𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Yaya Matsayin Alƙunutu Da ake Karantawa Asallar Asubahi? Shin Wajibi ne Sai Mutum ya yi Ko Liman Yana ɗaukewa mamu?
AL-ƘUNUT A SALLAR ASUBA
𝐀𝐌𝐒𝐀❗
Alƙunuti sunnah ne na
addu'a da ake yi awani bigire kebantacce na tsayuwa wanda aka shar'anta asallar
wutiri bayan dagowa daka
ruku'u a bisa zance
ingantacce cikin zantukan Malamai.
Ana yin Alƙunutu idan wata
masifa ko bala'i ya aukawa Musulmai sai su dunga addu'a bayan dagowa daka
ruku'u akowacce raka'ar karshe ta sallar farillah guda biyar, Har Allah ya yaye
musu wannan bala'i daya auka musu yadauke musu shi. Duba littafin (Tas-heehi
du'aa'i na Shaik Bakar Abu Zaid shafi na 460)
Amma yin Alƙunutu ko da yaushe
Asallar asuba bai inganta daka Annabi sallallahu Alaihi wasallam ya keɓance sallar asuba
yana alƙunuti a cikinta ko da yaushe ba, Abin da yatabbata daka
gareshi shi ne yana yin Alƙunutu idan wata masifa tasauka, ya yi alƙunutu asallar asuba
dasauran salloli yana yi wa ZAKWAAN DA USAYYAH mummunar addu'a saboda kashe
mahaddata Alƙur'ani dasu kai wadanda Annabi (Sallallahu Alaihi
Wasallam) yaturasu zuwa garesu dansu sanarda da su addinin musulunci, yatabbata
ya yi ƙunuti asallar asuba yana rokawa raunana daka cikin
muminai dabasu samu damar yin hijiraba saboda rauninsu Allah yakubutar da su daka
Abokan gabarsu, bai dawwama akan hakan ba, halifofi shiryayyu suka tafi akan
haka abayansa, Abin da yake alheri ga limamai shi ne sutakaita dayin Alƙunutu asallar asuba
dama sauran salloli sai dai idan wata masiface ta aukawa musulumi, anan
yahalatta aita Alƙunuti har Allah yayewa Musulmi wannan masifar. Kamar
yanda hadisinda Asha-bul Sunan suka ruwaito banda Abu dauda daka Abu malik
Al'Ashja'iy Allah ya kara masa yarda. Albani ya Ingantashi a cikin Irwa'u (435)
Mafificiyar shiriya ita
ce shiriyar manzan Allah
sallallahu Alaihi
wasallam. fatawa lajnatul da'imah (7/47)
Sannan ba a iyakance
wata addu'a damutum
zai yi A'alƙunuti na wata masifa
da ta samu Musulmai ba, liman zai yi addu'a wacce tadace dahalin da ake ciki da
kuma masifar kamar yanda aka ruwaito Annabi sallallahu Alaihi wasallam ya
tsinewa wasu kabilun dasuka bijirewa sahabbansa suka kashesu, da kuma rokawa
raunana da suke makkah Allah yakubutar dasu. Amma Akwai wasu sigogi da'aka
ruwaito Annabi sallallahu Alaihi wasallam da shabbansa sun yi a addu'ar ƙunuti a cikin sallah
kamar yanda baihaiƙi yaruwaito (2/210) Albani ya ingantashi a cikin Irwa'u
(2/170).
Yahalatta kayi alƙunuti da addu'a
takashin kanka kamar yanda Imamun Nawawi yabayyana a cikin Almajmu'u dinsa
(3/497).
Dan samun karin
bayani za ka iya yin wacce aka ruwaito sannan kakara dataka duba (ƙiyamu ramazhan na
shaik Albani (31)
Hadisai da'aka
ruwaito akan alƙunuti da kuma
ingantaccen zance na
malamai shi ne ana yinsa bayan dagowa daka ruku'u idan kayi kafin tafiya ruku'u
babu komai kana da zabin idan kagama karatun sallah kayishi kafin tafiya ruku'u
sannan za ka iya yin ruku'u idan kadago saikayi alƙunutin. Kamar yanda
shaik Usaimeen yabayyana a cikin Sharhin Mumti'i Ala zhadul mustaƙni'i ( 4/64)
Dan haka yin Alƙunuti asallah baya
kan mamu,
liman ne ke haƙƙin yinsa, shi mamu
zaidunga Ameen ne lokacinda liman yake addu'ar
Alƙunutin.
