Ticker

6/recent/ticker-posts

Amfani Da Karin Magana A Matsayin Kanun Labari: Nazari A Kan Littafin Magana Jari Ce Na Abubakar Imam

Citation: Usman, MUHAMMAD Ph.D (2025). Amfani Da Karin Magana A Matsayin Kanun Labari Nazari A Kan Littafin Magana Jari Ce Na Abubakar Imam. Yobe Journal of Language, Literature and Culture (YOJOLLAC), Vol. 13, Number 1. Department of African Languages and Linguistics, Yobe State University, Damaturu, Nigeria. ISSN 2449-0660

AMFANI DA KARIN MAGANA A MATSAYIN KANUN LABARI NAZARI A KAN LITTAFIN MAGANA JARI CE NA ABUBAKAR IMAM

BY

USMAN, MUHAMMAD Ph.D

Tsakure

Karin Magana wani ɓangare ne na adabin gargajiya na Hausa wanda ake amfani da shi a cikin zantukan yau da kullum. Ba a banza ake saka karin magana cikin zance ba, akwai dalilai da dama ciki kuwa har da jawo hankalin mai sauraro natsu da kai ya fahimci saƙonnin dake ƙunshe waɗanda suka shafi yanayin da ake ciki. Imam ya yi amfani da karin magana masu dama a labarinsa kodai a matsayin kanun wasu daga cikin ‘ya’yan labaransa ko waɗanda ya saka cikin zantukan taurarinsa. Waɗanda ya yi amfani da su a matsayin kanun wasu daga cikin ‘ya’yan labaransa kuwa ya yi haka ne domin ya fito da saƙonnin da karin maganar suka ƙunsa a sarari domin mai sauraro ko karatu ya fahimci zahirin saƙonnin ta amfani da abubuwan da suka abku ga wasu taurarin sakamaon abubuwan da suka aikata walau alheri ko sharri.

Muhimman kalmomi: Karin Magana da kanun labarai da Magana Jari Ce,

Abstract

Proɓerbs is an important form of oral literature mostly employed by Hausa people in their daily conɓersations. It is not just used for entertainment but it is mostly used to send numerous messages that suite the current situations. Imam used this form of oral literature in his story not only for entertainment but as heading of some of his frame stories to practically demonstrate the meaning of the form in order to draw the attention of his reader to the fact that whateɓer one does, be it good or bad, the results of his actions will be at his door waiting to pay him back as can be seen in the eɗamples from some of the frame stories.

Key words Karin Magana, title and Magana Jari

1.0 Gabatarwa

Magana Jari Ce labari ne da ya yi fice a tsakanin masana da manazarta da masu sha’awar karanta ayyukan adabin Hausa ko domin ƙara faɗaɗa ilimi ko kuma domin nishaɗi. Adon harshe na daga cikin tubalan da Imam ya yi amfani da su wajen gina labari kuma ya. Wannnan maƙalar ta yi ƙoƙari ne wajen taskace bajimtar da Imam ya yi ne ta amfani da karin magana a matsayin kanun labarinsa na Magana Jari Ce. Haka kuma ya yi amfani da ita wajen raawa mafi yawa daga cikin ‘ya’yan labaran cikin littafin. Mawallafin ya yi haka ne domin ya fito da ma’anar karin magana sarari musamman ga waɗanda ba su fahimci muhimman saƙonnin dake ƙunshe cikin karin magana ba, akasarin mutane suna amfani da karin magana ne ba tare da sun san zahirin saƙonnin dake cikinta ba. Za a iya cewa wannan ƙoƙari da Imam ya yi tamkar fassara ce ya yi tare da misalai domin mai karatu ko sauraro ya yi karatun ta-nutsu.

2.0 Karin Magana

Masana da manazarta adabi sun ta kai komo kan ma’anar karin magana. ma fi yawansu, sun yi ittifaƙin cewa abu ne mai wahala a ce kai tsaye ga wata ma’ana da aka yi ittifaƙi da ita. Amma wannan bai hana kowa tunanin samar da fahimtarsu ba. Amin (2002) ya ambato ra’ayoyin masana da ra’ayoyinsu suka sha bamban danagne da ma’anar karin magana amma dai za a iya cewa kusan bambance-bambancen ba su taka kara sun karya ba. Hasali ma, Amin (2002) cewa ya yi idan aka yi la’akari da ma’anonin da waɗannan masana suka bayar na karin magana, duk da bambance-bambance, za a iya cewa karin magana:

i. Yawanci taƙaitacciyar maganar al’umma ce (mai ma’ana).

ii. Yawanci karɓaɓɓiyar magana ce da al’umma ta amince da ita.

iii. Magana ce da ke cike da zuzzurfar ma’ana.

 iɓ. Magana ce da ba ta tsufa.

v. Magana ce da ke da ɗandanon daɗi (a kunne).

vi. Maƙasudinta shi ne isar da wani saƙo a kan gaɓa.

Masana irin su Bishop (1922) da Whitting (1931) da Bichi (1977) da Umar (1978) gaba ɗaya sun yi ittifaƙi cewa abu ne mai wahala a iya tantance wa tsakanin zancen hikima na kacici-kacici da karin magana. Whitting (1931) cewa ya yi akasarin masu tattara zantukan hikima na taka-tsatsan wajen kawo fitaccen bambanci tsakanin karin magana da jumlolin zantukan hikima. Bada (1995) ya ruwaito wasu masana adabin baka da suka bayar da gudumuwa wajen bayyana ma’anar karin magana dangane da ƙumshiyarta. Daga cikin waɗannan masana, akwai Ploppenganer (1969) wanda ya bayar da ma’anar karin magana da cewa ‘Karin magana zancen hikima ne da ke bayani kan al’amuran rayuwa baki ɗaya. Wilson (1970) a nasa bayanin dangane da ma’anar karin magana, ya ce karin magana zancen ne cikin hikima na al’ummar duniya. Kelson (1971) ya ce ‘Karin magana zancen hikima ne da ke fayyace gaskiyar al’amari.’ Shi kuwa Nwoga (1975) a tasa fahimtar dangane da karin magana, ga yadda ya ce ‘Karin magana, taƙaitaccen zance ne cikin hikima da ke fito da falsafar al’ummar zamanin da.’ Haka shi ma Hook (1977) cewa ya yi ‘Karin magana zance ne da ke nuna hikimar al’umma ta gargajiya.’

