Citation: Abubakar BABANGIDA, Hassan MUSA & Masaya Luje NJELU (2020). Ta’aziyya A Wasu Waƙoƙin Alhaji Dr Mamman Shata Katsina. Yobe Journal of Language, Literature and Culture (YOJOLLAC), Vol. .8 Department of African Languages and Linguistics, Yobe State University, Damaturu, Nigeria. ISSN 2449-0660
TA’AZIYYA A WASU WAƘOƘIN
ALHAJI DR MAMMAN SHATA KATSINA
Abubakar BABANGIDA
Hassan MUSA
Masaya Luje NJELU
Tsakure
Wannan muƙala mai taken Ta’aziyya a wasu waƙoƙin DR. Mamman Shata Katsina ta yi bayanin yadda Marigayi Alhaji Dr.
Mamman Shata ya ambaci mutuwa a wasu waƙoƙin ta’aziyya domin isar da saƙo ga masu sauraro. An nazarci wasu daga cikin waƙoƙin ta’aziyya ta fuskar matakan
nazarin waƙar baka inda aka fi mayar da hankali kan yanayin ta’aziyya da juyayi da
yi wa mamaci adu’a da fatan alkairi da nema masa gafara da sauran abubuwan
alkairai da ya aikata a duniya.
Abstract
The
paper tittles: Nazarin Ta’aziyya a Wasu Waƙoƙin
Alhaji Dr. Mamman Shata Katsina. This study aim at pin-pointing the poems who
adopted death (ta’aziyya) tragedic and cruel words style in his selected
stanzas. Ta’aziyya based on qualitative research on the stanzas of some poems of Mamman
Shata Katsina. The Shata ta’aziyya songs discuss condolence, redumption
retaliation and God willing. The research is library base document based on qualitative
research as mentiond above.
1.0 Gabatarwa
A ra’ayin C.N.H.N
(2016, sh. 416) an bayyana ta’aziyya da gaisuwar da ake yi wa mutanen da aka yi
wa mutuwa don sanyaya musu zuciya ko gaisuwar mutuwa. Dukkan al’aumma sun yi
imani da mutuwa ta zama dole ga kowane mai rai. in har lokacin ta ya yi. Hausawa
a kowane yanayi, sun yi imani da cewa lallai mutuwa tana riskar mutum ko da
jinya ko babu jinya.
Wannan takarda za ta yi
nazari ne a kan ta’aziyya a wasu daga cikin waƙoƙin Alhaji (DR) Mamman Shata Katsina. A
wasu lokuta Mamman Shata yana yin waƙoƙin ta’aziyya ne da nufin yin ta’aziyya
ko jimami ko juyayi ko kuma faɗakarwa ko tabbatar da tsoron
Allah da nuna buwayarsa ko ambaton wasu ayyuka da mamacin ya yi na alkairi da
sauransu.
1.1 Iyakar Bincike
Wannan takarda, za ta
kawo wasu daga cikin ɗiyan waƙoƙin Dr. Mamman Shata
Katsina na ta’aziyya na sharhantawa domin nazari.
1.2 Hanyoyin Tattara Bayanai
An yi
karance-karance, wato an karanta littattafai da muƙalu da ɗakunan karatu kamar
na Kwalejin Umar Suleiman, Gashua da Kwalejin Atiku Abubakar, Nguru. Haka kuma
an saurari waƙoƙin ta’aziyya na Mamman Shata a rediyo da wayoyi. An kuma
jujjuye su a takarda da kuma sauran abubuwan da aka gudanar domin nazarin
wannan takarda.
1.3 Ra’in Bincike
An ɗora muƙalar ne bisa ra’in
Katanci na Mike Horward Abrams (1953). Wannan ra’in yana bayyana dangantakar
adabi da marubucin adabin da kuma mihimmancinsa da ya kasance tunani da dabarun
marubuci. Wannan ra’in na Abrams (1953) shi ne Hassan (2013) ya yi amfani da shi.
Hassan ya yi amfani da ra’in ne domin nuna mutuntakar Abubakar Imam a littafin Magana Jari Ce. Ya nuna jarunta da
tattalin arziƙi da matsayin mace da sauransu.
