Citation: Baba HUSSAINI & Hussaini Isah MUHAMMAD (2020). Karin Magana Da Kirari Da Habaici A Wasu Waƙoƙin Sarauta Na Haruna Aliyu Ningi. Yobe Journal of Language, Literature and Culture (YOJOLLAC), Vol. .8 Department of African Languages and Linguistics, Yobe State University, Damaturu, Nigeria. ISSN 2449-0660
KARIN MAGANA DA KIRARI DA HABAICI A WASU WAƘOƘIN SARAUTA NA HARUNA ALIYU
NINGI
Baba HUSSAINI
Hussaini Isah MUHAMMAD
Abstract
This
paper focuses on the study of Hausa idioms in some selected court songs
composed by the popular singer Haruna Aliyu Ningi. It also discusses figures of
speech such as proverbs, epithes and innuendo. Four selected songs serve as the sources of the
data. The theory Waƙar Baka Bahaushiya (WBB) propounded by Gusau (2015) has been
adopted for the study. Finally, the study discovers how the singer (Haruna Ningi) displays a high level of proficiency in the use of proverbs, epithets, and innuendo to convey messages in his songs to his audience.
1.0 Gabatarwa
Kiɗa da waƙa abubuwa ne da suka daɗe da samun matsuguni a rayuwar al’ummar Hausawa. Wannan
ne ya sa a kowane zango na rayuwar Hausawa akan sami tasirin kiɗa da waƙa, sannan kowane mataki na rayuwar Hausawa
tun daga yarinta zuwa tsufa akwai waƙoƙi a ɗamfare da su. Wannan shi ya haifar da waƙoƙin yara da waƙoƙin ‘yan mata da waƙoƙin tashe da waƙoƙin daka da waƙoƙin raino da waƙoƙin daɓe da waƙoƙin niƙa da waƙoƙin cikin tatsuniyoyi da waƙoƙin fina-finai da waaƙoƙin fada (sarauta) da waƙoƙin siyasa da waƙoƙin bege da waƙoƙin kiɗan fiyano da waƙoƙin kiɗan disko. Makaɗan baka na Hausa mutane ne
masu hikima da basira wajen saƙa maganganun hikima da
amfani da adon harshe a cikin waƙoƙinsu. Wannan dalili ya sa waƙoƙin baka suke da mutuƙar tasiri a rayuwar
al’ummar Hausawa, sannan mawaƙan baka suka zamo mutanen
da suke ba da gudummawa wajen ci gaba da raya adabin baka na Hausawa. Shi ya sa
masana da manazarta suke ta bibiyar waƙoƙinsu domin nazartar su a ilmance.
Wannan
takarda za ta yi bayani ne a kan wasu hikimomi a waƙoƙin sarauta na Haruna Aliyu Ningi. A cikin takardar an kawo tarihin
Haruna Aliyu Ningi a taƙaice sai kuma ma’anar
maganganun hikima da ma’anar karin magana da kirari da kuma habaici. Haka kuma
an kawo misalai na waɗannan ire-iren hikimomin magana daga wasu ɗiyan waƙoƙin sarauta na Haruna Aliyu Ningi tare da yin sharhinsu.
1.1 Taƙaitaccen Tarihin Haruna
Aliyu Ningi
An haifi
Haruna Aliyu Ningi ranar Talata 22/11/1972 a ƙauyen Rumbu da yake ƙaramar hukumar Ningi ta
jahar Bauchi[1]. Ya yi karatun allo a wurin mahaifinsa a
inda ya sauke Alkur’ani, ya kuma karanci littattafan Fiƙihu da Hadisai da
sauran littattafai na addini. An saka Haruna a makarantar firamare ta garin
Rumbu daga shekarar 1977-1981. Ya samu nasarar shiga makarantar sakandire da
take garin Bura daga 1981 zuwa 1986. A shekarar 1994 ya sami gurbin ci gaba da
karatu a makarantar Kimiyya da Fasaha da ke Ƙauran
Namoda a inda ya samu shaidar Difiloma a ɓangaren harkokin kuɗi (Financial Studies) a shekarar 1996. Daga nan sai ya dawo gida
ya fara harkar siyasa. Haruna ya fara waƙa ne a shekarar 1996 a lokacin siyasar UNCP da
DPN.
