Ticker

6/recent/ticker-posts

Wutar Kaikayi

Ruƙayya Ibrahim Lawal (2023). Wutar Kaikayi. Ɗaukar Jinka (Labaran Da Suka Samu Nasara A Gasar Gajerun Labarai Ta Arc. Ahmed Musa Dangiwa, 2022). Kangiwa Multimedia and Communication Company LTD

WUTAR ƘAIƘAYI

Na

Ruƙayya Ibrahim Lawal

Da hanzari na bar yin safa da marwan da nake yi a ƙofar ɗakin da aka shigar da mijina don ba shi agajin gaggawa cikin asibitin, ganin babban likitan da yake duba shi ya fito tare da tawagar masu taimaka masa. Na tari gabansu a rikice ina ƙwalla ina tambayarsa,

“Likita yaya jikin nasa? Me ya same shi?” Sai dai a maimakon ya ba ni amsar tambayar da na yi masa shi ma tasa tambayar ya watso mini.

“Mijinki yana shaye-shaye ko?”

Sai da na ji wani bargon kunya ya lulluɓe ni, har na sunkuyar da kaina zuwa ƙasa. Sanin cewa ba a ɓoye wa likita komai ya sa na ɗaga masa kai alamar ‘eh’, don sosai kunya nake ji a ce wai mijina ne ɗan shaye-shaye. Sai da ya yi gyaran murya sannan ya ce.

“Bayan kammala gwaje-gwaje mun tabbatar da cewa zuciyarsa na gab da daina aiki, yanayin bugawarta ya yi rauni sosai, wanda kuma duk silar shan kayan mayen da yake yi ne. Shi ya sa yanzu duk lokacin da ya ga wani abin da ya firgita shi irin yadda ya ga na yau, komai zai iya faruwa.

Ba iya zuciyarsa ba, hatta hantarsa ma tuni ta fara taɓuwa, don haka rayuwarsa a yanzu dai sai yadda ta yiwu naƙuda a ɗakin mayya.” Yana gama faɗin hakan ya kewaye ni ya yi gaba tawagar ɗaliban jinya suna take masa baya.

Abin mamaki sai na ji duk firgicin da nake ciki ya kau a zuciyata, a halin yanzu kuma tausayinsa nake ji kawai na irin yadda silar shaye-shaye ya rasa komai na rayuwarsa...

Kasancewar a I.C.U (Ɗakin ba da kulawa ta musamman) yake, kuma sun hana mu shiga. Sai na je ina leƙa shi ta gilashin tagar ɗakin. Yanayin yadda na gan shi a ciki ya firgita ni ainun, yana kwance ne kawai tamkar gawa. Na tsare shi da ido ina kukan zuci da na sarari, daga hawayen da ke tsiyaya a gefen fuskarsa na fahimci har a lokacin wutar nadamar da take hanƙoro a zuciyarsa ba ta lafa ba. An saka masa wata na’ura da take taimakawa wajen dai-daita bugawar zuciyarsa, saboda yanayinsa ya ta’azzara.

Da na kalli zanen bugun zuciyar tasa a jikin na’urar, sai ya zamar mini tamkar majigin da na fara hango silar faruwar komai...

“Inna lillahi, wayyo!” Na furta a gigice tare da farkawa a firgice, na miƙe a kan gotaccen gadon da nake kai a kwance, ina rarraba idanu. Da fuskar Sayyid na yi tozali yana huci tamkar kumurci. Kamar mai jira, ya ci gaba da tsula mini bel ɗin hannunsa.

Na shiga tsalle-tsalle ina kare jikina da hannayena, gami da ƙaraji, gangar jikina tana zuƙo raɗaɗin dukan.

Ƙururus! Na jiyo sautin karyewar abu da nake kyautata zaton katakon gadon ne, lokaci ɗaya kuma na ji sautin kukan yara yana tashi cikin wani firgitaccen yanayi.

Sai a lokacin sha’afaffiyar ƙwaƙwalwata ta tuna mini cewar ina kwance ne a kan gadon tare da yarana uku.