Ita kuwa Finnegan (1970:28) cewa ta yi ‘idan aka yi la’akari da kusancin da ke tsakanin zantukan hikima gaba ɗayansu, to abu ne mai wahala a tantance bambancin da ke tsakanin karin magana da sauran zantukan hikima.’ Haka shi ma Nyembeze (1974) cewa ya yi ‘abu ne mai wahala wani ya iya nuna bambanci tsakanin karin magana da sauran zantukan hikima na al’umma.’ A ra’ayoyin waɗannan masana sun zo daidai dangane da ma’anar karin magana. A zahiri maganar tasu haka take domin idan aka dubi zantukan hikima na Hausa, za a iske kusan ba abu ne mai sauƙi ba a ce za rarrabe tsakaninsu. Wato kowane lokaci za a iya aza ɗaya a muhallin ɗayan. Misali idan aka ɗauki wannan baƙar maganar mai cewa ‘Shakulatin ɓangaro, ungulu ta ga gawar mota.’ Wasu na iya ɗaukar wannan a matsayin karin magana a yayin da wasu za su kalle ta a matsayin baƙar magana ko shaguɓe.

Hassan (2009) ya tofa albarkacin bakinsa a wata maƙala da ya gabatar da cewa adabin baka musamman ma zantukan hikima irin su karin magana da zambo da habaici da kirari da sauransu, wani bakandamen fage ne da ke tattare da hikima da falsafar rayuwar Bahaushe. Ya ce falsafar rayuwa ba ta tsaya ne a kan nishaɗi ko molon ka ba ne kawai, har ma takan shafi al’amuran tattalin arziƙi da siyasa da yanayin zamantakewar al’umma. Wannan ya nuna a fili kenan cewa nazarin adabi ya wuce maganar nishaɗi. Amma kuma marubucin ya gano cewa sau da yawa ‘yan siyasa na yawan amfani da ire-iren waɗannan karin magana domin shawo kan al’ummominsu domin ganin ba su tayar da ƙayar baya ba. Ya buga misalai da wasu daga cikin waɗannan nau’o’in karin maganar kamar su:

i. Idan dambu ya yi yawa ba ya jin mai.

ii. Ba kullum ake kwana a gado ba.

iii. Da muguwar rawa gwamma ƙin tashi

Malumfashi da Ibrahim (2014) sun bayyana cewa kalmomi guda biyu ne aka gina wannan lafazi da su, wato ‘kari’ da kuma ‘magana.’ Sun yi bayanin cewa:

 ’kari’ na nufin wani ɓangare ko rabi ko karyayye ko kuma rababbe. Alhali kuma ‘magana’ na nufin zance ko furuci ko kalami da mutum kan yi domin a fahimci abun da ke cikin zuciyarsa. Kenan idan muka dubi batun a yadda yake a zube, za mu ce ba wani abu ba ne karin magana face zancen da aka yi wa giɓi ko aka karya ko raba shi ko kuma aka kawo wani ɓangare aka yi watsi da waniɓangarenMalumfashi da Ibrahim (2014)

Bunza (2017:3) ya tofa albarkacin bakinsa a kan matsayin karin magana inda ya ce:

Karin magana babbar taskar adabi ce ta adana muhimman abubuwa na kunne ya girmi kaka. A ƙa’idar masana adabi, karin magana wata taƙaitacciyar ko gajeruwar jumla ce mai ɗauke da babban saƙon da ya fi ta tsawo a zahiri idan za a yi fashin baƙinsa. Daga cikin karin magana akwai masu ba da haske a kan bincike da dabarun bincike da ƙwarewar mai aikin bincike kamar:

i. Abin da wayo ya ɓoye hankali ke gano shi

ii. Tafiya da waiwaye tana maganin mantuwa

iii. Matambayi ba ya ɓata

iv. Gani ya kori ji

Wannan bayani da Bunza ya yi, ya ƙara fito da maganar masana cewa karin magana taƙaitaccen zance ne ko gajeruwar kalma ce mai ɗauke da faffaɗar ma’ana da ke bukatar nazari ko zuzzurfan tunani kafin a gane irin saƙonnin da take ɗauke da su.

A taƙaice, wannan nazarin yana ganin za a iya cewa karin magana wani taƙaitaccen zance ne na hikima da ke cike da fasaha na iya tsara magana cikin hikima wadda ba kowa ne zai iya fahimtar saƙo ko ma’anar da ke tattare da ita ba face wanda ya laƙanci harshen da aka gina ita karin maganar da shi. Yawanci akan gina karin magana ne ta la’akari da wani abu da aka saba da ganinsa mai ɗauke da wani darasi da ya kamata a lura da shi. Ana gina karin magana da kalmonin da aka saba amfani da su cikin zancen yau da kullum, sau da yawa ma’anonin kan sauya daga ma’anarsu ta zahiri. Ana amfani da sunayen dabbobi da tsirrai da garuruwa da kayan amfanin da sunayentufafi da da sunayen sana’o’i da sunayen muƙamai na sarauta da dai sauran duk wani abu da ɗan’adam ya sani ya kuma san amfaninsa.

A karin magana akan danganta zance ko aikin da ake yi kuma ya dace da yanayi ko lokacin da abu ya auku. Misali, idan ana cikin maganar wani da ake son gani cikin gaggawa, sai kwatsam a gan shi ya zo ba tare da an aika ɗan saƙọ ba. Nan take sai a yi amfani da karin magana da ta dace da zuwansa, ‘Faɗuwa ta zo daidai zama,’ Ko ‘Kaya sun tsinke a gindin kaba,’ ko kuma ‘Ɗan halas ya ƙambato.’