Haruna
Aliyu Ningi mawaƙi ne da ya yi shuhura a ɓangaren waƙoƙin siyasa. Daga cikin fitattun waƙoƙinsa akwai: “PDP jam’iyata” da “Ku faɗa wa Obasanjo; Mu kan ba mu
yarda ta zarce ba” da kuma “Shegiyar uwa mai kashe ‘ya’yanta PDP” da sauransu.
Haka kuma, yana aiwatar da waƙoƙinsa ne da kayan kiɗan zamani tare da ‘yan amshi a sitidiyonsa mai suna Baushe Media
da ke kan Titin Bakaro daura da gidan sarki a garin Bauchi.
2.0 Wasu Hikimomi a Waƙoƙin Sarauna na Haruna Aliyu Ningi
Maganganun
hikima/azanci su ne maganganu masu ɗauke da wasu kalmomi na musamman, sun ƙunshi sarrafa kalmomi da jimloli wajen ƙera magana mai ɗauke da hikima da gwaninta da samar da zuzzurfar ma’ana (Ahmad,
2016, sh. 2).
Ɗangambo
(2011, sh. 67-73) ya bayyana cewa maganaganun hikima/azanci sun haɗa da karin magana da azanci
da ƙarangiya da kacici-kacici da zaurance da sara da take da kirari da
habaici da zambo da gatse.
Shi kuwa
Gusau (2011, sh. 14-15) ya kawo adabin baka na azancin magana waɗanda suka haɗa da karin magana da
tumasanci da kirari da baƙar magana da barkwanci da
gatse da kacici-kacici da shaguɓe da ba’a da gugar-zana da sara da dungu waskiya da santin magana
da zambo da zaurance da habaici da kuma saye.
Ke nan za
a iya cewa maganganun hikima/azanci maganganu ne da ake amfani da wasu zaɓaɓɓun kalmomi domin yin
kwalliya da ƙawata magana a yayin isar da saƙo.
Daga
cikin maganganun azancin da aka yi misalai da su a wannan takarda akwai karin
magana da kirari da kuma habaici.
2.1 Karin Magana
C.N.H.N
(2006) ya bayyana ma’anar karin magana da cewa, “Magana ce ta musamman wadda
sai an yi tsokaci ake ganewa” (sh. 235).
Karin
magana wata dunƙulalliyar magana ce ta hikima wadda take ɗauke da ma’ana mai yawa
(Abba da Zulyadaini, 2000, sh. 140).
Ta
la’akari da waɗannan ma’anoni da aka kawo, za a iya cewa karin magana gajeriyar
jimla ce ta hikima wadda ta ƙunshi magana mai faɗi amma a dunƙule wuri ɗaya.
Mawaƙa suna amfani da hanyoyin guda uku wajen tsarma karin maganar da
suka zaɓa (wato
cikar karin magana da ƙari ko ragi ga karin magana
ko kuma ambato ma’anar karin magana)[2]. Ma’ana suna sarrafa karin maganar ne ta
hanyar yin amfani da shi kai tsaye kamar yadda yake, ko kuma su baddala shi, su
canza masa fasali ta yadda ma’anarsa ba za ta ɓuya ba.
Haruna
Aliyu Ningi yana amfani da wannan salo na karin magana domin nuna gwanintar
harshe da yin kwalliya tare kuma da jan hankalin mai sauraro a wurare
mabambanta a wasu waƙoƙinsa na sarauta kamar haka:
Misali na 1:
Jagora:
In dai Sarki ya fito wuri,
: A daina
kiran bayi,
‘Y/Amshi:
Iye iye.
Jagora: Wanda
ya sa kaza a baki,
: Ba
a mar maganar ƙoyi,
‘Y/Amshi:
Iye iye.
Jagora: Ɗan jikan
Usmanu ɗan
Kabiru,
: Mai
nasara ya yi,
‘Y/Amshi:
Iye iye.
Jagora:
Ya gaji ya ba ku ba wai ku fara,
: Bai sa
da tsaki ba.
‘Y/Amshi:
Ka ja mu zuwa Zanna Katsina,
: Alhaji
Lawan Musa,
: Mahassada
ba za su iya ma ba.