1.4 Tarihin Alhaji (DR) Mamman Shata Katsina A Taƙaice
Ɗangambo (2013) cewa
ya yi, “kafin a nazarci kowane aiki na fasaha, waƙa ce ko labari,
lallai ne a kawo taƙaitaccen tarihin mawallafi” (sh. 4-15). An haifi Alhaji
(DR.) Mamman Shata a garin Musawa ta jihar Katsina, a shekara (1923) Shata ya
fara waƙa ne saboda ƙiriniya irin ta
yarinta, (ba gada ya yi a wurin iyayensa ba.) Daga bisani Shata ya yi ƙaura da iyalansa zuwa
birnin Kano. Marigayin ya yi waƙoƙi[1] da dama,
saboda shi da kansa; bai san iya adadin waƙoƙin nasa ba. A lokacin
milkin soja na Janaral Yakubu Gawon, Shata ya samu kyautar yabo a fagen waƙa. Kuma Jami’ar
Ahmadu Bello Zariya ta ba shi digin girmamawa na (DR.).
Mawaƙin ya yi
tafiye-tafiye a dalilin sana’arsa ta waƙa. Ya ziyarci ƙasashen Afrika da ma ƙasashen Yamma kamar
Canada ta Amurka da Birtaniya da Faransa da sauransu. Shata ya yi harkar siyasa
a rayuwarsa tun daga Jumhuriya ta farko. Ga misali ya yi NEPU[2] a
jumhuriya ta farko, ya yi GNPP a (1980) da kuma N.P.N. Ya taɓa rike miƙamin kansila da kuma
shugaban jam’iyar S.D.P na ƙaramar hukuma Kankiya ta jihar
Katsina. Shata ya Rasu a shekarar (1999) an kuma binne shi a garin Daura kamar
yadda ya bar wasiyya. Ya bar mata uku waɗanda suka haɗa da Furera da Hadiza da Binta. Ya bar
‘ya’ya 19 da jikoki 28. Sai dai ya yi aure-aure da dama, wasu matan sun rabu
ne, wasu kuwa mutuwa ce ta raba su. Mahdi mai dogon zamani shi ne laƙabin da ake yi wa
Mamman Shata katsina.
2.0 Ma’anar Ta’aziyya da Sigogi
Bargery (1934) ya
bayyana Kalmar ta’aziyya da cewa, “gaisuwa ce ta jajantawa bayan wani jarumi ko
wani ya riga mu gidan gaskiya.” Ta’aziyya na nufin jajantawa ko gaisuwa da
adu’o’i ga iyaye da abokai da ‘ya’ya da dukkan ahalin mutumin da ya rasu. A nan
za mu iya cewa, mutuwa da ta’aziyya suna tafiya kafada da kafada. Saboda sai an
yi mutuwa kana a yi ta’aziyya. Ta’aziyya kuwa, na ɗauke da furuci ko
kalamai na tausayawa, cikin tattausan lafazi. Ga kuma nuna buwaya da matsiyi da
ikon ubangiji.
2.1 Sigogin Ta’aziyya
Ta’aziyya a ƙasar Hausa na da
sigogi daban-daban. (Da yake jinsin mutane maza da na mata sun bambanta da
juna.) Idan muka duba ɓangaren maza, a
lokacin ta’aziyya, suna zama ne a kofar gidan mamaci domin karɓar ta’aziyya daga
wurin mutane. Sai dai a wasu lokuta, wasu mazan kan shiga cikin gida wurin mata
domin yi musu ta’aziyyar. Sai dai irin wannan tsari da maza ke shiga cikin gida
kamar yadda aka faɗa a baya, ya danganta
da kusancin mutumin/mutanen da mamacin ko danginsa. Haka zaika lamarin ke
kasancewa a ɓangaren mata.