Shau! Na ji saukar bel a cikin ƙwayar idanuna, ba shiri na buɗe baki cikin galabaitacciyar murya.

“Wayyo Allahna! Zai fitar mini da ido!” Take idon ya fara tsiyayar da ruwa tamkar famfon da ya birke. Yayin da shi kuma yake ta bambamin cewa na raina shi da na yi bacci ban jira dawowarsa ba, sai faman ba shi haƙuri nake.

Na dafe idon da hannu ɗaya ina sauraren yadda yake zogi tamkar an baɗa masa niƙaƙƙen barkono.

Ihun yara ya ci gaba da mamaye ilahirin ɗakin. Na juya yamutsattsiyar fuskata ina ƙare wa yamutsattsen mijin nawa kallo.

Ya ɗaga hannu da niyyar sake jibga ta ga yarana a cikin wani yanayi. Ganin bai san zuru ba, sai na saka ɗaya hannun na ture shi ya baje a ƙasa, na yi kan yarana.

Safna ‘yar shekaru biyu da rabi ce riƙe da hannu tana kuka, ashe ƙarar karyewar ƙashinta na ji, kuma ni ce na taka mata hannun lokacin da nake tsalle-tsalle.

Sautin kukan Sabir ɗan shekaru huɗu da ya ratsa masarrafar jina ya sa na bar wurin Safna na shiga neman sa. Na yi nasarar gano shi a bayan gadon ne sakamakon wadataccen hasken wutar lantarki da ya mamaye ɗakin, wanda nake kyautata zaton mijin nawa ne ya kunna ta.

Ɗago yaron ke da wuya maganaina suka sauka a kan goshinsa da ke fesar da jini. Na janyo shi, kafin na yi wani yunƙuri na ceton su Sayyid ya yi nasarar miƙewa yana zage-zage.

“Ke Jaka! Lallai kin isa. Ni kika ture? Za ki kawo mini abincina ko sai na ɗora daga inda na tsaya?” Ya yi zancen cikin sautin ‘yan maye.

‘An kuma, wai mace ta haifi mace.’ na faɗa a raina.

A zahiri kuwa ban ce masa kanzil ba, na fice zuwa madafa ina masa fatan shiriya.

Bayan na kawo masa abincin ne na shiga lallashi da kula da yarana wanda suka yi bacci da ƙyar. Karim ɗan shekara ɗaya ne kaɗai Allah Ya kare bai samu rauni ba. Hasalima duk abin nan da ake shi bacci yake abinsa.

Shi ma watsattsen mahaifinsu yana gama cin abincin ya mimmiƙe ya fara jan rago, cike da takaici nake tuna silar komai.

Kamar yadda huɗubar Liman ke tasiri a zuciyar masu tsoron Allah, haka huɗubar aboki ta yi tasiri wurin samar da gurɓatacciyar ɗabi’a ga matashin mijina.

Wannan ne dalilin da ya sa a rayuwata ba abin da na tsana sama da zaman majalisa da abokai. Me yiwuwa hakan ya samo asali ne a dalilin illar da abokantakar ta haifar mini.

‘Aboki fitilar sharri ko ba mai kina kai safe, wake ɗaya mai ɓata iri, macijin sari ka noƙe, gayyarka daban ce.’

Wannan ne kirarin da nake yi wa aboki dalilin matsalar da ya jaza mini a gidan aurena.

Aboki ne ya ɗora mijina a makauniyar hanya a dalilin zaman majalisa, biyo bayan korarsa daga wurin aiki da aka yi. Yayin da ya kasa riƙe gidansa, damuwa ta samu matsugunni a zuciyarsa, gurɓataccen amininsa ya yi nasarar ɗora shi a keken ɓera ta hanyar ba shi fatawar cewa tsotse-tsotsen kayan maye yakan wanke baƙin ciki da damuwa, shi kuwa ya riƙe wannan huɗubar gam.

Tun daga wannan ranar farin ciki ya ƙaura a gidan aure na, tashin hankali ya maye gurbinsa.