(Muhammad, 2019, sh. 153). Waƙar ‘Zannan Katsina’.
Ta la’akari da abin da aka kawo a
wannan ɗan waƙa a misali na 1, an fahimci
cewa Haruna Ningi ya yi amfani da tushen karin maganar nan da ke cewa, “Wanda
ya sa kaza a bakinsa ba ya kallon ƙwai”. Kaza tana cikin jinsin tsuntsaye da ake kiwo a gida musamman don
samun ƙwai da nama don ci ko sayarwa domin biyan buƙatu, tana da yawan tone-tone. Ƙwai kuwa
wata mulmulallar halitta ce da tsuntsaye suke fitarwa daga jikinsu.
Hikimar
da ke cikin wannan karin magana ita ce tana nuni ne da wanda ya riga ya wuce ka
ya fika, kamar yadda Bahaushe ke cewa “Na gaba ya yi gaba, na baya sai
labari”. Mawaƙin ya yi amfani da wannan karin magana ne don sanar da waɗanda suke adawa da Zannan
Katsina cewa ya riga ya fi su, ba ta su yake ba. A nan makaɗin ya kira Zannan Katsina
da Sarki, su kuwa masu adawa da bayi.
Misali na 2:
Jagora: Duniya
rawar ‘yan mata,
: Sai na gaba ya koma baya,
‘Y/Amshi:
Iye,
Jagora:
Shi ya sa nake jin ƙyamar,
: Ɗan mutum da ba ya shakkar ƙarya,
‘Y/Amshi:
Iye,
Jagora:
Duk kuɗinka duk
mulkinka,
: Ko
kanka ya fi ƙaton ƙwarya,
‘Y/Amshi:
Iye,
Jagora:
Ba ka wuta bare Aljanna,
: Shi ne
abin da nai tsinkaya,
‘Y/Amshi:
Iye,
Jagora:
In ba cikin kuren hali ba,
: Ni dai
ba zan yi ma waƙe ba.
‘Y/Amshi:
Yakubu Tafidan Soro,
Jagora:
Iye,
‘Y/Amshi:
Mai gida gidan alfarma,
: In da
mu ba za a kushe ma ba.
(Muhammad, 2019, sh. 166). Waƙar ‘Tafidan Soro ta i’.
A
wannan ɗan waƙa na misali na 2 da ya gabata, Haruna Ningi ya yi amfani da karin maganar
daidai yadda ake amfani da shi yau da kullum ba tare da samun wani sauyi ba ta
fuskar ƙari ko ragi, watau, “Duniya rawar ‘yan mata sai na gaba ya koma baya”. Duniya
wuri ne da ɗan’adam da sauran halittu ke rayuwa. Haka kuma za a iya bayyana
rawa da kaɗa jiki da
girgiza shi da rausaya don nishaɗi musamman in akwai kiɗa. Rawar ‘yan mata kuwa suna yin ta ne ta hanyar kaɗa jiki da girgiza da
rausaya a cikin da’ira ko kuma su jeru a layi guda ɗaya. Ta farko idan ta zo
sai ta yi rawa daga nan sai ta juya ta zagaya ta koma bayan ‘yar’uwarta.
Idan aka
dubi hikimar da ke cikin wannan karin magana za a ga cewa duniya ba ta rawa,
amma sai aka siffanta ta da yanayin yadda ‘yan mata suke rawa. A nan ana magana
ne a kan yadda ɗabi’ar duniya take yau gare ka gobe ga ɗan’uwanka, shi ya sa ta
zama rawar ‘yan mata wanda yake gaba zai iya dawowa baya. Ana amfani da wannan
karin magana ne domin a nuna wa mutane cewa rayuwar duniya ba ta da tabbas,
tana juyawa ne kamar yadda ‘yan mata suke juyawa idan suna rawa. Tana iya sauyawa
a kowane lokaci, wanda yake sama ya dawo ƙasa. Idan
dama a hanunka take za ta iya kuɓucewa ta koma hanun wani daban.
Mawaƙin ya yi amfani da wannan karin magana ne domin yin habaici ga
wani da suka samu takun saƙa a tsakaninsu a inda yake
nuna masa cewa duk damar da yake da ita mai iya gushewa ce ta koma hannun wani.