Wata sigar ta’aziyyar
kuma, ita ce wadda ta shafi ƙungiyanci. Ga misali masu bin ƙungiyar izala, ba
kasafai suke karanto adu’o’i cikin harshen larabci ba. Daga an kai mamaci an
dawo sai a yi wa juna sannu sannu. Haka waɗanda suka zo yin ta’aziyyar daga baya, sai
dai su ce “sannu Allah ya masa Rahama.” A ɓangaren masu bin ƙungiyar ɗariƙa kuwa, sukan karanto
adu’o’in ta’aziyya cikin harshen Larabci. Haka ma waɗanda suka zo
ta’aziyyar ke aiwatarwa. Adu’o’in na iya zama a ɓoye ko kuma a bayyane kowa yana ji.
Hausawa sun tabbatar
da mutuwa wajibi ce, kuma dole sai an mutu ake yin ta’aziyya. Wannan dalilin ya
sanya mawaƙan baka da dama kan ambton ta’aziyya a cikin waƙoƙinsu. DR. Mamman
Shata Katsina ya ambaci ta’aziyya sau da dama a cikin waƙoƙinsa, duk domin isar
da saƙo ga ahalin mamaci. A al’adance, yin ta’aziyya na sanyaya
zukatan dangin wanda ya rasu. Saboda ana yin adu’o’i da faɗin halayen mutum na
gari da kuma fatan alkairi. Da yake akwai dalilai ko saƙonni da dama na yin
waƙa,
wata waƙar ana yin ta ne saboda ta’aziyya ko jimami ko soyayya ko
faɗakarwa ko hannunka
mai sanda ko tunawa da wanda ya mutu a yi masa fatan samun Rahamar Ubangiji.
3.0 Tarken Wasu Waƙoƙin Mamman
Shata na Ta’aziyya
Kamar yadda aka
bayyana a baya kaɗan, Alhaji DR. Mamman
Shata Katsina ya aiwatar da wasu waƙoƙi na ta’aziyya waɗanda yake yi wa
mutane daban-daban a cikinsu gaisuwa da Allah ya sanyaya haƙuri a zukatan ahalin
mamacin. To a wannan ɓangare su waɗannan waƙoƙi ne na ta’aziyya. Za
a ɗauki wasu a cikinsu a
yi musu tarke ko sharhi, musamman ta bin wasu ɗiyan waƙoƙinsa.
A wani ɗa na waƙar Ciroman Gombe,
Alhaji Shata Katsina yana cewa:
Jagora: Kowa
ya mutu bai yi sauri ba,
Mu da muke ba mu daɗe ba,
Sai mun zo Ciroman
Gombe,
Mutuwa ta min gaggawa ta,
Ɗauke
Ciroman Gombe.
Y/amshi: Allah jiƙan
Ciroman Gombe.
(Shata: waƙar ta’aziyyar Ciroman
Gombe ɗa na 1-5)
A wannan ɗiyan waƙar Shata ya nuna
cewa; mutuwa ta yi masa hanzari ta ɗauke Ciroma. Wannan ya tabbatar da cewa,
akwai ɓirɓishin maguzanci cikin
baitocin wannan waƙar. Ga kuma ta’aziyya da aka bayyana kamar yadda
musulunci ya tanada.
Har ila yau a cikin
waƙar
“Ciroman Gombe” Shata ya bayyana ta’aziyyasa da nufin isar da saƙo ga masu sauraro. Ga
abin da Mahadin yake cewa:
Jagora: Da ni da Gombe sai wata rana,
Domin ba ciroman Gombe,
Shaida a mutanen
Gombe,
Matanku zuwa ga
mazanku,
‘Yan ƙanana zuwa ham manya,
Na ƙauye duk da na birni,
Ku da Alhaji sai wata
rana.
Y/amshi: Allah ya jiƙan
Ciroman Gombe.
(Shata: Waƙar Ciroman Gombe ɗa na 1-7)
A waɗannan gunduwowin waƙar, Shata ta’aziyya
ya yi da kuma bayyana yadda mutuwa take ɗaukar mutum; ko da ya kasance na kirki ne a
kowane lokaci. Da kuma yadda take da ciwo da raɗaɗin a zukatan mutane. Mawaƙin ya nuna Ciroma a
matsayin mutumin kirki kuma adali. Wannan ya yi dai-dai da abin da Hausawa suke
cewa, “rumfa ta faɗi.” Idan wani mai
taimako ko ɗaukar ɗawainiyar iyali ko
al’umma a kafaɗarsa; ya zama babu
shi.