Alƙunuti wanda muka
tashi mukaga ana yi akasar nan kowacce sallar asuba da kuma siga daya dasunan
mazhabar malikiyyah bidi'ane bai tabbata daka Annabi sallallahu Alaihi wasallam
ba.
Asalin Alƙunutu asallar asuba
malamai sun yi saɓani akansa akwai
wadanda suke ganin shar'antuwarsa kamar malikiyyah da shafi'iyyah, akwai
wadanda ba sa ganin shar'antuwarsa kamar Hanafiyyah da Hanabila.
Ibnu ƙudama rahimahullah a
cikin Almugni ( 1/449) Yace: Ba sunnah ba ne alƙunutu asallar asuba
ko watanta daka cikin salloli, inba wutiriba, haka Assauri ya ce da Abu hanifa,
haka aka ruwaito daka ibnu Abbas, da Abdullahi Ɗan Umar da Ibnu
mas'ud da Abul dar-daa'i.
Malik da Abi laila da
hasan bin salih da shafi'i sukace: Sunnah ne yin alƙunutu asallar asuba
adukkanin zamunnah domin Anas yace: ( Manzon Allah sallallahu Alaihi wasallam
baigushe ba yana alƙunutu asallar asuba har ya bar duniya) Imamu Ahmad a cikin
Musnad ɗinsa.
Umar ya kasance yana
Alƙunutu
agaban sahabbai da wasunsu. Da Abin da aka ruwaito Annabi Sallallahu Alaihi
wasallam ya yi alƙunutu tsawon wata guda akan wasu larabawa rayayyu sannan
yadena. Muslim.
Abu huraira yaruwaito
irin wannan hadisin daka Annabi Sallallahu Alaihi wasallam, ( Annabi Sallallahu
Alaihi wasallam ya kasance baya alƙunutu asallar asuba sai
dai idan zai yi wa wasu mutane addu'a ta alkhairi, kozai musu addu'a mummuna.)
Alƙunutun Umar ya kasance
lokacin saukar musibu domin mafiya yawan ruwayoyi sunzo akan baya alƙunutu, jama'a da yawa
sunruwaito haka daka gareshi, wannan yake nuna baya alƙunutu sai a lokacin
saukar musiba. Mausu'ah fiƙ-hiyyah ( 34/58).
Tare dacewa magana mairinjaye
ita ce: Baya halatta yin alƙuntu asallar asuba ko da yaushe sai
dai idan masifa tasauka, Sai dai babu laifi dankayi sallah abayan wanda yake alƙunutun asallar asuba ɗin, dayin Ameen a
addur'asa.
Shaikul Islam ibnu
taimiyyah rahimahullah yace: Idan mamu yabi limamin dayake alƙunutu asallar asuba
ko sallar wutiri zai yi ƙunuti tare da shi, yana alƙunutunne kafin ruku'u
ko bayan ruku'u. idan baya alƙunuti ba zai yi ba.
Koda liman yana ganin
Mustahabbancin wani abu, mamu kuma baya ganin hakan sai ya barshi dan samun
haduwar kai da hadewa yakyauta, Maj-mu'u fatawa (22/ 268).
Dan haka dai lazimtar
yin alƙunutu ko da yaushe asallar asuba ba sunnah ba ne, sai dai
idan wata matsala ta tunkaro Musulmi ko wani bala'i sai aita alƙunutu harsai Allah
yakau da wannan matsalar.
WALLAHU A'ALAM
Zauren Tambaya Da
Amsa a bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ga Masu Buƙatar Shiga Wannan
Group za ku iya bi ta Links ɗin mu...
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.