Misali na 3:
Jagora:
Dakata ki ji zancen,
: Ubansu
Auwalu gamzaki,
: Baba
sai an yi gayya,
: Tukun
a ɗau jinkar ɗaki,
: Sannu
Baban Umar,
: Abin
kwatancen mai mulki,
: Ga uban
Fauziya,
: Farida
mai babbar mota,
‘Y/Amshi:
Sarkin Gandun Zazzau,
Jagora:
Sai Sama’ila ɗan Musa,
‘Y/Amshi:
Baba sarkin dattaku,
: Gaskiya
ta yi halinta.
(Muhammad, 2019, sh. 172). Waƙar ‘Sarkin Gandun Zazzau’.
A wannan ɗan waƙa na
misali na 3 da
ya gabata, Ningi ya yi amfani da hikima wajen isar da saƙonsa a inda ya yi amfani da
karin maganar nan na Hausawa da ke cewa, “Hannu ɗaya ba ya ɗaukar jinka”. A nan makaɗin ya yi amfani ma’anar da karin maganar ne ya baddala shi ta siga
daban, ya mayar da shi “Sai an gayya tukun ɗau jinkar ɗaki”.
Jinka na
nufin hayin ɗakin ciyawa. Ɗaki kuwa ana iya bayyana
shi da ginin da aka yi da ƙofa don kwanciya ko ajiya
ko yin wani abu. Jinkar ɗaki kuwa ita ce rufin da ake yi da ciyawa a ɗora a kan ɗaki domin yin maganin rana
ko ruwan sama. Ita jinka duba da girma da nauyi da take da shi, ba zai yiwu
mutum guda ya iya ɗora ta a kan ɗaki ba, sai an yi mata taron dangi, kamar yadda Bahaushe ke
cewa, “Hannu da yawa magani ƙazamar
miya”.
A nan
mawaƙin yana sanar da mutane cewa, Sarkin Gandun Zazzau ya fi ƙarfin mutum ɗaya ne, wato sai dai taro.
2.2 Kirari
A ra’ayin Gusau (2002) ya
bayyana cewa:
Kirari shi ne faɗin wasu kalmomi ga kai ko
wani waɗanda za
su sa a ji daɗi ko a cim ma wani girma a idon jama’a. A wajen gina kirari akan
yi amfani da nasabar mutum tun daga iyayensa har zuwa ‘ya’yansa da matansa da
sauran danginsa, ko a yi amfani da kalmomin bunƙasawa ko
sunayen manyan dabbobi da na sauran abubuwa. (sh. 38).
Dangane
da wannan ma’ana da aka kawo a sama, za a iya bayyana kirari da cewa salo ne da
ake amfani da wasu kalmomin kambamawa ko cicciɓawa, domin a fito da darajar mutum ko wani abu. A wajen fito da
darajar akan ambaci nasabar mutum ko wani abu da yake da alaƙa da shi.
Haruna
Ningi yana amfani wannan salo na kirari a wasu waƙoƙinsa na sarauta domin isar da saƙo ga masu
sauraro, kamar haka:
Misali na 4:
Jagora:
Taso garzaƙu noman wuya,
: A nai
ka ana kuka,
‘Y/Amshi:
Iye iye,
Jagora:
Duk wani mai kwaɗayin gudu,
: Ku ce
da shi ya guje laka,
‘Y/Amshi:
Iye iye,
Jagora:
To sai iskar rani,
: Mai sa
mutum ya sake shirin jinka,
‘Y/amshi:
Iye iye,
Jagora:
Ruwa da kada kai ne,
: Lawal
mutum ba zai matsi baƙi ba,
‘Y/Amshi:
Ka ja mu zuwa Zanna Katsina,
: Alhaji
Lawan Musa,
:
Mahassada ba za su iya ma ba.