A wata waƙar Shata ta Habibu
Fari, makaɗin ya ƙira ta’aziyya duk
domin isar da saƙo da gina tunaninsa ga masu sauraro. Ga abin da yake
cewa:
Jagora: Ya Allah don
Rasulullahi,
Don albarkar
shaihunanka,
Ya gafarta wa Habibu fari.
‘Yan amshi: Allah ka jiƙan Habibu Fari
(Shata: waƙar Habibu fari da
Habibu baƙi ɗa na 13-15)
A waɗannan ɗiyan waƙar Mamman Shata yana
ta’aziyya yake ta mutuwar Ciroman Gombe. Kuma ya yi ta ne kamar yadda addininsa
ya tanada.
3.2.1 A cikin wasu ɗiyan waƙar ta Habibu fari,
Shata ya yi ta’aziyya kamar yadda yake cewa:
Jagora: Allah ya jiƙan Habibu fari,
Ya Allah gafartawa
Habibu fari,
Allahn da ya wo
Habibu fari,
Ya ɗauki abinsa kar ku ji
wai.
‘Y/amshi: Allah ka jiƙan Habibu fari.
(Shata: Waƙar Habibu fari da
Habibu Baƙi ɗa na 1-5)
A cikin ɗiyan wannan waƙar, Shata ya yi
ta’aziyya ne. ya kuma tabbabatar da cewa lallai Habibu fari ya mutu. Saƙo ne na ta’aziyya, da
yake isar wa jama’a cewar wanda bai sani ba ma ya sani. Habibu fari ya riga mu
gidan gaskiya. Haka a kuma cikin waƙar da Shata ya yi wa
sarkin Daura, ga abin da yake cewa a cikin wasu ɗiyoyin waƙar kamar haka:
Jagora: Mamman mai Daura,
Aniyarka ta bi ka,
Uban Baushe ɗan Musa,
Mu fatan da muke,
Aniyarka ta bi ka,
Na mai ɗaki ɗan Musa.
‘Y/Amshi: Lafiya zaki Mamman baban galadima ɗan Musa.
(Shata: Waƙar lafiya zaki Mamman baban Galadima ɗan sarki ɗa na 22-26)
A wannan ɗiyan waƙar, Shata yana
ta’aziyya ne, da bayyana fatan alkairi ga sarkin Daura. Mawaƙin, a cikin ɗiyan waƙar ya bayyana wa
mutane tabbas Mamman Bashar mai Daura yana da kyakkyawar aniya/zuciya. Shata
yana rokon Allah halinsa na alkairi ya bi shi. Wannan fatan da Shata ya yi wa
sarkin Daura. Na daga cikin ta’aziyya kamar yadda aka bayyana a sama kaɗan.
A cikin wata waƙarsa mai suna “Wali”.
Mawaƙin ya yi ta’aziyya a wasu ɗiyan waƙar tasa, ga abin da
Makadin yake cewa:
Jagora: Lamarin duniya shiga da fita ne,
Har in mun mutu sai labari,
‘Yan amshi: Wali ɗan Usmanu Salgare.
(Shata: waƙar Wali ɗan Usmanu Salgare.)
A wannan ɗiya waƙar, Shata ya yi
nasiha ne a cikin ta’aziyya. Inda ya tabbatar da cewa tabbas duniya shigar
shantun ƙadangare ce, saboda haka, mawaƙin yana jaddada
lallai ko ana so ko ba a so mutuwa ta zama wajibi ga mai rai.
Akwai wata waƙar da shi Mamman
Shata Katsina ya yi wa wani bawan Allah mai suna Isyaku. Nan ma mawaƙin ya ambaci
ta’aziyya a cikin waƙar kamar haka:
Jagora: Wo duniyar nan ba ta zama ba ce,
Yan amshi: Isyaka ka dawo Lafiya.
(Shata: waƙar Isyakau a dawo
lafiya.)