Har sai da ta kai da zarar mijina ya dawo daga majalisa to fa tawa ta same ni wai kura da hatsin gandu.

Don haka na ci alwashin raba shi da miyagun abokanai har ma da mummunar ɗabi’ar da ya koyo a wurinsu.

A taƙaice dai ranar a haka na ƙarasa sauran awanni ukun da suka rage na daren ina kukan zuci, sai gab da asuba bacci ɓarawo ya sace ni.

Washe gari Sayyid ya farka a wartsake bayan ya fahimci komai da ya faru ya yi kuka sosai, musamman da ya kasance shi mutum ne mai tsananin tausayi da nuna zallar so da ƙauna ga iyalansa.

Bayan dawowarmu daga nemawa yaran magani ya tasa su a gaba yana hawaye da faɗar “Ku yi haƙuri yarana duk laifina ne, ban san wane laifi na yi wa ƙaddara ba ta saƙale ni a haka.”

Na matsa kusa ina lallashin shi tare da ƙoƙarin janyo hankalinsa, “Kada ka zargi ƙaddara a cikin wannan al’amari, domin wannan ba aikinta ba ne, aikin son zuciya ne, son zuciya kuma shi ne ɓacinta. Ya kai mijina ka ji tsoron Allah ka daina tu’ammuli da kayan maye tunda har ya bayyana a gare ka cewar ba ya daga cikin ɗabi’un nagartattun bayi. Ko ma don lafiyarka da kare martabar ‘ya’yanka ya kamata a ce ka daina. Dubi yadda ka zamo sanadin illata lafiyar ‘ya’yanka da matarka, maye ya tagayyara rayuwar ahalinka, ta yadda ka kasa riƙe amanarmu da ta rataya a wuyanka...”

Har zuwa lokacin bai tamka ba, hakan ya ba ni ƙwarin gwuiwar ɗora igiyar zancena da faɗar, “A suratul Ma’ida aya ta 90, Allah Maɗaukakin Sarki ya ce, Ya ku waɗanda suka yi Imani, haƙiƙa giya da caca da gumaka da kibiyar neman sa’a, ƙazanta ne daga cikin ayyukan shaiɗan, ku nisance su ko da za ku samu rabo.

Ka sani fa, dukkaninmu makiyaya ne kuma za a tambaye mu a kan ababen kiwonmu. Wace amsa ka tanadarwa wannan ranar mai zuwa duk daren daɗewa?”

Ina zuwa nan a zancena sai ga hawaye suna tsere a kan kyakkyawar fuskarsa. Na yi shiru ina nazarin yadda jikinsa ya yi sanyi tamkar kazar da aka jefa da gishiri. Kamar da gaske wai karuwa ta ga noman Ɗan koli. Take a wurin Sayyid ya yi mini alƙawarin daina shaye-shaye da kuma rabuwa da abokin da ya shirya masa wannan gadar zaren.

Zamanmu da Sayyid ya yi daɗi a cikin satin da na yi masa nasihar. Ya daina dawowa gida a buge, haka ya fara sana’ar adaidaita sahu da yake karɓar sojan haya, yana neman na sayan gari a cikin gari. Har ma ya kai ni asibiti aka duba mini idona da ya ci gaba da tsiyayewa a hankali har ya ƙanƙance.

Bayan cikar awanni ɗari da sittin da takwas da suka bayar da kwanakin mako, giyar mamaki ta fara ɗawainiya da ni. Ina zaune na samu labarin cewa mijina yana tsare a hannun jami’an tsaro sanadiyyar kayan maye da ya sha ya kifar da wasu bayin Allah har suka ji raunuka.

A gigice na ƙarasa caji ofis ɗin na same shi zaune ya yi tsamo-tsamo tamkar kazar da ta faɗa ruwan zafi, muna haɗa ido ya kautar da kansa.

“Yanzu Sayyid ka yi mana adalci kenan? Da ma tuban muzuru ka yi?” Na yi zancen ina goge guntuwar ƙwallar da ta zubo mini.