(Muhammad, 2019, sh. 149). Waƙar ‘Zannan Katsina’
Ta
la’akari da abin da aka nazarta a wannan ɗan waƙa da aka kawo a
misali na 4, mawaƙin ya
yi wa Zannan Katsina kirari a inda ya yi amfani ɗa kalmomin cicciɓa daraja irin su, ‘garzaƙu’ da ‘iskar rani’ da kuma
‘ruwa da kada’, duk domin ya fito da darajarsa ta
hanyar kirari. Garzaƙu noma ne da ake yin sa cikin wahala, saboda ana yin sa ne cikin
yunwa, gida ba abin da da za a ci, ga kuma ƙasa a
bushe saboda rashin ruwa. To shi noma ne na dole, domin in ba a yi ba, halin da
za a shiga, sai ya fi wanda ake ciki. Iskar rani ita ce iskar da ake yi da rani
wadda ba ruwa za ta kawo ba, zafi gare ta. Mawaƙin ya
siffanta Zannan Katsina da waɗannan abubuwa ne duk
don kambama Zannan Katsina ta amfani da salon kirari
Misali na 5:
Jagora:
Baba toron giwa ne,
: Bai
tsoron karkanda,
: Bindiga
mai harsashi,
: Maganin
‘ya’yan gunda,
: Ga uban
Ummu da Zainab,
: Mai
tsawon rayi leda,
: Ga uba
gun su Aliyu,
: Wanda
bai son lalata,
‘Y/Amshi:
Sarkin Gandun Zazzau,
Jagora:
Sai ama’ila ɗan Musa,
‘Y/Amshi:
Baba sarkin dattaku,
: Gaskiya
ta yi halinta.
(Muhammad, 2019, sh. 176).
Waƙar ‘Sarkin Gandun Zazzau’
Shi ma wannan ɗan waƙar na misali na 5 da ya gabata, yana bayyana hikimar
Haruna Ningi wajen yin amfani da salon adon harshe na kirari, a inda ya
kururuta Sarkin Gandun Zazzau da kalmomin zugugutawa irin su, ‘toron giwa’ da
‘bindiga’ da ‘leda’. Toron giwa shi ne gawurtaccen ko riƙaƙƙen namijin giwa. Bindiga
kuwa wani irin makami ne da ake sa wa harsashi, domin harbawa wajen yaƙi ko farauta. Ita kuma leda wani mazubi ne na zamani da ake amfani da ita wajen
zuba abin masarufi.
Saboda
haka Haruna Ningi ya kwatanta Sarkin Gandun Zazzau da toron giwa wanda ba ya
jin tsoron karkanda. Karkanda wata dabbar daji ce mai girma da ɗan ƙaramin ƙaho a hanci. Ya yi wannan
kwatance ne don ya fito da jarumtar Sarkin Gandu a idon masu sauraro. Sannan
kuma ya kira shi da bindiga da leda ne duk don ya kuranta shi ya fito da
darajarsa. Haka kuma ya ambaci sunayen ‘ya’yansa, domin ya fayyace iyalansa ta
hanyar kirari.
Misali na 6:
Jagora:
Ga ruwana da kada,
: Ku cewa
mai su na shirya,
: Ga
kutungu ɓauna,
: Ina da
mai ƙaryar laya,
: Ga gari
mai nisa,
: Zuwanka
sai am ma niya,
: Mai
kare kama karenka,
: Masu
kura sun sau ta,
‘Y/Amshi:
Sarkin Gandun Zazzau,
Jagora:
Sai Sama’ila ɗan Musa,
‘Y/Amshi:
Baba sarkin dattaku,
: Gaskiya
ta yi halinta.
(Muhammad, 2019, sh. 179). Waƙar ‘Sarkin Gandun Zazzau’
A
wannan ɗan waƙa na misali na 6, Haruna Ningi ya yi amfani da salon kirari ta
hanyar kwarzanta Sarkin Gandun Zazzau a inda ya kira shi da, ‘kutungun ɓauna’ da ‘gari mai nisa’
duk domin ya fito da darajarsa.
Misali na 7:
Jagora:
Mai al’umma masoyin kowa,
‘Y/Amshi:
mai mutane,
Jagora: Ɗanyen kara mahorin wawa,
‘Y/Amshi:
Mai mutane,
Jagora:
Mai sa maza gudu sai tsawa,
‘Y/Amshi:
Mai mutane,
Jagora:
Jikan Nagwaggo mai kama ruwan,
: Masu
gaba,
‘Y/Amshi: Mai martaba Lawal Ɗan Musa,
Jagora: Ɗan Nagwaggo,
‘Y/Amshi:
Allah tsare ka Sarkin Wamba,
: Sannu
Baba.
