𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Malam mene ne hukuncin wanda yake wasa da azzakarinsa maniyyi ya fito? Ko Kuma matar da take sanya yatsa a cikin farjinta? Malam gaskiya Allah ya jarrabe ni da wani halin wasa da gabana lokacin da na ji sha'awa takamani. Yau nakai shekara biyu ina yinsa Na yi kokarin dainawa daga nadaina kwana biyu zan koma.
𝐀𝐌𝐒𝐀❗
Alal-Haƙiƙa wannan wata Mas'alace
da ana iya cewa ta yawaita sosai awannan zamanin,
musamman tsakanin Samari da 'Yammata,
harma da Matan-Aure da kuma Mazan-Aure.
Yin haka bai halatta
ba kuma yana daga cikin manyan laifiu a musulinci. Yana janyowa mai yin hakan
fushi da kuma tsinuwa daga ubangiji ( S.W.A).
Ibnu Katheer
Rahimahullah ya ce Imamush-Shafi'i da waɗanda suka goyi bayansa ya kafa hujja da
haramcin wasa da gaba da faɗin Allah maɗaukakin Sarki:
وَالَّذِينَ
هُمْ لِفُرُوجِهِمْ حَافِظُونَ إِلَّا عَلَىٰ أَزْوَاجِهِمْ أَوْ مَا مَلَكَتْ
أَيْمَانُهُمْ فَإِنَّهُمْ غَيْرُ مَلُومِينَ فَمَنِ ابْتَغَىٰ وَرَاءَ ذَٰلِكَ
فَأُولَٰئِكَ هُمُ الْعَادُون
Bayin Allah nagari
Sune waɗanda dangane da
farjinsu suke kiyayeshi. Face a kan matan aurensu, ko kuwa abin da hannayen damansu
suka mallaka (kuyanginsu) to lalle sũ ba waɗanda ake zargi ba ne. Saboda haka wanda ya
nemi abin da ke bayan wancan, to, waɗancan sũ ne masu ƙetarewar haddi.
(Suratul Mũminun 5-7)
Imamush-Shafi'i a
cikin littafin Aure ya ce sai ya kasance Allah ya bayyana kiyaye farjin su sai
fa a kan matayen su ko abin da damar su ta mallaka, sai ya zama haramun idan ba
matar ka ba ce ko kuyangar ka sai Allah ya karfafi maganar da cewa " wanda
ya nemi koma bayan hakan yana cikin masu taka dokokin Allah"
Bai halatta amfani da
azzakari ba sai a kan matar ka baiwar ka, bai halatta jin daɗi da shi da hannu ba
wallahu A'alamu kitabul ummu na imamu shafi'i.
A Sunnah kuwa sun
kafa hujja da hadisin Abdullahi dan mas'ud Yardar Allah ta kara tabbata a gare
shi yace: Mun kasance tare da Annabi sallallahu Alaihi wasallam muna samari ba
mu samu komai ba sai Annabi sallallahu Alaihi wasallam ya ce damu "ya ku
taran samari duk wanda ya samu halin ɗaukar dawainiyar iyali ya yi aure, domin ya
nasa kamewa daka gani, yana kuma tsare farji, wanda kuma bai samu dama ba to na
hore shi dayin azumi domin azumi yana kariya daka faɗawa haram. Bukhari
5066.
Sai shari'ah ta
shiryar lokacin da mutum ya gajiya wajen yin aure sai ya dunga azumi domin
azumi yana kariya daka faɗawa haram. Bukhari
5066.
Manzon Allah
(Sallallahu Alaihi Wasallam) yana cewa "Mutum bakwai, Allah ya tsine mu
su. Kuma ba zai dube su da rahama ba ranar al-ƙiyamah. Zai ce mu su
Ku shiga wuta tare da masu shigar ta:
1. Wanda yake yin
luwaɗi
2. Wanda ake yin Luwaɗin da shi
3. Mai yin zina da
dabbobi
4. Mai yin zina da
Uwa/Mahaifiya
5. Mai yin zina da
'yar ta
6. Mai yin zina da
hannayensa (wato mai yin wasa da azzakarinsa da kuma....