Haka na yi ta yi wa jami’an magiya suka yi kunnen uwar shegu da ni, har sai da na kira yayansa Bilal, nan ma da ƙyar da jibin goshi suka ba mu belinsa da alƙawarin cewa zai biya kuɗin sabuwar adaidaitar da ya ɓata da kuma kuɗin jinyar mutanen da ya raunata, duk da cewa shi ma ya samu raunin.

A haka muka ɗauko shi zuwa gida aka ci gaba da yi masa maganin gargajiya, na ci gaba da jinyar su shi da yarana biyu da nake kan jinya, ni ma ga nawa jikin. A raina na ce, ‘Wannan shi ne haihuwar guzuma ɗa kwance uwa kwance.’

A lokacin da muke tsaka da tunanin mafitar inda za a nemo musu kuɗinsu kafin wa’adi ya cika, bayan cewa cikinmu ma a ɗamfare suke da yunwa. A lokacin ne kuma ciwon sikilar Sabir ya motsa fiye da koyaushe, jikinsa sai zafi yake yi, yana faman kuka da faɗar Mama hannuna ciwo, wayyo ƙafata! Guiwata!!

A haka ciwon ya ci gaba da cin ƙasusuwansa yana shanye masa ɓargo ba tare da mun iya yin wani yunƙuri na ceton shi ba.

Ranar Lahadi da dare Sayyid ya shigo gidan a dame, ya zauna a kusa da ni kansa a sukunye ya ce, “Matata ki yi haƙuri, na sani cewa ban zamo nagartaccen miji a gare ki ba, na tauye yardar da kika ba ni, kika zaɓe ni a cikin jerin taurarin da suke son haska rayuwarki a wancan lokacin, sai ga shi na ƙuntata duniyarki da duhu mai tsanani. Daga ƙarshe ma na yi silar mayar da ke nakasasshiya mai ido ɗaya a lokacin da kike ganiyar ƙuruciyarki.” Ya sauke ajiyar zuciya.

A lokacin ni kuma hawaye ya ɓalle mini.

Ya ɗora da cewa “Mun yi shawara ni da Inna cewa zan siyar da wannan gidan nawa, mu koma can gidan da take mu raɓe...”

Na yi saurin ɗago ɗayan idon da ya rage mini na kalle shi, a take ya ɗauki haske cewa ina neman ƙarin bayani ne, don haka bai jira cewata ba,

“Na san me kike tunani, amma ina amfanin baɗi ba rai? Siyar da gidan shi ne kawai mafita, domin Oga Goje bai san me ake kira mutunci ba.”

Sai a lokacin na harhaɗo kalmomi da ƙyar “Amma ina kuɗin da na ba ka a watannin baya? Me ne amfanin zinari idan ba zai biya buƙata ba?”

Ya juya mini baya yana yunƙurin tashi, “Na tattare su na saka a wani kasuwanci mai matuƙar riba, kayan na sauka za ki zama matar Alhaji.”

Na yi ‘yar dariyar farinciki, “Allah ya tabbatar mana da alkhairi.”

Duk da jikina bai ba ni ba, sai dai ko ba komai an samu zaftarewar ɗaya daga cikin matsalolin da suka gurgunta mana rayuwa.

Washe garin ranar, Sayyid ya haɗa takardun gidan ya fita ya bar ni ina hawaye, ba wai don an sayar da gidan ba, sai dai an ce sabo turken wawa.

Wata rana da ba za ta taɓa gogewa a ma’adanar taskace shuɗaɗɗun abubuwa da ke ƙwaƙwalwata ba.

A tsakiyar wannan daren ne, da na riski kaina a cikin matsanancin tashin hankali da ya yashe dukkanin nutsuwata.

Sheɗar Sabir ta zo iya maƙogwaro, a lokacin da yake fafutukar ƙwato numfashinsa daga mutuwar da ke ziyartarsa a lokacin ne watsattsen mahaifinsa ya shigo a bige.

‘Mai hali ba ya fasa halinsa.’

