Godiya ta tabbata ga Allah Madaukakin Sarki, wanda ya shar'anta ma bayi hukunce-hukuncen da suka dace da hali da yanayinsu, don su iya bauta ma Allah cikin sauki, don rayuwarsu ta inganta, kuma ya yi musu sakamako a Ranar Lahira.
Tsira da amincin Allah su tabbata
ga Ma'aikin Allah, Annabi Muhammadu, wanda ya zo mana da wannar Shari'a mai
sauki, da iyalan gidansa, da Sahabbansa da wadanda suka bi su da kyautatawa.
Allah Madaukakin Sarki ya
farlanta fitar da Zakka, har ya sanya shi cikin rukunnan Muslunci guda biyar,
kamar yadda ya tabbata ta harshen Manzonsa (saw).
Fitar da Zakka da bayar da ita ga
talakawa da wadanda suka cancance ta yana daga cikin manyan abubuwa da suke
bayyana kyaun Shari'ar Muslunci, da kasancewarta babban hanya ta warware
matsalolin rayuwar al'umma; matsalolin zamantakewa, matsalolin siyasa, da matsalolin tattalin arziki da sauransu.
Allah ya ce:
وَمَا أُمِرُوا إِلَّا لِيَعْبُدُوا اللَّهَ
مُخْلِصِينَ لَهُ الدِّينَ حُنَفَاءَ وَيُقِيمُوا الصَّلَاةَ وَيُؤْتُوا الزَّكَاةَ
ۚ وَذَٰلِكَ دِينُ الْقَيِّمَةِ
{Ba a umurce su da komai ba face
su bauta ma Allah suna masu tsarkake Addini gare shi, suna masu karkata gare
shi, kuma su tsayar da Sallah, su bayar da Zakka, wannan shi ne Addini
tsayayye} [al-Bayyinah: 5].
Kuma Allah ya ce:
ۚ
وَأَقِيمُوا
الصَّلَاةَ وَآتُوا الزَّكَاةَ وَأَقْرِضُوا اللَّهَ قَرْضًا حَسَنًا ۚ وَمَا تُقَدِّمُوا
لِأَنفُسِكُم مِّنْ خَيْرٍ تَجِدُوهُ عِندَ اللَّهِ هُوَ خَيْرًا وَأَعْظَمَ أَجْرًا ۚ
{Ku tsayar da Sallah, ku bayar da
Zakka, ku bai ma Allah rance, duk abin da kuka gabatar ma kawunanku za ku same
shi a wajen Allah, shi ya fi alheri, kuma ya fi girman daraja} [al-Muzammil:
20].
Ayoyi a kan farlancin Zakka suna
da yawa. Daga cikin Hadisai kuma akwai fadin Annabi (saw):
" بُنِيَ الإِسْلاَمُ عَلَى خَمْسٍ:
شَهَادَةِ أَنْ لاَ إِلَهَ إِلَّا اللَّهُ وَأَنَّ مُحَمَّدًا رَسُولُ اللَّهِ، وَإِقَامِ
الصَّلاَةِ، وَإِيتَاءِ الزَّكَاةِ، وَالحَجِّ، وَصَوْمِ رَمَضَانَ
"
[البخاري ,صحيح البخاري
,1/11]
((An gina Muslunci a kan abubuwa
guda biyar; Shaidawa babu abin bauta sai Allah, kuma Annabi Muhammad ma'aikin
Allah ne, da tsayar da Sallah, da ba da Zakka, da aikin Hajji, da Azumin watan
Ramadhan)). Sahihul Bukhari (8), Sahihu Muslim (16).
Zakka tana daga cikin rukunnan
Muslunci, ita ce mahadin Sallah a cikin nassoshin Shari'a. Musulmai gaba daya
sun hadu a kan farlancinta, sun yi Ijma'i yankakke wanda babu shakka a cikinsa.
Don haka duk wanda ya yi inkarin wajabcinta to hakika ya kafirta, za a nemi ya
tuba, idan ya tuba, ya yarda da wajabcin Zakkar shi kenan, idan kuma ya ki tuba
to za a kashe shi a matsayin kafiri, wanda ya yi ridda daga Muslunci. Ba za a
yi masa wanka ba, ba za a suturce shi a likkafani ba, ba za a yi masa Sallah
ba, ba za a yi masa addu'an neman rahma ba, ba za a bisne shi a makabartan
Musulmai ba, kawai za a tona rami ne a can nesa a rufe shi, don kar warinsa ya
dami mutane, 'yan'uwansa su cutu.
Haka duk wanda ya ki bayar da
Zakka, ko ya rage abin da ya wajaba a kansa a cikinta alal hakika ya cancanci
ukuba mai tsananin gaske.