A waɗannan ɗiyan waƙar, mawaƙin ya yi ta’aziyya
inda ya ƙara fito wa ya jaddada wa mutane cewa, duniya fa barin ta
dole ne, mutum ko yana so ko ba ya so dole sai ya mutu.
A cikin waƙar ta’aziyya ta
Abubakar Tafawa Shata ya fito ƙarara ya yi ta’aziyya a wasu ɗiyan waƙar kamar haka:
Jagora: Ya ‘yan Nijeriya sun yi kuka,
‘Yan Nujeriya sun yi
shiru,
Sun buɗe baki sun rasa,
Ran Abubakar Tafawa.
‘Y/amshi: Allah
jiƙan Abubakar Tafawa.
(Shata: Waƙar Ta’aziyyar
Abubakar Tafawa Balewa ɗa na 6-9)
A cikin wasu ɗiyan wannan waƙar, Shata ya bayyana
ta’aziyarsa a fili. Domin ya nuna mihimmancin Abubakar Tafawa, ya zarce ga
mutum guda ɗaya rak. Ya nuna
cewar, ƙasar (Nijeriya) ce da mutananta suka yi babban rashi.
Haka ya tabbatar da kirkin Tafawa a sarari.
A cikin waƙar, Shata ya ci gaba
da bayyana ta’aziyya a wasu ɗiyan waƙar kamar yadda yake cewa:
Jagora: Ƙasashen waje sun
aiko,
A rediyo hatta a
takarda,
Sun masa adu’a tun farko,
Sun masa adu’a nan ƙarshe,
Allah jiƙan Abubakar Tafawa.
‘Y/amshi: Allah jiƙan Abubakar Tafawa.
(Shata: Waƙar Abubakar Tafawa
Balewa ɗa na 10-14)
A ɗiyan waƙar ta sama Shata ya ƙara jaddada mutuntaka
da baiwa da adalcin Abubakar Tafawa Balewa a cikin ta’aziyya. Domin ya tabbatar
ba a Nijeriya kaɗai ba, har ma da ƙasashen ƙetare an san mutumin
kirki ne kuma adali.
A cikin waƙar Alhaji Habu ABCD
Mawaƙin ya ambaci ta’aziyya a wasu ɗiyan waƙar tasa kamar yadda
kada baki yake cewa:
Jagorta: Jihar
arewa mun yi,
Babban rashi Alhaji,
Garba Habu ABCD,
Ka ce Habu ABCD nan,
Arewa har ma duk
Nijeriya,
An yi asarar rashin Habu ABCD.
‘Y/amshi: Alla
jiƙan Alhaji Garba Habu A BCD
(Shata: Waƙar: Alhaji Garba Habu
ABCD ɗa na 1-6)
A cikn waɗannan ɗiyan waƙar, Shata ya fito da
darajar Alhaji Habu ABCD a cikin ta’aziyya. Ya nuna rashinsa asara ce ga
yankinsa na arewacin Nijeriya da ƙasar gaba ɗaya.
A cikin wasu ɗiyan waƙar ta Alhaji Habu
ABCD, Mawaƙin ya ƙara ambaton ta’aziyya a muryarsa.
Kamar yadda Mahadin mawaƙan ke cewa:
Jagora: Manoman cikin daji na fata,
Manoman cikin birni
na fata,
Kome mutum ke
shiryawa,
Da taimakon Habu
ABCD.
‘Y/amshi: Allah
jiƙan Haji Garba Habu ABCD.
(Shata: Waƙar Alhaji Garba Habu
ABCD 8-14)
A wannan ɗiyan waƙar, Shata ya miƙa ta’aziyyarsa ne kai
tsaye ga manoma. Bisa rashin Habu ABCD. Wannan ya nuna cewa mamacin yana
taimakawa masu ƙananan ƙarfi ko marasa galihu.
Shata a cikin waƙar ta Habu ABCD, ya
ci gaba da furta ɗiyan ta’aziyya kamar
yadda yake cewa:
Mutuƙar ka kai masa kuka,
Shi zai je da ƙafa ya tashi,
Ya duba ya ma taimako
bisa,
Kan aikinka Alhaji
Habu ABCD,
Allaji jiƙan Haji Habu ABCD.