(Muhammad, 2019, sh.
204). Waƙar ‘Murnar Naɗin Sarkin Wamba’
.
Idan aka
dubi wannan ɗan waƙa na misali na 7 da ya gabata, Haruna Ningi ya yi amfani da salon
kirari, ya yabi Sarkin Wamba, Alhaji Lawal Musa, a inda ya nuna cewa shi mutum
ne mai son jama’a, sannan kuma ya yi amfani da kalmomi kambamawa irin su
‘danyen kara’ da ‘tsawa’. Ɗanyen kara shi ne karan
dawa ko gero ko takanɗa da makamantansu wanda bai bushe ba mai wahalar karyuwa. Tsawa
kuwa ita ce wata ƙara haɗe da walƙiya da ke bayyana a yayin da ake ruwan sama. Duk a yanayin da
mutum yake ciki sai gabansa ya faɗi a yayin da aka yi tsawa. Sannan tana da illa idan ta faɗa a kan mutum ko bishiya.
Mawaƙin ya kira Sarkin Wamba da waɗannan sunaye ne, duk don ya kambama shi ya fito da daraja da ƙimarsa da illarsa in ka takale shi a idon masu sauraro. Sannan
kuma ya faɗi
nasabarsa ta hanyar ambato sunan kakansa, domin bayyana asalinsa ta hanyar
kirari.
2.3 Habaici
Gusau
(2002) yana da ra’ayin cewa:
Habaici wasu kalmomi ne da
ake faɗa a
fakaice don a ɓata wa wani mutum rai, ba tare da an bayyana mutumin da ake
nufi ƙuru-ƙuru ba. Habaici ya fi zambo sauƙi. Domin
akwai sakaya zance a cikinsa, wato ba a fitowa fili ƙarara a yi wa mutum shi, kuma ba a faɗin wata fitacciyar siffar
mutum ko wani fitaccen halinsa. Kalmomin sakayawa da ake amfani da su a habaici
sun haɗa da
‘wane ko ‘wanga’ ko waɗanga’ da sauransu. Domin haka ake cewa; habaici riga ce duk wanda
ya sa za ta shige shi. (sh. 37)
Ta kallon
wannan ma’ana, ana iya cewa habaici kalmomi ne da ake amfani da su don a muzantawa
wani ya ji haushi, zuciyarsa ta sosu. A wajen yin habaici ba a fitowa ƙarara a bayyana da wanda
ake da shi, sai dai akan yi amfani da waɗansu kalmomi kamar wani ko wasu ko wane ko wanga da
makamantansu.
Haruna
Aliyu Ningi yana amfani da wannan salo na habaici a waƙoƙinsa na sarauta. Ga abin da yake cewa:
Misali na 8:
Jagora:
Ke waccan matar,
: Ki san
da ke nake maganar Zanna,
‘Y/Amshi:
Iye iye,
Jagora:
Abin da yake inuwa,
: In ba
wuya ba ba ya zuwa rana,
‘Y/Amshi:
Iye iye,
Jagora:
Da ke fa da shi sai dai,
:
Ubangijinmu ɗai a bayanaina,
‘Y/Amshi:
Iye iye,
Jagora:
Don shi yaka yin ikon da mu,
: Ba za
mu fasa iyewa ba,
‘Y/Amshi:
Ka ja mu zuwa Zanna Katsina,
: Alhaji
Lawan Musa,
:
Mahassada ba za su iya ma ba.
(Muhammad, 2019, sh. 152). Waƙar ‘Zannan Katsina’
A wannan ɗan waƙa da ya gabata a misali na 8, Haruna Ningi ya yi amfani
da hikima a inda ya yi habaici ga wata mata da Zannan Katsina ya kashe wa maƙudan kuɗaɗe a lokacin da yake neman aurenta, amma sai ta yaudare
shi ta auri wani mai riƙe da sarauta. To cikin
ikon Allah sai aka yi masa sarautar da ta fi ta wancan wanda ta aura martaba da
daraja.
Misali na 9:
Jagora:
Duk wani ɗan sarki,
: Abin da
zan faɗe shi ba
zai so ba,
‘Y/Amshi:
Iye iye.