Da wannan fassara ne aka aza wannan aiki tare da ƙudurin ɗaukar labarin Magana Jari Ce domin kwakkwafe ire-iren saƙonnin da Imam ya bijiro da su cikin littafin. Littafin ya shahara sosai a idon masana da ɗaliban adabin Hausa har da masu sha’awar karanta habarcen Hausa saboda a fito da fa’idojin da ke tattare a cikin karin magana da suka shafi gargaɗi da ilmantarwa da samar da nishaɗi ga mai sauraro da mai furtawa.

Wannan wata dabara ce kamar yadda masana da manazarta irin su Ɗangabo (2008) da Umar (2010) da Bugaje (2014) suka bayyana cewa salo ne da ake daukar halayyar wani abu maras rai a bai wa wata halitta mai rai. Misali:

i. Yaro man kaza

 ii. Babba juji ne

 iii.Namiji dangin barkono sai an tauna ka a san yajinka

Karin magana ginshiƙi ne wajen fito da fasahar harshe a cikin zancen yauda kullum. Ana iya cewa tamkar gishiri ne a miya domin kuwa wata dabara ce da take nuna irin yadda al.ummar da take amfani da ita. Ba karin magaana ne kaɗai azancin magana da Imam ya yi amfani da ita ba a wannan labarin, akwai sauran nau’o’in azancin magana irin su kirari da kacici/kacici da baƙar magana da shaguɓe da sauransu amma dai karin magana ne ta fi ɗaukar hankalin wannan maƙala, saboda haka a kanta ne nazarin ya mayar da hankali. Imam ya yi amfani da karin magana a matakai uku a cikin wannan labaari nasa. Da farko ya yi amfani da ita a matsayin kanun labarin baki ɗaya inda ya sanya masa suna .Magana Jari Ce. A mataki na biyu, an kasa labarin zuwa kundaye uku, to haka aka sanyawa kowane kundi suna da wannan karin magana ta Magana Jari Ce. Sai kuma a mataki na uku inda Imam ya sakawa taurarin wasu daga cikin ɗiyan labaran karin magana a cikin lafuzansu. Wani bincike da aka gudanar ya tabbatar da cewa Imam ya yi da karin magana har guda ɗari biyu da talatin daidai wannan labari. Usman (2023).

3.0 Maganna Jari Ce

Bayan kammala gasar da ta haifar da waɗancan litattafai guda biyar da aka ambata a baya, sai East ya nemi da a ba hukumarsa aron Imam ya zo Zariya takanas don ya ƙara samar da ƙarin litattafan karantawa a makarantun elementare na lardin Arewacin Nijeriya. Matakan da aka ɗauka don samar da Magana Jari Ce, Malumfashi (1995) ybayar da haske inda ya ruwaito rahoton hukumar talifi na cewa:

 An yi amfani da labarai daga wasu littattafan labarai da tatsuniyoyin sassan duniya dabam-daban aka sake rubuta su tare da tunanin mai karatu ɗan Afirka. Wannan aiki (na rubuta Magana Jari Ce) ya samu kammaluwa ne tare da taimakon malam Abubakar Kagara, (NAK/ANDIOZA, 1936).

Usman (2023) ya ruwaito cewa a wannan labari na Magana Jari Ce, Imam ya yi amfani da karin magana guda ɗari biyu da talatin (230) daidai, wasu a matsayin kanun ‘ya’yan labarun da kuma waɗanda ya saka a lafuzzan taurarin ‘ya’yan labarun da kuma waɗanda shi kansaya yi amafani da su a labarun da ya buɗe littafi na ɗaya da littafi na biyu da kuma littafi na uku. Karin magana ta yi tasiri sosai a matsayin wani ginshiƙin tubulin ginin labarin Magana Jari Ce.

Iya zancen hikima tamkar wanda ya mallaki uwar kuɗi ne a harkar kasuwanci. Kuma kamar yadda ba kowane mutum ba ne yake iya mallakar jari, haka nan ba kowane mutum ba ne yake da baiwar iya bayar da labari na hikima, shi ya sa masu iya magana suke cewa:

Wannan maƙalar ta tsakuro karin magana guda uku domin amfani da su a matsayin misalai.

4.1 ‘Munafuncin Dodo Ya Kan Ci Mai Shi’

Wannan shi ne labari na goma sha huɗu (14) a jerin ‘ya’yan labaran da aka bayar a littafi na ɗaya. Labarin yana ɗaukene da irin mummunan sakamako da mai ƙulla munafunci kan ci karo a ƙarshen al’amari. Gargaɗi ne ga suka wanda ya fahimci darasin da yake ƙunshe cikinsa. Idan dai kwaɗayin duniya mutum ya sa a gaba, to ba inda wannan kwaɗayin zai kai shi illa mahalaka kamar yadda aka gani gun waɗannan mutanen uku.

4.1.2 Ma’anar Karin Maganar Ta Sarari Da Ta Ɓoye

Munafunci mummunar ɗabi’a ce, Dodo kuwa halitta ce da Bahaushe ya yi imani da wanzuwar sa kafin zuwan addinin musulunci. Bahaushe ya kwatanta su ne saboda dukkansu daga ƙarshen al’amari halaka ma’abucinsu suke yi. Amma Bahaushe na amfani da karin maganar ne da nufin isar da gargaɗi ga duk mai irin wannan ɗabi’a ta munafunci da cewa koda ya ga yana cin nasara yayin da yake ƙulle-ƙullensa, to ya san da sani wata rana zai halaka yana ji yana gani kamar yadda Dodo yake hallaka mutumin da ya mallake shi yayin da ya kasa biya masa buƙatunsa. Wannan ayar ta nuna irin ayyukan da munafukai suke haɗin gwiwa da juna wajen saɓawa umurnin Allah mai girma da ɗaukaka. Saboda irin wannan aiki da suke aikatawa sai suka shagala da wanzuwar Allah, to haka shi ma Allah Ya manta da su baki ɗaya har zuwa ranar tashin ƙiyama. Har ila yau, wannan ayar ta bayyana yadda Allah Ya manta da masu wannan mummunar ɗabi’a wanda ya nuna tabbacin hasarar rahama da suka yi tun a duniya. Ita kuma wannan ayar da ta biyo baya, ta nuna ƙarara irin tanadin da Allah Ya yi wa munafukai maza da munafukai mata a ranar lahira. Wutar jahannama ce makomarsu kuma a can za su dawwama har abada.