Zakka tana wajaba ne a abubuwa
guda hudu:
Na farko:
Abubuwan da suke fitowa a kasa na
kayan gona:
Zakka tana wajaba a cikinsu
saboda fadin Allah Madaukaki:
يَا أَيُّهَا الَّذِينَ آمَنُوا أَنفِقُوا مِن
طَيِّبَاتِ مَا كَسَبْتُمْ وَمِمَّا أَخْرَجْنَا لَكُم مِّنَ الْأَرْضِ وَلَا تَيَمَّمُوا
الْخَبِيثَ مِنْهُ تُنفِقُونَ وَلَسْتُم بِآخِذِيهِ إِلَّا أَن تُغْمِضُوا فِيهِ وَاعْلَمُوا
أَنَّ اللَّهَ غَنِيٌّ حَمِيدٌ
{Ya ku wadanda suka yi imani, ku
ciyar daga dadadan abin da kuka nema kuka samu, da kuma abin da muka fitar muku
daga kasa} [al-Baqara: 267].
Kuma Allah ya ce:
وَآتُوا حَقَّهُ يَوْمَ حَصَادِهِ
{Ku ba da hakkinsa a ranar girbe shi}
[al-An'am: 141].
Hakkin dukiya mafi girma shi ne
Zakka. Annabi (saw) ya ce:
«فِيمَا سَقَتِ السَّمَاءُ وَالعُيُونُ
أَوْ كَانَ عَثَرِيًّا العُشْرُ، وَمَا سُقِيَ بِالنَّضْحِ نِصْفُ العُشْرِ»
[البخاري، صحيح البخاري،
١٢٦/٢]
((A abin da ruwan sama ya shayar ko ya kasance
ta idaniyar ruwa za a fitar da zakkar daya bisa goma, a abin da aka samu ta
hanyar bayin ruwa za a fitar da rabin daya bisa goma)) Bukhari (1483).
Zakka ba ta wajaba har sai ya kai
Nisabi, shi ne wusiki biyar, saboda fadin Annabi (saw):
«لَيْسَ فِيمَا دُونَ خَمْسَةِ
أَوْسُقٍ صَدَقَةٌ، وَلَا فِيمَا دُونَ خَمْسِ ذَوْدٍ صَدَقَةٌ،
[مسلم، صحيح مسلم، ٦٧٣/٢]
((Babu Zakka a kayan gona ko 'ya'yan itatuwa
har sai ya kai wuski biyar)). Muslim (979).
Wuski shi ne sa'i sittin (60) da
sa'in Annabi (saw). Don haka Nisabi shi ne sa'in dari uku (300), wanda yake
dadai da kilo dari shida da sha biyu (612), kowane sa'i kilo biyu da digo sha
biyar (2.15).
Abin da za a fitar a ciki shi ne
daya bisa goma, idan da ruwan sama aka shayar da shukan ba tare da wahala ba.
Ba a fitar da Zakka ga kayan
marmari da ganyaye, kamar kankana, lemo, yakuwa da alayyaho da makamantansu,
saboda Sayyidina Umar (ra) ya ce: (Babu Zakka a kayan marmari). Sayyidina Aliyu
(ra) ya ce: (Babu Zakka a apple da abin da ya yi kama da shi).
Na biyu: Dabbobin Ni'ima:
Su ne rakuma, shanu, da tumaki da
awaki, idan sun kasance sakakku, suna kiwo daga ciyawar da Allah ya tsirar, ba
tare da aikin dan-adam ba, kuma an tanade su don tatsa, da haifuwa, idan sun
kai nisabi Zakka ta wajaba a kansu.
Nisabin rakuma shi ne rakuma
biyar (5), shanu talatin (30), tumaki da awaki arba'in (40). Amma idan daurarru
ne, wadanda ake ciyar da su, kuma ba na kasuwanci ba ne babu Zakka a kansu.
Amma idan na kasuwanci ne akwai Zakka a kansu.
Na uku: Kudi:
Su ne zinari da azurfa, a kowane
yanayi suke. Allah ya ce:
وَالَّذِينَ يَكْنِزُونَ الذَّهَبَ وَالْفِضَّةَ
وَلَا يُنفِقُونَهَا فِي سَبِيلِ اللَّهِ فَبَشِّرْهُم بِعَذَابٍ أَلِيمٍ
{Wadanda suke taskance zinari da azurfa ba sa
ciyar da su saboda Allah ka yi musu bushara da azaba mai radadi.