7. mace mai yin hakan
ga al'aurar ta)
sannan shi kuma
wannan aiki yana daga cikin irin laifukan da mutanen Annabi Lut ( A.S) suka
aikata. Sannan kuma an Ruwaito cewar duk masu yin hakan idan har basu tuba ba.
za su tashi a ranar al-ƙiyamah Hannayen su ɗauke da ciki ( wato juna biyu)
Sannan kuma Likitoci
masu ilimin sanin lafiyar jikin Bil-adama sun fadi wasu illoli da dama wadan da
yin hakan yake haifarwa:
1. Zai sa Gabanka Ya
Koma Ɗan Karami Kamar Na Kananan Yara. Ko da daga baya idan
kayi Aure. Ba za ka iya Cika Mace Ba. Sabida Jijiyoyin Wannan Gaban Naka za su Saki.
za su Sami Disfunction.
2. Zai ɗauke Maka Karfin
Sha'awar da Allah ya Halicceka Akan ta. za ka zama Baka da wani Sha'awa Na
Mace. Duk ka tafiyar da Sha'awarka kai kaɗai.
3. za ka Sami Ƙuick Release. Ma'ana
Saurin Kawowa. Idan kayi Aure Ba za ka iya Gamsar da Matarka ba. Domin Nan da
nan za ka ke Kawowa, ko Second Ukku Ba za ka iya yi ba. Daga nan Kuma ka Gama.
Domin Ba za ka iya Komawa Ga Matarka ba. Wanda a Dabi'a Ansa Namiji da Komawa
na biyu wani ma har na Ukku. Sabida Faɗin Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam
inda yake Cewa idan ɗayanku ya biya bukatarsa
ga matarsa, sannan yake nufin zai sake komawa karo na biyu, sai ya yi alwala
bayan karo na farko ɗin, kafin ya koma ba
biyun. Malamai Suka Ce, Sabida Hakan Yana samarwa Namiji Nishaɗi. Ka Gwada ka Gani.
za ka Tabbatar da hakan In sha Allah.
4. Lalataccen Maniyyi
zai Daskare maka a Cikin Mararka. A haka zakake ta yawan ciwon Mara. Domin
Wannan Maniyyin da yake fitowa da Daidai lokacin da kake yin Istimna'in Domin
Biyan Bukatar Kanka da kanka, baya Fita Gabaki ɗaya, Sannan Kuma Ba zai Koma Asalin
inda Aka Halicceshi ba. Sabida haka ke nan Zai Tsaya Maka a Mararka. Sabida
haka zai Baka Matsala ba Karama ba.
5. Rashin haihuwa:
wannan daskararren maniyyin yana kashe kwayoyin halitta daga jikin Namiji ko
Mace.
6. Mantuwa mai
tsanani ( mantuwar karatu e.t.c)
7. Raunin idanu masu
yin hakan idan basu daina ba, suka makancewa kafin wani lokaci mai nisa.
8. Ciwon hauka da
Kuma kaskanci.
Wannan kaɗan na tsakuro daga
cikin irin illolin da yake haifarwa. A jikin Namiji ko Mace.
Duk wanda ya saba
Aikata Irin wannan Al'amari yana tattare da waɗannan Matsalolin da na Ambato. Kuma
Tabbas Sai Bayan Aure Mutum zai Tabbatar da Waɗannan Abubuwa da na Lissafo Su. Sabida
haka idan har baka yi Nisa ba. To Kayi Gaggawar Denawa. Shi ne Abin da Ya fi
Alkairi a gareka. Tin kafin ka Tsinci kanka Tattare da waɗannan Matsaloli da na
Kawo.
Allah Shi ne Masani.
Zauren Fatawoyi Bisa
Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance damu cikin wannan group domin Fadakarwa...
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.