4.1.2 Sharhin Labarin

Wannan labarin ya fito da illar munafunci a fili inda aka ga sakamakon ƙulle-ƙullen makirci saboda cutar da wani ya koma kan mai ƙullawa. Tun da farko waɗannan mutane guda uku ba amintattatu ba ne ga al’umma, abin da suka sa a gaba shi ne cutar da al’umma masu neman na kansu domin neman rufa wa kansu asiri. Babban darasin da aka koya a wannan labarin shi ne kar mutum ya sake ya bi son zuciya ko ya zama mai haɗama kan abin duniya. Waɗannan samari sun kasance mahandama da babakere wajen son abin duniya. Da a ce sun haɗiye haɗamarsu, kowa ya haƙura da abin da ya samu, da sun ci gaba da rayuwa, watakila ma su yi tunanin barin wannan muguwar sana’a, amma son zuciya ya kai su ga rasa rayuwarsu.

Shi kuwa Kaɗo dayake ba mugu ba ne, kuma Allah ya sa kuɗin duka rabonsa ne, sai ya dawo ya iske kuɗin cikin kwanciyar hankali, ya kwashe kayansa ya koma gida rayuwa ta canza duniya ta dawo sabuwa. Saboda haka, a kullum ana so zuciyar mutum ta zama tsarkakka cikin kyakkyawan tunani. Wannan ita ce mafita ga duk mai son ya samu alheri cikin rayuwarsa. Amma duk wanda ba shi da wata manufa sai ƙulla makirci da husuma a cikin al’umma, to babu makawa ƙarshensa zai kasance nadama ne wadda ba za ta amfane shi ba duniya da lahira. Waɗannan ɓarayi su uku, tun da farko ba su zaɓarwa kansu sana’a da za ta kai su gaci ba, sun ta’allaƙa ne kan cutar al’umma ta hanyar tare hanya su ƙwace musu dakiyoyinsu da duk wani abu da suka mallaka. A maimakon su yi amfani da ƙarfinsu su nemi halas, sai suka zaɓi amfani da ƙarfi su cutar da jama’a. Dayake duk mugun da bai yi mugunta wa kansa ba bai cika mugu ba, sai ga shi daga ƙarshe, sun ƙullawa junansu makirci wanda shi ne ya zama ajalinsu su ukun duka. Kamar yadda aka karanta, duk wanda ya ɗauki wannan mummunar ɗabi’a, to ko ya so ko ya ƙi, haka ko makamancin haka ƙarshensa zai kasance, kuma ya je lahira ya ci karo da fushin Allah maɗaukakin Sarki.

Akwai darussa masu muhimmanci a wannan labarin. Daga ciki akwai mai tayar da mutum daga barci musamman wanda ya kasance babu komai a zuciyarsa illa kwaɗayin tara abin duniya ta kowane hali. Rashin godiya ba abin koyi ba ne. Da waɗannan samari sun dangana da abin da kowa zai samu idan aka yi rabon nan to da sun sun tsira da rayukansu. Amma haɗama da mugun nufi sun ja masu hasarar dukiya da rayukansu. Allah Ya kyauta.

4.2 ‘Iya Gani Iaya Ƙyalewa’

Shi kuwa wannan labarin wani maharbi ne da ya iske wani maciji cikin halin ƙunci, wato dutse ya danne shi macijin kuma ya rasa yadda zai yi ya kuɓuta. Macijin ya roƙi wannan maharbi da ya taimaka masa ya ture dutsen nan domin ya kuɓuta daga halaka. Maharbin ya jinjina ya kuma koka kan halin halittun zamani, kar taimako ya zama ƙari. Macijin nan ya yi alƙawarin ba zai cutar da mutumin nan ba. Amma abin mamaki, ture dutsen nan da ke kan macijin nan yake da wuya, sai ya kawo wa maharbin nan sara da niyar ya kashe shi. Daga nan ne aka tafi neman alƙalan da za su yanke hukunci kan wannan rashinamana ta maciji.

4.2.1 Ma’anar Karin Maganar Ta Sarari Da Ta Ɓoye

Duk abin da bai shafe mutum, to mafi a’ala ya bar shi kar ya sake ya saka baki ciki. Saka baki a al’amarin da bai shafe ka ba na iya zama maka matsala ƙatuwa da za ta dame ka koma ta zame maka hanyar halaka. Zaman lafiya shi ne barin abin da bai shafe ka ba. Turawa ma suna da makamanciyar wannan karin maganar, ‘let a sleeping dog lies.

Hikimar Bahaushe a nan idan idon mutum ya kai kan wani abu da bai shafe shi ba, to duk yadda za a yi kar ya sake ya sa bakinsa aciki saboda ya tsira da mutuncinsa da kimarsa. Shiga harkar da ba ta shafi mutum ba al’amari ne mai haɗari sosai da zai iya kai shi asarar lafiyarsa ko ma ransa baki ɗaya.