يَوْمَ يُحْمَىٰ عَلَيْهَا فِي نَارِ جَهَنَّمَ
فَتُكْوَىٰ بِهَا جِبَاهُهُمْ وَجُنُوبُهُمْ وَظُهُورُهُمْ هَٰذَا مَا كَنَزْتُمْ لِأَنفُسِكُمْ
فَذُوقُوا مَا كُنتُمْ تَكْنِزُونَ
Ranar da za a toye su a wutar
jahanna, sai a yi lalas da su a goshin masu su, da gefen jikinsu, da bayansu,
wannan shi ne abin da kuka taskance ma kawunanku, ku dandana abin da kuka
kasance kuna taskancewa} [al-Taubah:
35].
Abin da ake nufi da taskance su
shi ne rashin bayar da su saboda Allah, babba a ciki kuwa shi ne Zakka da Allah
ya farlanta.
Ya tabbata Annabi (saw) ya ce:
«مَا مِنْ صَاحِبِ ذَهَبٍ وَلَا
فِضَّةٍ، لَا يُؤَدِّي مِنْهَا حَقَّهَا، إِلَّا إِذَا كَانَ يَوْمُ الْقِيَامَةِ،
صُفِّحَتْ لَهُ صَفَائِحُ مِنْ نَارٍ، فَأُحْمِيَ عَلَيْهَا فِي نَارِ جَهَنَّمَ، فَيُكْوَى
بِهَا جَنْبُهُ وَجَبِينُهُ وَظَهْرُهُ، كُلَّمَا بَرَدَتْ أُعِيدَتْ لَهُ، فِي يَوْمٍ
كَانَ مِقْدَارُهُ خَمْسِينَ أَلْفَ -[681]- سَنَةٍ، حَتَّى يُقْضَى بَيْنَ الْعِبَادِ،
[مسلم، صحيح مسلم، ٦٨٠/٢]
((Babu wani ma'abocin zinari da
azurfa wanda ba ya bayar da hakkinsu face idan Ranar Kiyama ta kasance za narka
su a fadada su kamar faranti na wuta, sai a toya su a wutar Jahannama, sai a yi
masa lalas da su gefensa da goshinsa da bayansa, duk lokacin da ya yi sanyi sai
a sake maimaitawa, a ranar da take kwatankwacin shekara dubu hamsin, har sai an
yi hukunci tsakanin bayi)) Muslim (987).
Zakka tana wajaba a zinari da
azurfa sawa'un an buga su sun zama kudi, ko kayan ado, saboda dalili bai
banbance ba. Ya tabbata daga Abdullah bn Amr (ra) ya ce:
أَنَّ امْرَأَةً أَتَتْ رَسُولَ اللَّهِ صَلَّى
اللهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ وَمَعَهَا ابْنَةٌ لَهَا، وَفِي يَدِ ابْنَتِهَا مَسَكَتَانِ
غَلِيظَتَانِ مِنْ ذَهَبٍ، فَقَالَ لَهَا: «أَتُعْطِينَ زَكَاةَ هَذَا؟»، قَالَتْ:
لَا، قَالَ: «أَيَسُرُّكِ أَنْ يُسَوِّرَكِ اللَّهُ بِهِمَا يَوْمَ الْقِيَامَةِ سِوَارَيْنِ
مِنْ نَارٍ؟»، قَالَ: فَخَلَعَتْهُمَا، فَأَلْقَتْهُمَا إِلَى النَّبِيِّ صَلَّى اللهُ
عَلَيْهِ وَسَلَّمَ، وَقَالَتْ: هُمَا لِلَّهِ عَزَّ وَجَلَّ وَلِرَسُولِهِ
[السجستاني، أبو داود، سنن أبي
داود، ٩٥/٢]
((Wata mata ta zo wajen Annabi (saw) da 'yarta
a tare da ita, a hanunta akwai warwaro biyu na zinari masu kauri, sai Annabi
(saw) ya ce: "Shin kina bayar da Zakkar wannan?" Sai ta ce: A'a. Sai
ya ce: "Zai yi miki dadi a Ranar Kiyama Allah ya yi miki warwaro da su
warwaro na wuta?". Ya ce: sai ta cire su, ta jefa su ga Annabi (saw), ta
ce: Na bayar da su ga Allah da Manzonsa)). Abu Dawud (1563), Tirmiziy (637),
Nasa'iy (2479).
Zakka ba ta wajaba a zinari har
sai ya isa nisabi, shi ne Dinari ishirin (20), saboda Annabi (saw) ya ce:
وَلَيْسَ عَلَيْكَ شَيْءٌ - يَعْنِي - فِي الذَّهَبِ
حَتَّى يَكُونَ لَكَ عِشْرُونَ دِينَارًا،
[السجستاني، أبو داود، سنن أبي
داود، ١٠٠/٢]
((Babu komai a kanka na Zakkar zinari har sai
kana da Dinari ishirin)) Abu Dawud (1573).
Dinarin da ake nufi shi ne wanda
nauyinsa ya kai gram hudu da kwata, don haka nisabin zinari shi ne gram tamanin
da biyar (85g).
