، قال: قال رسول الله صلى الله عليه وسلم: «من لم يدع قول
الزور والعمل به، فليس لله حاجة في أن يدع طعامه وشرابه»
صحيح
البخاري (3/ 26)
Daga Abu Huraira
(ra), Annabi (saw) ya ce:
"Duk wanda bai
bar yin maganar karya ko aiki da ita ba, to Allah ba ya bukatar ya bar cin
abinci da shan abin shansa (Allah ba ya bukatar Azuminsa)".
Wannan ya sa wasu
Malamai cikin Salaf suke ganin gulma da cin naman mutane da annamimanci suna
karya Azumin mutum. Wasu Malaman kuma suna ganin ba ya karyawa.
Shaikhul Islami Ibnu
Taimiyya ya fayyace mas'alar inda ya ce:
"وتحقيق
الأمر في ذلك أن الله تعالى أمر بالصيام لأجل التقوى وقد قال صلى الله عليه وسلم:
"من لم يدع قول الزور والعمل به فليس لله حاجة في أن يدع طعامه وشرابه"،
فاذا لم تحصل له التقوى لم يحصل له مقصود الصوم فينقص من أجر الصوم بحسب ذلك".
مختصر
الفتاوى المصرية (ص: 289)
"Tantance magana
a kan haka shi ne; lallai Allah Madaukaki ya yi umurni da yin Azumi ne don
samar da Taqwa da jin tsoronsa, kuma Annabi (saw) ya ce:
"Duk wanda bai
bar yin maganar karya ko aiki da ita ba, to Allah ba ya bukatar ya bar cin
abinci da shan abin shansa".
To idan Taqwar ba ta
samu ga mai Azumi ba, to ba a samu manufar da ake so na yin Azumin nasa ba, don
haka zai tauye ladansa gwargwadon munanan abin da ya aikata".
Saboda haka Azuminsa
yana nan, amma kuma ba shi da ladan Azumin.
Don haka matukar
mutum yana Azumi, amma bai kiyaye harshensa daga maganganun banza da karerayi
da gulman mutane da zaginsu da cin namansu ba, to wahalar banza kawai yake sha,
ba zai samu ladan komai ba, saboda Allah ba ya bukatar Azumin da ba zai samar da
Taqwa ma bawa, ta hanyar kare gabobinsa daga aikata munanan aiyuka ba.
Dr Aliyu Muh'd Sani
(Hafizahullah)
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.