4.2.2 Sharhin Labarin

Karya alƙawari wani mummunan aiki ne da zai iya jawo wa mai wannan hali shiga uku da sanewar amintaka daga wanda aka karya wa alƙawari koma al’umma baki ɗaya. A mafi yawan lokuta, son zuciya shi ke kai wasu su karya alƙawarin da suka ɗauka da kansu ba tare da an tilasta masu ba, amma kuma daga baya idan sun samu biyan bukatarsu, sai su rufe ido gam su karya alƙawarin da suka ɗauka da kansu. Wannan shi ne abin da ya faru a tsakanin maharbi da macijin da maciji. Maharbin nan yana kyakkyawar niyya game da macijin da ya samu dutse ya danne, amma shi kuma macjin sai ya kasance mai mai karya alkawari. A labarce, wannan labarin ya bayyana wa mai karatu ko sauraro irin mu’amala da ke akwai a tsakanin mutane da dabbobi. Doki da Biri sun bayar da munanan kalamai dangane da mutum, suna ganin maciji ya kashe mutum shi ne daidai saboda irin yadda suke ganin muguntar mutum. Amma sai cikon alƙali na uku, wato kare ra’ayinsa ya sha banban da na ‘yan uwansa, ya nuna hikima da sanin ya-kamata. Wannan hukunci da ya yanke shi ne ya kuɓutar da maharbi ya kuma koma da maciji angulu loma kan masheƙiya. Wannan wani saƙo ne da ya kamata duk wanda ya ji wannan labari ya ɗauki darasi, idan ka yi alƙawari, to ka cika koda kuwa akwai wata ƙulallaiya a tsakaninka da wanda ka yi wa alƙawarin domin ba a kan ƙulallaiyar ka ɗauki alƙawarin ba. Bugu da ƙari, labarin na nuna wa al’umma cewa duk abin da za ka yi, to ka yi saboda Allah, shi kuwa Allah zai taimake ka ta inda ba ka zato.

5.1Alheri Danƙo Ne Ba Ya Faɗuwa Ƙasa Banza’

Wannan kuwa labarin wani saurayi ne mai son aikata alheri. A kullun hannunsa a sake yake wajen kyautatawa al’umma. Ya gaji dukiya mai yawa daga mahaifinsa, Allah kuma ya nufe shi da zama inuwa ga kowa da kowa . Alherinsa na zuwa ga duk wanda Allah ya ciyar ba sai wanda ya sani ba. Har fatake yake nemowa daga kan hanya ya kawo su gidansa ya ciyar da su. Wannan aikin alherin da ya gudanar da dukiyarsa, ya jawo masa alherin da ba ya lissafuwa.

5.1.1 Ma’anar Karin Maganar Ta Zahiri Da Ta Ɓoye

Wannan karin maganar tana nuna cewa duk wanda ya aikata aikin kirki to babu shakka zai samu kyakkaywan samakamako a rayuwarsa.A wannan karin maganar, Bahaushe ya kwatanta alheri da danƙo. Danƙo dai wani abu ne da ake amfani da shi wajen liƙe abu biyu a waje guda. Idan danƙo ya faɗi a ƙasa, ba za a iya ɗakko shi ba ba tare da ya ɗebo ƙasa a jikinsa ba. Hikimar Bahaushe a nan ita ce duk mai aikata alheri, daidai yake da yadda danƙo yake, wato aikin nan da ya yi na alheri ba zai tafi a banza ba, sai ya samu mafi kyawun sakamako abin da alherin da ya fi aikin alherin da ya yi. Ana amfani da wannan karin maganarwajen ƙarfafa gwiwar al’umma da ta kasance masu aikata kyawawan ayyuka domin ci gaban al’umma.

5.1.2 Sharhin Labarin

Labarin nan ya taɓo irin sakamakon da duk wani mai aikkata alheri yake samu. Hassan dai tun da Allah ya sa ya samu mallakar dukiyar da mahaifinsa ya bar masa a matsayin gado, ya nuna halin tausayi ga marasa shi. Kullun tunaninsa shi ne ta wace hanya ce zai taimakawa mabuƙata. Ko lokacin da ‘yan uwansa suka nemi su ba shi tsoron da talauci, bai girbiza ba, ya ci gaba da taimakon da ya saba. Abokansa sun amfana da dukiyar da Allah ya ba shi. Dayake Allah na iya gwada bawansa a duk lokacin da ya so, ya kuwa gwada Hassan da karayar arziki, duk dukiyarsa ta ƙare, ya shiga halin ƙaƙa-ni-ka-yi. Abokai da dangi duk suka watse suka bar shi cikin talauci kamar bai taɓa mallakar ko sisi ba.

Allah mai yin yadda ya so a lokacin da ya so, ya sake buɗawa Hassan wata kafar arziƙin, suniya ta dawo sabuwa. Lokacin da ya ga Allah ya maido masa da arziƙinsa, sai ya yanke shawara ya sake matsuguni tunda ya ga yadda mutanen garinsu suka juya masa baya a lokacin da dukiyarsa ta karye. Da ya sake gari kuma bai fasa abin alherin da ya saba ba. Ya kan gayyato fatake ya ciyar da su. Aikin alherin nan da yake yi ne ya jawo hankalin Sarkin wannan ƙasa, suka zo shi da wazirinsa suka ga irin taimako da Hassan yake yi wa al’umma. Shi kuwa Hassan bai san ko suwaye ba. Aikin alherin nan ne ya jawo Sarki ya naɗa shi wawan Sarki, ya samu ɗaukaka a wajen Sarki da jama’ar ƙasa baki ɗaya.

Karin maganar ta yi daidai da ƙumshiyar labarin idan aka yi la’akari da halin kirki da aka gani a wajen Hassan. Kyauta da taimakawa mabuƙata a duk lokacin da Hassan ya samu dama ta zama hanyar rufin asirin da Allah ya ba shi da ɗaukaka fiye da shi abin da ya kasance yana yi wa jama’a.