‘Y/amshi: Allah jiƙan Haji Habu ABCD.
(Shata: Waƙar Alhaji Habu ABCD ɗa na 12-17)
A waɗannan ɗiyan waƙar, Shata ya ƙara fito da hoton
ta’aziyya na halin Alhaji Habu ABCD. Tabbas kamar yadda aka bayyana a sama kaɗan, mawaƙin ya faɗi halin ƙwarai na marigayin ya
kuma isar da saƙon ne ga jama’a.
A wata waƙar sardaunan Sakkwato
Mamman Shata ya gina tunaninsa a kan ta’aziyya kamar haka:
Jagora: Da gudu domin abokan gaba,
Malam Bello gwanda shahada.
‘Yan amshi: Malam Amadu Bello.
(Shata: waƙar Amadu Bello
Sardaunan Sakkwato ɗa na 8-9)
Saƙon da waɗannan ɗiyan waƙar suke isarwa ga
jama’a shi ne, dukkan da mutane sun yi imani da mutuwa ba daɗi. Su na kuma tsoran
ta. Amma domin alkunya a idon jama’a ko ragwanta ko ƙasƙanci a wurin da bai
dace ba, sun gwammaci mutuwa gaba ɗaya. Domin haka ne suke yi wa Sardaunan
Sakkwato murna da aka kashe shi, gara ya yi shahada, da ya zauna ya ga wulaƙanci da maganganun
jama’a.
Haka ma waƙar da ya yi wa
sardauna Shata ya bayyana ta’aziyya a cikin wasu gunduwowin waƙarsa kamar yadda yake
cewa:
Jagora: Na san Kebbi don Ɗanhassan,
Na san Jega don Ɗanhassan,
Na san Kwantagora don
Ɗanhassan,
Albarkacinka duk na
san su,
Allah jiƙan ka Baban Hassan,
Gama ranar tafiya lahira,
Ku tabbata babu zaman duniya.
: ‘Y/ amshi: Sardauna bahago Ɗanhassan Gulbi ka ka
ci mai gardama.
(Shata: waƙar Ahmadu Bello
Sardaunan Sakkwato ɗa na 19-30)
A wannan ɗiyan waƙar, baya ga ta’aziyya
da ya yi. Shata ya tabbatar da cewa, mutuwa tana cikin zukatan mutane a kullum,
alƙawarin
ubangiji kuma ba ya tashi a kan mutuwa. Lallai mutuwa ta zama dole ga dukkan
rayayye idan lokacinsa ya yi. Babu jirkintawa babu tsini kuma babu dabara.
A cikin waƙar da ya yi wa BB
Faruƙu, likitan waƙar ya ambaci
ta’aziyya a cikin wasu baitocin waƙar tasa kamar yadda
ya kaɗa baki ya ce,
Jagora: Babar BB da,
Baban BB Allah,
Maza A Ji kansu.
‘Y/Amshi: BB Faruƙu na Allah.
(Shata: waƙar BB Faruƙu na Allah ɗa na 5-6)
Waɗannan ɗiyan waƙar na sama, ya nuna
cewar Shata yana da alƙawari da kuma sanin abin da ya dace da kuma zumunci.
Saboda ta’aziyya da ya yi wa iyayen BB Faruƙu. Wannan ya kai a ce
mawaƙin, yana da alƙawari da riƙe zumunci.
4.0 Kammalawa
Kamar yadda bayanai
suka gabata, Alhaji Dr Mamman Shata Katsina ya yi waƙoƙi da yawa waɗanda suka shafi
ta’aziyya ga al’umar Hausawa. Kamar yadda aka yi nazari a wannan takarda, waƙoƙin ta’aziyya na Shata
sun haɗa da waƙar Ciroman Gombe da
waƙar
ta’aziyyar Habibu Fari da waƙar ta’aziyyar Sardaunan Sakkwato
Ahmadu Bello da sauransu.