Jagora:
Albarkar Umar Kabiru,
: Ni ba
zan muku zambo ba,
‘Y/Amshi:
Iye iye.
Jagora:
Amma za ku jira shi,
:
Shekara ɗari ba ku karɓa ba,
Jagora:
Don na yi mafarki ne,
: Jiran
gidanku ban ga iyaka ba,
‘Y/Amshi:
Ka ja mu zuwa Zanna Katsina,
: Alhaji
Lawan Musa,
: Mahassada
ba za su iya ma ba.
(Muhammad, 2019, sh. 153). Waƙar ‘Zannan Katsina’
Idan aka
kalli wannan ɗan waƙa da ya gabata a
misali na 9,
Haruna Ningi ya yi zambo ne ga wani ɗan gidan sarauta waɗanda ya nuna adawarsa a kan Zannan Katsina, a inda yake
cewa sai dai ya mutu da baƙin ciki, domin ko zai yi shekara ɗari a duniya ba zai sami sarautar Zanna
ba. Saboda sarautar ta gidansu
Alhaji Lawal Musa ce su kaɗai kuma ahalin gidan ne za su yi ta gadarta.
Misali na 10:
Jagora:
Mai dashen karmami,
: Ku ce
meye hujjojinsa,
: Masu
shukar dusa kwa,
: To
basira ta kasa,
:
Tambayoyin da na kai,
: Ba
zan ɓace ba ya
ban amsa,
: Mai harara a duhu,
: To wanga aikin banza ta,
‘Y/Amshi:
Sarkin Gandun Zazzau,
Jagora:
Sai Sama’ila ɗan Musa,
‘Y/Amshi:
Baba sarkin dattaku,
: Gaskiya
ta yi halinta.
(Muhammad, 2019, sh. 179). Waƙar ‘Sarkin Gandun Zazzau’
A
wannan ɗan waƙa da ya gabata a misali na 10, Haruna Ningi ya fito da balagarsa
ta hanyar amfani da kalmomin habaici irin su ‘dashen karmami’ da ‘shukar dusa’
da ‘harara a duhu’. Dashen karmami na nufin sake shukar bushasshen ganyan dawa
da makamantansu. Shukar dusa kuwa na nufin binne furkaki da yake fita daga
jikin ƙwayar hatsi bayan an sirfa shi. Ita kuwa harara a duhu na nufin
kallon mutum da gefen ido domin tsorata shi ko kuma hana shi aikata wani abu a
cikin duhu ba tare da yana gani ba. Dashen karmami da shukar dusa dukkanninsu
wahalar banza ne, domin ba yadda za a yi a amfana da su. Harara a duhu kuwa
daidai take da ɓata lokaci, domin wanda aka harara bai san ana yi ba.
Domin
haka makaɗin ya yi
habaici ne ga wasu mutune biyu masu riƙe da Sarauta a ƙasar Zazzau da suke ganin Sarautarsu ta fi ta Sarkin Gandun Zazzau
martaba, amma kuma ya fi su samun ƙarɓuwa a wajen Sarkin Zazzau
da sauran jama’ar gari, sai suke ta nuna hassada da baƙin ciki tare da yada maganganu a bayan fage.
Misali 11:
Jagora: Wani
an yi mar naɗi yai girma,
‘Y/Amshi: Mai mutane.
Jagora: Ya kasa yin bikin sai gulma,
‘Y/Amshi:
Mai mutane.
Jagora:
In ban da masu hangen kurma,
‘Y/Amshi: Mai mutane.
Jagora:
Ya kogi ya rinƙa kyashin gulbi,
: To bar
shi baba,
‘Y/Amshi:
Mai martaba Lawal ɗan Musa,
Jagora: Ɗan Nagwaggo,
‘Y/Amshi: Allah tsare ka sarkin Wamba,
: Sannu
Baba.
(Muhammad,
2019, sh. 201). Waƙar ‘Murnar Sarkin Wamba’
A
wannan ɗan waƙa na misali na 11 da aka kawo a baya, mawaƙin ya fito da balagarsa a inda ya yi amfani da kalmmin habaici
irin su ‘gulma’ da ‘hangen kurma ‘ da ‘ƙyashi’. Gulma tana
nufin ɗaukar
zance daga wani zuwa wani ta yadda zai kawo saɓani a tsakani. Hangen kurma kuwa hange ne da yake gano wani a nesa
amma ba halin ya yi masa magana. Shi kuwa ƙyashi shi
ne kishin da mutum ke nunawa idan wani ya sami wani abu.