Na faɗa a raina ina kallon shi cike da tsana. Na yi kan yarona da yake ta faman kokawa da numfashinsa, amma na kasa dakatar da shi daga ci gaba da tunkarar ajalinsa.

“Ke ba ki ga na dawo ba ne? Uban me kike dubawa a wurin da kika zauna kamar an dasa ki?”

“Kana gani fa mutuwa yake yi, kusantar ajali yake yi.” Na faɗa cikin sautin kuka.

A maimakon Sayyid ya tauyasawa halin da nake ciki, a cikin hamagancinsa da shirmensa kawai sai ya bushe da matsananciyar dariya.

“Hahaha! Kamar fa Azara’ilu yana jinkirin ɗaukar ran nan bari na taya shi.”

Rufe bakinsa ke da wuya ya fisgo yaron da ke kwance a kan cinyata da ƙarfi ya maka shi da ƙasa.

Tamkar bulo ya faɗo daga hannun magini haka salwantaccen yaron ya faɗo daga hannun bugaggen ubansa da wani sauti ‘Tim!’.

“Innalillahi wa Inna ilaihir raji’un!” Na faɗa a rikice, na miƙe a kiɗime na yi kan yaron tare da ɗago shi ina jijjiga shi faɗar nake, “Sabir! Ɗana! Sabir ka motsa, ka yi mini magana!”

Sai dai ina! Tuni ruhinsa ya yi bankwana da gangar jikinsa.

Da na fahimci hakan cikin kuka na shafe idanunsa, na shimfiɗar da shi a ƙasa kan shimfiɗarmu na rufe shi da zani, na koma gefe ina ruzgar kuka na fitar hankali.

Shi kuwa Sayyid ya koma gefe sai tsala dariya yake cikin ficewar hayyaci, “Wai har ya mutu ne? Dalla ki daina kuka, ba ga ni nan ba, za ki samu wani lafiyayyen ɗan da ya fi wannan ma.”

Tun da nake a duniyata ban taɓa jin na tsani wani ɗan’adam ba kamar yadda na tsani Sayyid a ranar. Na tsine wa kayan maye da wanda ya ƙirƙiri shan su sau ba adadi, duk a wannan ranar.

Ba don alƙawarin da na ɗaukar wa margayiyar mahaifiyata ba, da a ranar ba abin da zai hana ni neman takardar sallama, ko na huta da ƙunci da azabar gidansa.

Washe gari da Sayyid ya tashi ya fuskanci abin da ya faru a daren jiya, ya sha kuka har da birgima, daga ƙarshe ma bai samu damar zuwa maƙabarta ba tsabar baƙin cikin da yake ciki na kashe babban ɗansa da yafi soyuwa a ransa.

A wannan ranar ne kuma bisa ga tilas muka bar gidan, ba tare da mun samu damar yin makoki a cikinsa ba.

Sama da sati biyu ina fushi da mijina a dalilin wannan abu, na jima ba na iya bacci sakamakon tunawa da waccan baƙar ranar da nake yi.

Wata rana da misalin ƙarfe shida na yamma na dawo daga ziyarar ahalina, na shiga sabon muhallin namu. Tun daga soro nake ganin hayaƙi yana tashi, wannan dalilin ya sa na ƙara sauri kamar zan wuce ƙafata.

A tsakar gidan na ci birki ina ƙare wa fasassun kwalabe da ƙonannun takardun kallo, hayaƙi duk ya turniƙe gidan.

Sautin shessheƙar kuka mai ƙarfi ta fara kawowa kunnena ziyara,

‘Waye mai wannan kukan?’

Tambayar da ta ziyarci zuciyata kenan. “Inna!” Na faɗa a razane, ban san lokacin da na sake hannun Safna ba na nufi ɗakin Inna gadan-gadan, domin kamar daga can sautin ke fitowa.

Zuwana tsakankanin ƙofofin guda biyu ne ya raba mini hankali gida biyu, domin sai na ji kamar a duka ɗakuna biyun kukan ke fitowa sau bibbiyu.