A wannan nazari an
lura Alhaji Mamman Shata mutum ne wanda yake kula da jama’arsa. Har yake yi
musu. Yana ta’aziyya ga duk wanda ya rasu a cikinsu. Haka an fahimci Dr. Shata
yakan zayyana wasu ayyuka da ma’amaloli da mutum ya yi a rayuwarsa. Yana yi wa
mutanensa ta’aziyya.
Manazarta
Abba, M. da
Zuladayyani, B. (2000). Waƙoƙin baka
na Hausa. Gaskiya
Co-oporation
Abraham R. C. (169). The dictionary of Hausa language. Goɓernment Printing Press.
Abram A. H. (1953).
The mirror and the lamp orientation of romantic theory. Oɗford University Press.
Bergery, G. P.
(1934). A Hausa English dictionary and
English Hausa ɓocabularies.
A.B.U. Press.
Bunza, A. M. (2002). Rubutun Hausa yadda yake da yadda ake yin
sa. Ibrash Islamic Publications Centre.
Bunza, A. M. (2013).
Death in Hausa folkloric perspectiɓe. International
Conference, In Honor of Professor (Ambassador) Ɗandatti Abdulƙadir
OFR,
1-19.
Bunza, A. M. (2013).
Littafin ruwan bagaja a ma’aunin matakan rayuwar bahaushe.
Humanities In Sub-saharan World Ruwan Bagaja In Perspectiɓe, 425-447.
C.N.H.N. (2016).
Ahmadu Bello University Press.
Ɗangambo, A. (2013). Ɗaurayar
gadon feɗe waƙa (sabon tsari). K. D. G. Publishers.
Gusau, S. M. (2003). Jagoran nazarin waƙar baka. Kano Benchmark
Publishers.
Gusau, S. M. (2008). Waƙoƙin baka
a ƙasar Hausa: Yanaye-Yaneyensu da sigoginsu. Benchmark
Publishers.
Gusau, S. M. da Aliyu
I. F. (2011). Waƙoƙin baka
na Hausa.
Century Research and Publishing.
Gusau, S. M. (2014). Waƙar baka bahaushiya (The Hausa oral song). Century Research and Publishing.
Hassan, S. (2013). Mutuntakar Abubakar Imam a littafin ruwan
bagaja. [Kundin digiri na uku]. Jami’ar Ahmadu Bello.
Mashi, M. B. (1986). Waƙoƙin baka
na siyasa.
[Kundin digiri na biyu]. Jami’ar Bayero Kano.
Sarɓi, S. A. (2007). Nazarin waƙe na Hausa. Samarib Publishers.
Umar, M. B. (1980).
Waƙoƙin baka madubin
rayuwar al’umma. Takardar da aka gabatar
taron ƙarawa juna ilimi, Argungu.
Usman, H. S. (2015). Nazarin tirken ta’aziyya a waƙoƙin DR.
Mamman Shata Katsina.
[Kundin digiri na biyu]. Jami’ar Bayero Kano.
Waƙoƙin Baka Na Hausa
(2011). Department of Hausa Federal College of Education Katsina. Centuary
Research and Pubblishing.
Yakasai, S. A.
(2013). Jagoran ilimin walwalar harshe.
Garkuwa Media Services.
[1] Jama’a da dama sun tabbatar da
cewa, baiwar da ta ƙara ɗaukaka darajar Mamman Shata a duniyar adabin Hausa ita
ce; yin waƙa nan take
ba sai ya shirya ba. Wasu daga cikin waƙoƙin da ya yi a irin wannan yanayin
sun haɗa da waƙar Kennedy center da Allah mai
aradu mai talata da Ɗanfulani da
Dejin Ruhu da sauransu.
[2] Lokacin wannan siyasa ta NEPU an yi
abubuwa da dama a ƙasar nan
tamu (Nijeriya) an yi waƙe-waƙe, an yi rikici da kashe-kashe. An
yi rabuwar dutsi hannun riga tsakanin masu milki da talakawa da alamajirai.
Domin ƙarin bayani
za a iya duba aikin farfesa Ibrahim Malumfashi mai taken Yankan Kunkurun Bala a
Himma ta jami’ar Umar Musa ‘Yar adu’a Katsina

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.