Saboda
haka mawaƙin ya yi amfani da dabarar adonta harshe ta baubawan burmi wadda
ta haifar da mutuntarwa. Kogi da ƙyashi kalmomi ne gamin
bauta, ba ta inda suka haɗu da juna. Kogi abu ne marar rai aka danganta shi da ƙyashi wanda yake ɗabi’a ce wadda aka san ta a wajen ɗan’adam. A nan an mutumtar
da kogi ta hanyar ba shi ɗabi’ar mutum ta ƙyashi.
Makaɗin ya yi amfani da waɗannan dabaru ne domin yin
habaici ga wani da aka yi wa Sarauta, ya nuna cewa Sarautar da aka yi masa ta
fi ƙarfinsa, domin ya kasa taɓuka komai sai hassada da gulmace-gulmace.
3.0 Kammalawa
Kamar
yadda bayanai suka gabata a wannan maƙala, an yi nazari ne
dangane da yadda Haruna Aliyu Ningi yake sarrafa wasu daga cikin maganganun
hikima, waɗanda suka
haɗa da
karin magana da kirari da habaici a wasu waƙoƙinsa na sarauta.
A
takardar an fara da kawo tarihin Haruna Aliyu Ningi a taƙaice. Haka kuma an kawo ma’anar maganganun hikima da ma’anar karin
magana da kirari da habaici daga masana da manazarta daban-daban. An kuma kawo
misalai da bayanan yadda Haruna Ningi yake amfani da waɗannan dabaru na Karin
magana da kirari da kuma habaici wajen ƙawata waƙarsa, da yi mata kwalliya tare da jawo hankalin masu sauraro
daga ɗiyan wasu
waƙoƙinsa na sarauta. Har ila yau, an fito da waɗannan dabaru na karin
magana da kirari da habaici daga ɗiyan wasu waƙoƙin sarauta na Haruna Aliyu Ningi, tare da yin nazari da sharhinsu.
Manazarta
Abba, M. da Zulyaidaini, B.
(2000). Nazari kan waƙar baka ta Hausa. Gaskiya Corporation Company.
Ahmad, A. M. (2011). Matsayin
habaici a zantuttukan hikimar Hausa. [Kundin digiri na biyu]. Jami’ar Amadu
Bello.
Ahmad, M.I. (2016). Maganganun
azanci a waƙoƙin Malam Aƙilu Aliyu: Tsokaci a kan kirari da zambo [Takadar da aka gabatar domin neman shawarwari da kuma
cikasa wata ƙa’ida ta neman digiri na uku]. Jami’ar Bayero.
C.N.H.N, (2006). Ƙamusun Hausa. Ahmadu Bello University
Press.
Ɗangambo, A. (2011). Rabe-raben adabin Hausa (sabon tsari). KDG
Publishers.
Gusau, S. M. (2002). Sarkin
taushi Salihu jankiɗi. Baraka Press and
Publishers.
Gusau, S. M. (2003). Jagoran
nazarin waƙar baka. Benchmark Publishers.
Gusau, S. M. (2011). Adabin
Hausa a sauƙaƙe. Century Research and Publishers.
Gusau, S. M. (2015). Abdu
karen Gusau. Century Research and Publishing.
Hussaini, B. (2009). Haruna
Aliyu Ningi da wasu waƙoƙinsa. Ramadan Press.
Muhamamd, H. I.
(2019). Nazarin adon harshe a waƙoƙin sarauta na Haruna Aliyu Ningi. [Kundin
digiri na biyu]. Jami’ar Bayero.
Satatima, I.G. (2013).
Salon tsarma karin magana cikin waƙoƙin siyasa: Tsokaci daga wasu fitattun waƙoƙin jamhuriyya ta huɗu zuwa yau. Harsunan Nijeriya, ƊƊIII 271.
[1] Hussaini
(2009)
[2] Satatima
(2013, sh. 271)

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.