Hausawa na cewa ‘Alheri gadon ƙaya.’ Duk mai aikata alheri tabbas zai ga sakamako mai kyau ko ba-daɗe, ko ba-jima. Idan dai Allah Ya taimake ka ka zanto mai kyakkyawar zuciya, ka zama babu abin da yake cikin zuciyarka illa taimakawa mai neman taimako, to ka sha kuruminka, in Allah Ya so daga ƙarshe sai ka ga sakamakon alheri ya zo maka a lokacin da ba ka zaton hakan. Wannan ne ya faru da Hassan. A yayin da ya dage wajen aikin alheri, tun yana ainihin garinsu, har ‘yan uwansa ma sun so su raba shi da taimakon mabukata, amma ya ƙi. Allah Ya jarabce shi da karayar arziƙi, ya zamanto ba shi da komai, abincin da zai ciyar da iyalinsa ma babu. Ya zama abin zunɗe a wajen ‘yan uwa da abokai. Kwatsam sai Allah Ya sake buɗa masa wata hanyar. Karayar arziƙi da ya samu a baya ba ta hana shi ci gaba da taimakon mabukata ba, amma sai ya sake gari domin ganin yadda mutanen garinsu suka kasance masu yi masa dariya a lokacin da ya samu karayar arziƙi. Hassan ya ci gaba da taimakon al’umma a garin da ya koma har ma hukuntan garin suka san ahlin kirkin da yake aikatawa a garin. Wannan ne ya jawo Sarkin garin ya kusance shi domin ya ga irin aikin alherin da Hassan yake yi da idanunsa. Ganin yadda Hassan yake taimakawa al’umma ne ya sa Sarkin ya jawo shi a jika har ma yi masa sarauta a garin. Haka masu iya magana suka ce ‘Idan Allah Ya taimake ka kaikuma ka taimaki na baya gare ka.

6.1 Naɗewa

Babu shakka Imam ya yi bajinta wajen fito da manufar Bahaushe dake ƙumshe cikin karin maganarsa ta amfani da su a matsayin tubalin ginin labarinsa mai ƙumshe da tarbiyya da nasiha da gargaɗi da hangen nesa ga al’umma cikin raha da annashuwa.Wannan dabara ta taimaka wajen ƙara fito da martabar harshen Hausa a idon duniya musamman ta fuskar adabi da harsunan al’ummomin duniya ya zama ɗaya daga cikin sanadin da harshen Hausa ya samu gindin zama a tsakanin manyan harsunan nahiyar Afirka.

Wannan salo da Imam ya yi amfani da shi, ba haka kawai ya ƙirƙiro shi ba, yana da manufa, manufar kuwa ita ce ya ankarar da al’umma irin muhimmancin da karin magana take ɗauke da shi a gare su ta wajen tsaftace zamantakewa da faɗakawa da kuma nishaɗantarwa. Imam ya fito da kyawun tunani dake ƙunshe cikin harshen Hausa a dunƙule masu ɗauke da kyawawan manufofi da suke gyara halin mutum da kuma maganganun dake tsoratar da duk wani mai aikata laifi a sarari ko a ɓoye. Haka kuma akwai karin maganar dake ƙoƙarin ƙarfafa gwuiwa da zaburar da al’umma cewa babu wani abin kirki da yake samuwa sai fa idan an tashi tsaye da nema. Akwai misalai da yawa da za a iya hakaitowa a cikin labarin musamman waɗanda suke ɗauke da kanun karin magana.

 Idan an fahimci karin maganar da Imam ya yi wa labarin kanu da shi, wato ‘magana jari ce,’ sai a ga cewa ko shi kansa Imam ɗin, ya cancanci a jingina wannan karin magana da shi. Dalili kuwa shi ne iya maganar ne ya zama silar ɗaukakar da Allah Ya ba shi. Tarinsa ya nuna shi haziƙi ne tun kafin ma ya shiga makarantar boko, wato tun lokacin da yake gaban mahaifinsa a garinsu Kagara. Ya yi karatun addini mai zurfi a gaban mahaifinsa inda har harshen Larabci ya koya. Hazaƙarsa ne ma ta sa aka ɗauki shi aikin malanta a yayin da ya kammala makarantar sakandare ta Katsina a matsayin malamin harshen Ingilishi. Imam mutum na farko da masaurautar Katsina ta naɗa a matsayin sakataren majalisar sarkin Katsina.

 


 

Manazarta

Abdullahi, I.M. (1995) “Wasu Tubalan Ginin Littafin Magana Jari Ce”, Sashen Harsunan Nijeriya, Jami’ar Usman Ɗanfodiyo, Sakkwato.

Amin, M.L. (2002) “Hausa Metaphysical World Ɓiew’: A paremeological Eɗpression. An unpulished Ph. D Thesis submitted to the Department of African Languages and Cultures, A.B.U.Zaria.

C.N.H.N (2006) Ƙamusun Hausa. Kano: Jami’ar Bayero.

Hassan S. (2012) “Ba a mugun Sarki sai migun bafade’ Tsokaci daga Magana Jari Ce no 3 (There is no wicked King but a wicked courtier) Fiescript in honour of Professor Ɗalhatu Muhammad Zaria. Department of African Languages and Cultures, Ahmadu Bello University, Pp 376-386.

Imam, A. (1980) Magana Jari Ce. Zariya: Northern Nigerian Publishing Company.

Imam, A. (1946) Tafiya Mabuɗin Ilimi: Zariya: Northern Nigerian Publishin Company.

Jami’ar Bayero Kano (2013) Sababbin Kalmomi: Ingilishi zuwa Hausa, Littafi Na Biyu. Zaria: Ahmadu Bello University Press Limited.

Jez, B. (2003) Foreign Influences and their Adaptation to the Hausa Culture in Magana Jari Ce by Abubakar Imam in Studies of the African Languages and Cultures, No 33, 2023, Stanislaw Pilaszewicz, University of Warsaw.

Mahuta, I. (1980) “Nason Alfulaila wa laila cikin adabin Hausa, misalai daga Magana Jari Ce. B.A. Hausa Usman Danfodio University, Sokoto.

Malumfashi, I. (2009) Adabin Abubakar Imam. IBM Printers, No 11 Muri Road,Kaduna.

Malumfashi da Marafa (2014) Ƙamusun Karin Maganar Hausa. Garkuwa Publishers, Kaduna, Nigeria.

Mora, A. (1989) (ed): Abubakar Imam’s Memoirs. Zaria: Northern Nigerian Publishing Company.