Ban tsaya dogon nazari ba, na shige ɗakin Inna da ke bangaren hagu.

A kwance na same ta cikin jini tana mayar da numfashi.

“Inna me....me ya same ki?” Na faɗa cikin tsinkakken sauti.

Na kai hannu zan kama ta cikin kuka ta ce “Kada ki taɓa ni, ki tafi ki bar ni, raɓar ku zunubi ne a gare ni, ki bari na tafi a wanke.”

Na kalli cikin idonta da ruɗaɗɗiyar fuskata, a take na karanto damuwar da ke zane a allon fuskarta. Kawai sai na fice da gudu cikin damuwa na yi ɗakinmu, Safna ta bi bayana a ɗimauce.

A lokacin kuma magariba ta kawo kai don haka ɗakin ya yi duhu. Shessheƙar kukan da na jiyo ce ta alamtawa ƙwaƙwalwata cewar Sayyid yana cikin ɗakin, hakan ya saka ni ƙarasawa ciki a hanzarce.

Na tarar da shi ya haɗa kai da guiwa yana rera kuka tamkar yaron goye. Cike da ƙarfin hali na juya na ja hannun Safna na kai ta maƙwafta, a can na ajiye Karim na juyo zuwa gida yayin da nake karanta wasiƙar jaki. ‘Meke faruwa? Ruwa fa ba ya tsami banza.’

Ɗakinmu na koma na same shi cikin tausasa harshe. “Me ya ƙuntata rayuwar mijina da yake yi mini asarar hawayensa haka?”

Ya ɗago kansa tare da zuba mini jajayen idanunsa da suka canza launi, ya sake fashewa da kuka. Da ƙyar na lallashe shi.

Cikin sautin kuka ya ce, “Na shiga uku Zainab! Na ɗebo ruwan dafa kaina, ni da albarka mun yi hannun riga, ni tsinanne ne, ba zan sake haɗa hanya da alkhairi ba a rayuwa.”

Kalamansa sun gigita duniyata, sun yi tsauri a sikelin auna fahimtata, sai kawai na zuba masa kadarar mujiyata, alamun neman fitilar da za ta haska mini ma’anar kalamansa.

“Na fasa wa Mahaifiyata kai da kwalba...”

Kuka ya fara cin ƙarfinsa, ya ja dogon numfashi ya ce “Na yi wa Mahaifiyata fyaɗe.”

“Na yi wa Mahaifiyata fyaɗe.”

“Na yi wa Mahaifiyata fyaɗe.”

“Na yi wa Mahaifiyata fyaɗe.”

Wannan sautin ne yake ta yi mini amsa amo a kunnena, kafin lantarkin da ke janyo sautuka zuwa ga masarrafar jina ya ɗauke.

Na yi faɗuwar ‘yan bori a ƙasa.

‘Ya Ilahi! Wannan wace irin makauniyar rayuwa ce?’

Ko bai faɗa ba, hasashena ya hakaito mini komai da ya faru.

Idan na kintata dai-dai ranar ma kayan mayen nasa ya shawo ya dawo gida a bige, shi ne giyar mayen ta ɗebe shi zuwa ɗakin Inna da tunanin nan ne muhallin da ya dace da zuwansa. Za ta yi yunƙurin dakatar da shi sai dai wanda ya yi nisa ba zai ji kira ba, hankalin da ya gushe bayani ba zai dawo da shi ba. Shi ne ya afka mata a tsammaninsa ni ce.

Kafin na gama farfaɗowa daga shokin ɗin da kalamansa suka ba ni na jiyo shi yana faɗar, “Allah ya tsine wa giya da duk wani nau’in kayan maye. Wallahi daga yau ba zan sake taɓa ko da sigari ba, na ga izina.”

Cikin wani irin yanayi yake zancen sannan ya sake cewa “Ka cutar da ni Habib, da ka sanya ni a halaka ka yi amfani da dukiyarka wurin siya mini giya, ga shi ka taɓar da rayuwata.”