Haka Zakka ba ta wajaba a azurfa
har sai ya kai nisabi; shi ne uqiya biyar, saboda Annabi (saw) ya ce:
«لَيْسَ فِيمَا دُونَ خَمْسِ
[البخاري، صحيح البخاري،
١١٦/٢]
((Babu Zakka a kasa da uqiya
biyar)). Bukhari (1447), Muslim (979).
Uqiya shi ne dirhami arba'in, don
haka nisabin shi ne dirhami dari biyu (200), wanda yake daidai da gram dari
biyar da casa'in da biyar (595g) na dirhami.
Zakka ta wajaba a kudi na
takardu, saboda a yau su ne canjin zinari da azurfa, su suka maye gurbinbsu,
don haka idan azurfa ya isa nisabi to Zakka ta wajaba.
Zakka tana wajaba a zinari da
azurfa da takardun kudi sawa'un suna wajenka, ko kuma suna wajen mutane, kana
binsu bashi. Saboda haka Zakka tana wajaba a bashin da kake bi. Idan bashin
yana wajen mai wadata ne wanda zai iya biya, to mutum zai yi lissafi ya fitar
da Zakka da shi, ko kuma ya jinkirta har sai ya karba, sai ya fitar masa, na
tsawon shekarun da suka yi.
Amma idan kuma bashin yana hanun
talaka ne, ko mai kin biyan bashi, wanda karban kudin daga wajensa yana da
wahala, to babu Zakka a kan wannan bashi, har sai lokacin da mutum ya karba,
sai ya fitar na shekarar da a cikinta ya karba, ban da sauran shekarun da suka
gabata.
Na hudu: Kayan kasuwanci:
Su ne dukkan abin da aka tanada
don neman kudi da kasuwanci da su; na gida, ko fili, ko dabbobi, ko abinci, ko
motoci ko kayan shago da sauran dangogin dukiya. Sai mutum ya kimanta su a
kowace shekara, sai ya fitar da Zakkarsu a karshen shekara, zai fitar da daya
bisa hudun daya bisa goman kimar kayan, sawa'un kimar dadai yake da yadda ya
sayi kayan, ko ya yi kasa da haka, ko ya fi haka.
Babu Zakka ga abin da mutum ya
tanada don amfanin kansa, kamar abinci, ko kayan shimfida, ko gidan zama, ko
motocin hawa, ko kayan sakawa, in ban da zinari da azurfa. Saboda Annabi (saw)
ya ce:
«لَيْسَ عَلَى المُسْلِمِ فِي
فَرَسِهِ وَغُلاَمِهِ صَدَقَةٌ»
[البخاري، صحيح البخاري،
١٢٠/٢]
((Babu Zakka a kan Musulmi a
bawansa ko dokinsa)) Bukhari (1463), Muslim (982).
Haka babu Zakka ga abin da aka
tanada don bayar da haya, kamar gidaje da filaye, da motoci da makamantansu,
Zakkar tana wajaba ne a kudin da aka tara na hayan, idan sun shekara, sun kai
nisabi.
Don haka 'yan'uwa wadanda suka
mallaki nisabi, wajibi ne su gaggauta fitar da Zakkar dukiyarsu, su sauke
wajibin da yake kansu, don su samu tsarki da albarka a cikin dukiyarsu, kuma su
samu lada da tsira daga azaba da fushin Allah Madaukaki. Kuma wajibi ne mutum
ya tsarkake niyya, ya sake ransa wajen ba da Zakkar, kar mutum ya bayar alhali
ransa ba ya son bayarwan.
Wanda ya yi jinkiri bai fitar da
Zakka ba, to ya ribaci wannan wata mai albarka, wata mai falala, watan kyauta,
watan da talakawa suke cikin bukata zuwa ga abinci, suke bukatar sababbin
tufafi don Eidi ma iyalan, suke bukatar yalwata abinci ma iyalansu a ranakun
Eidi. Lallai duk wanda ya makara bai bayar da Zakka a kan lokacinta ba, to ya
gaggauta ya bayarwa a wannan wata, la'alla ya samu falala saboda falalan watan.
Allah ya karba mana Ibadunmu, ya
gafarta mana zunubanmu, ya taimake mu a kan kiyaye Azuminmu, ya nufe mu da
yawaita aiyukan da'a a cikin wannan wata, ya shiryar da mu hanya madaidaiciya.
Kuma Allah ya jikan iyayenmu, ya yaye mana matsaloli da fitintinu da suke damun
kasarmu, na kuncin rayuwa da rashin tsaro da aminci, ya ba mu shugabanni na
gari, masu tsoron Allah da kishin al'umma da tausayin talakawa.
Dr Aliyu Muh'd Sani
(Hafizahullah)
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.