Musa, A. (1993) “Karin Maganar Magana Jari Ce, Kundin Neman Digiri Na Farko, Sashen Harsunan Nijeriya da Afirka, Jami’ar Ahmadu Bello, Zariya.

Suleiman, I.I. (1990) “Morality in Imam’s Magana Jari Ce, A Departmental Seminar Paper at Department of Nigerian and African Languages, Ahmadu Bello University, Zaria.

Usman, M. (1998) “Tarsashin Adabin Baka A Magana Jari Ce, Kundin Digirin Tsakiya, Sashen Harsunan Nijeriya da Afirka,Jami’ar Ahmadu Bello Zariya.

Usman, M. (2014) “Man as A Greedy Being: A case study of some stories in Magana Jari Ce. Journal of Liberal Arts, Department of Nigerian Languages, Kaduna State University,Kaduna.

Usman, M (2023) “Karin Magana A Tunanin Bahaushe Nazari Daga Magana Jari Ce Na Abubakar Imam. Sashen Harsuna Da Aladun Afirka, Jami,ar Ahmadu Bello Zariya

Wali, Z.N. (1976) “Nazari A Kan Littafin Magana Jari Ce. Kundin Digirin Farko,Sashen Harsunan Nijeriya, Jami’ar Bayero, Kano. 

 Rataye

 Litafi na 1.

1. Magana jari ce

2. Ba a fafe gora ranar tafiya 

3. Magana jar ice

4. Matambayi ba ya ɓata

5. Gobe ma rana ce

6. Baƙo da Tukura duka Umbutawa ne

7. Baya ba zane

8. Ana tsoron Inna in ji ‘ya’yan mayya

9. Banza ta koriwofi

10. Gani ga wane ya ishi wane tsoron Allah

11. Allah abin tsoro, mutum ma abin tsoro n

12. Rai dangin goro ne, ban iska yake so

13. Da Tukura da Baƙo duka Umbutawa ne

14. Ta faru ta ƙare, an yi wa mai dame ɗaya sata

15. Sauri ya haifi nawa

16. Wayon a ci an kori kare daga gindin ɗinya

17. Mai hali ba ya barin halinsa 

18. A bar kaza cikin gashinta 

19. Zuwa da wuri ya fi zuwa da wuri-wuri

20. Gaba siyaki baya damisa

21. Yau da gobe ba ta bar kome ba

22. Ta faru ta ƙare, an yi wa mai dame ɗaya sata

23. Kowa ya daka rawar wani ya rasa turmin daka tasa

24. Kau-da-bara ba ta ci sai an haɗa da gociya

25. So hana ganin laifi

26. In ajali ya yi kira ko ba ciwo a je

27. Kunar baƙin wake

28. Gani ya kori ji

29. Duk abin da mutum ke aikatawakomai daɗewa zai ga sakayya

30. Kome ka shuka shi za ka girba

31. ‘Yan zamani sanin ku ba sanin halinku ba

32. Abin da ya yi Goje, shi ya yi Ƙaura

33. Mai rai ba ya rasa motsi

34. Cin danƙo har da su kaza

35. Dabara ita ce yaƙi ba ƙarfi ba 

36. Sarkin yawa ya fi Sarkin ƙarfi

37. Sarkin yawa ya fi Sarki ƙarfi

38. Soyayya gamon jini 

39. Tsohon doki sai mai shi

40. Ungulu ta koma gidanta na tsamiya

41. Ba a san inda rana za ta faɗi ba

42. Aikata alheri ga kowa sakayyarka na gun Allah

43. Raina kama ka ga gayya

44. Raina kama ka ga gayya

45. Ɗan hakin da ka raina shi ke tsole ma ido

46. Ɗan-Adam tara yake bai cika goma ba

47. Baki shi kan yanka wuya

48. Abin da ya ci Domaba ya barin Awai.

 Littafi na 2

 Ƙarfe duka ƙarfe ne amma ko cikin karafaakwai azurfaakwai tagulla

 Maza dangin gujiya ne sai an fasa akan san bidi

 3 In an bi daga-daga, na ƙurya ka sha kashi

 In laila ta ƙiya sai a koma basha

 Cin ƙwan makauniya

 Ta safe ta raggo, in safiya ta yi sai mu mutanen Sarki

 7. Da muguwar rawa gwamma ƙin tashi

 8. Ba kullun ake kwana a gado ba

 9. Gidan ma-ƙi-gudu da kara a kan nuna

 10. Gani ya kori ji

 11. Me ya raba dambe da faɗa?

 12. Dare ɗaya Allah ka yi Bature

 13. Kowa ya bar gida gida ya bar shi 

 14. An yi ba a yi ba kenan, juyin gatar fara

 15. Sa’a ta fi manyan kaya

16. Akwai ranar ƙin dillanci, ranar da akuyar mai gari ta ɓata

17. Abokin ɓarawo ɓarawo ne

18. Bakin da Allah Ya tsaga ba Ya hana mashi abinci

19. An ƙi cin biri an ci dila 

20. ɓoye wa abokin kuka mutuwa? 