Sai a wannan lokacin ne mutuwar Sabir ta dawo mini sabuwa, tsanar halayen Sayyid ta linku a zuciyata.

Na ɗago idona na watsa masa mugun kallo.

“Da ma tsalle ɗaya ake yi a faɗa rijiya, idan an shiga kuma sai a yi uku ma ba a fito ba. Irin wannan ranar ce nake jiye maka zuwanta, amma da yake mai rabon shan duka ba ya jin kwaɓo sai ka yi biris da kalamaina. Yau wa gari ya waya?”

Ranar a haka hargitsattsen mijin nawa ya raba hargitsattsen daren yana kuka, hargitsattsiyar fuskarsa ta bayyanar da hargitsin da ke cikin hargitsattsiyar zuciyarsa.

A safiyar wannan ranar ne na tashi da matsananciyar faɗuwar gaba da kasala. Sai wuraren ƙarfe tara na safe na fito daga ɗakina jiki a sanyaye, na nufi ɗakin Inna ina takawa a hankali tamkar kazar da ƙwai ya fashewa a ciki.

‘Ko da wane ido zan kalli wannan baiwar Allah?’ Da wannan tunanin na daure na sa kai a ɗakin.

“Assalamu alai...”

Sallamar ce ta maƙale a ƙasan maƙoshina sakamakon yin arba da sandararriyar gawarta a kan gadon da na yi. A hanzarce na ƙarasa na ɗora yatsana a saitin mazuƙan iskarta, don na tabbatar da zargina a kanta.

“Innalillahi wa Inna ilaihir raji’un! Mun shiga uku, Sayyid!” Na faɗa ina ƙwala masa kira da ƙarfi.

Kafin na gama rufe bakina ya faɗo ɗakin tamkar wanda aka ingizo.

“Me... Me ya faru?” Ya tambaya a dabarbace.

Ko da na labarta masa abin da ke faruwa sai gani na yi ya zube a ƙasa ‘sharaf!’ Kamar tsohuwar katanga.

Silar zuwan mu asibiti kenan, wanda kuma ga abin da likita ya gama faɗa mini game da rashin lafiyar tasa.

Nan take ƙwaƙwalwata ta tafi tunanin Ziko, wani matashi da ke yankinmu wanda ya jima yana shaye-shaye lokacin ina budurwa. Amma zuwa yanzu labarin ya zama tarihi a sanadiyyar faɗakarwa a kan illar sha da fataucin miyagun ƙwayoyi da tallafin koya sana’a da wani ɗan kasuwa mai kishin al’umma ya ƙaddamar ga wasu ƙididdigaggun matasa na yankinmu, Ziko yana daga cikin waɗanda suka samu horon. Yanzu haka ya nisanci shaye-shaye da abokan banza ya zama nagartaccen mutum har ma ya yi aure yana zaune ƙalau ga sana’ar ɗinki da yake koyarwa wasu matasan abin da ba a taɓa tsammani ba.

Gatan da mijina bai samu ba kenan, shi ma na san wataƙila da shaye-shayensa ya zama tarihi.

Ina ma ace gwamnati ko masu hannu da shuni za su samar da wani tsari na tallafa wa masu shaye-shaye a unguwanni, da kuma sama musu sana’ar dogaro da kai. Tabbas da za a samu sassauci sosai na yawan shaye-shayen da yake neman ƙone ƙasata kamar wutar daji.

Da ma in dai ba zaman banza, ba a ƙunci a banza, muddin ba ƙunci ba shaye-shaye a banza.

Yau dai ga inda rashin abin yi da biyewa abokan banza ya kai mijina.

Da a ce ya samu irin wannan tallafin kafin ya yi fargar jaji wataƙila da bai shiga wannan yanayin da koyaushe zai iya tafiya ya bar ni da ƙuncin da zai zame mini lumbu-lumbu wutar ƙaiƙayi da za ta ci gaba da zurɗar zuciyata har zuwa numfashina na ƙarshe ba.

Ɗaukar Jinka

Post a Comment

0 Comments