21. A bari ya huce shi ke kawo rabon wani

22. Me ya gama kifi da kaska?

23. Zaman duniya iyawa ne, kowa tasa ta fisshe shi

24. Zato zunubi ko da ya zama gaskiya

25. Ɗan kaciya in bai ci kaza ba, ai ba ya yin bara

26. Sata gidan ɓarawo rance

27. Kowa da kiwon da ya karɓe shi, maƙwabcin mai Akuya ya sai kura

28. Ana zaman ƙarya, baƙauye ya zo birni ya tambayi masussuka an ce babu

29. Ka zama dungu, a bar ka ana ƙyamar ka, a yanke ka ba a samun sabo

30. In ka ji makaho ya ce a yi wasan jifa, ya taka dutse ne

31. Kora da hali ya fi kora da kara

32. Ruwa baya tsami banza

33. Yaro da gari abokin tafiyar manya 

34. Ko kura ta tsufa ta fi gaban kare

35. Ba kullun ake kwana a gado ba

36. Baki shi kan yanka wuya

37. Rashin sani ya fi dare duhu

38. Ƙuda wajen kwaɗayi a kan mutu

39. Wuri ya ja wuri

40. Kwaɗayi mabuɗin wahala

41. Allura ta tono garma

42. Kowa ya ɗebo da zafi bakinsa

43. Kowa ya yi ƙaryar dare gari zai waye 

44. Baki shi kan yanka wuya

45. Ta faru ta ƙare an yi wa mai dame ɗaya sata

46. Ba kullun ake kwana a gado ba

47. Allah Ya yi masa gyaɗar dogo

48. Banza ba ta kai zomo kasuwa

49. Raɓa na raukar raɓa

50. Akwai ranar ƙin dillanci ranar da hajjar mai gari ta ɓata

51. Ana wata ga wata, ana kuɗin ƙasa gari ya watse

52. Ba a mugun Sarki sai mugun bafade 

53. An yi gudun gara an faɗa zago

54. Kama da wane ba wane ne ba

55. Ta Malam ba ta wuce amin

56. Na gaba ya yi gaba na baya sai labari 

57. Komai ta tafasa ta ƙone

58. Sarkin yawa ya fi sarkin ƙarfi

59. Ba kullun rana take Juma’a ba

60. Hankali ke gani ido gululu ne

61. Abin da ya koro ɓera ya faɗa wuta ya fi wutar zafi

62. Mahaƙurci mawadaci

63. Yau da gobe sai Allah

64. Mahaƙurci mawadaci

65. Komai ta tafasa ta ƙone

66. Bayan wuya sai daɗi

67. Gaba da gabanta maibaggu ya ga haƙorin uwarzana

68. Kunne ya girmi kaka

69. Kowa ya bar naman kura ba zai sa kura ta bar nasa ba

70. Son a sani yaji da kwarin miji

71. Gajin haƙuri shi ya kawo mai aka shuka

Littafi na 3

1. Magana jari ce

2. Aiki da zato zunubi ne ko ya zama gaskiya

3. Girma da arziƙi ita ta sa jan sa da abawa

4. Bara na yi wake bana na yi harawa 

5. Yaro ko da ganin birni ya san ya fi garinsu

6. Kada kaza ta yi murna don ta ga ana jan hanjinyar uwa tata

7. Jifa in ta wuce kanka ko kan wa ta faɗ

8. Hauka da naɗe-naɗe, mutuwa ta ga ladan

9. Idan bori gaskiya ne ya faɗa rijiya

10. Kashin birbiri da faɗuwa da naɗewa 

11. A bar kaza cikin gashinta

12. Ɓatan ɓakatantan

13. Na san a rina, an saci zanen mahaukaciya

14. Ba rabo ba, ɗan wabi ya mutu

15. Na san a rina an saci zanen mahaukaciya

16. Girman kai rawanin tsiya

17. Rabo rababbe, tsuntsu daga sama gasasshe

18. Gaba damisa baya siyaki

19. Da muguwar rawa gwamma ƙin tashi 

20. Sauri shi kan haifi nawa

21. Zuwa da wuri ya fi zuwa da wuri-wuri 

22. Tsintar dami a kala

23. Ba ta rinu ba ta yi shuɗi

24. Yi wa shakiyyi shakiyanci gyaran akayau ne

25. Yau ci nan sha nan kura ta kashe mai gwaiwa

26. Shan ruwa ya fi barinsa

27. Akwai ranar ƙin dillanci ranar da akuyar mai gari ta ɓata

28. Wuri ya ja wuri

29. Zomo ba ya fushi da makashin sa sai maratayi

30. Kowa ya ci ladan kuturu dole ya yi masa aski

31. Munafunci dodo ya kan ci mai shi

32. Komai ta fanjama fanjam

33. Baki shi kan yanka wuya

34. Mai rabon shan duka ba ya jin kwaɓo sai ya sha

35. Mayar da mashi ran gaba tsoro ne 

36. Ramuwar gayya ta fi gayya zafi

37. Tsugune ba ta ƙare ba an sayar da kare an sai biri

38. Tsuntsu mai wayau a ƙoto ake kama shi

39. Rama cuta ga macuci ibada

40. Idan mutum ya ce zai haɗiye gatari sai a sakar masa ƙota

41. Da hannu kan san girma

42. Ƙashin bakin tukunya ka shiga ka ƙi fita

43. Tsintattar mage ba ta mage

44. Zomo ba ya fushi da makashinsa sai maratayinsa

45. Ga ƙoshi ga kwanan yunwa

46. Tsuguni ba ta ƙare ba an sai da kare an sai biri

47. Dalilin kaza kaɗangare kan sha ruwan kasko

48. Sa’ar Sarki ta fi fatauci, ta ko fi a duka gona noma

49. Rasin sani ya fi dare duhu

50. Garin baƙo kowa Sarki

51. Duk ƙoƙarin kura yana ga haƙoranta

52. Kora da hali ta fi kora da kara

53. Gamo da Katar

54. Zato zunubi ko ya zama gaskiya

55. Mai arziƙi ko a kwara ya sayar da ruwa

56. Yaro da gari abokin tafiyar manya 

57. Taron Kwara da Ama

58. Da birin da ke dawa da wanda ya yi makuwa duk dawa za su kwana

59. Riga-kafin mugunta rashin yi wa wani 

60. Randa kina ɗaka Allah na ba ki ruwa ki sha

61. Duk wanda ya ji ƙan wani Allah Ya ji kan sa

62. Mutum dangin gwanda ne, ba ya jimirin zungura

63. Kowa ya ce yana iya haɗiye gatari sai a sakar masa ƙota

64. Bakin da Allah Ya tsaya ba Ya hana masa abinci

65. Duk bori ɗai ake wa tsafi

66. Tsuntsu duka dai na cin kashi amma na angulu ake gani

67. Cin danƙo har da su kaza

 Yobe Journal of Language, Literature and Culture (YOJOLLAC)

Post a Comment

0 Comments