TUBALIN KARAMCI A GININ WASU WAƘOƘIN MAMMAN SHATA KATSINA
Daga
Muhammad Abubakar Zabi
Sashen Koyar Harsunan Nijeriya
Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo,
Sakkwato
TSAKURE
Al’ummar Hausawa al’umma
ce da ta kasance tana cuɗanya da mutane daban-daban masu al’adu mabambanta tun
shekaru da yawa. Karamci da mutuntawa da kuma kyautatawa a cikin al’umma na
nuna ingantuwar al’umma bisa ga tubalin nagarta da kowace al’umma ke son ta
kasance da shi. A farkon rayuwar al’ummar Hausawa ta kasance bisa tsarin
gargajiya wanda tun a wancan lokacin al’ummar Hausawa an san su da karamci da
kyautatawa. Daga baya kuma addinin Musulunci ya zo ya sake ƙarfafa musu waɗannan
al’adu da ɗabi’un. Wannan ɗabi’a
ita ce ta ɗauki al’ummar Hausawa zuwa wani mataki na musamman.
Daga ƙarshe
Turawa sun zo sun kawo wayewa irin tasu da samun ci gaba irin na zamani, duk da
haka karamcin Bahaushe bai samu wata tawaya mai yawa ba. Idan aka duba adabin
Hausa za a samu cike yake da karamci da kuma kyautatawa musamman a sassansa na
karuruwan magana, tatsuniya, labarai da kuma waƙoƙi. A wannan takarda za a yi ɗan tsokaci ne game da Tubalin karamci a ginin wasu waƙoƙin Alhaji Mamman Shata Katsina.
1.0
Gabatarwa
Ba shakka, Allah,
Ubangiji, mai Jinƙai mai Rahama ya
ba ɗan’adam ikon yin karamci ta fuskar girmamawa da
kyautatawa da kuma nuna halin dattako ga abokan zaman rayuwa.
Newman (1997) yana
ganin, karamci shi ne halin kyauta ko kuma wata baiwa daga Ubagiji.
Akwai hanyoyi da dama da
za a iya yin nazarin karamci na al’ummar Hausawa.
Ita wannan takarda za ta
zaƙulo irin karamci da sarakuna suke yi wa
al’ummar Hausawa kamar yadda Alhaji Mamman Shata Katsina ya nuna a cikin wasu
waƙoƙinsa.
1.1 Taƙaitaccen Tarihin Alhaji Mamman Shata Katsina
An haifi Alhaji Mamman
Shata Katsina a zamanin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko, kuma ya yi wayo a
zamaninsa. Wasu kuma sun ce an haifi Alhaji Mamman Shata Katsina a zamanin
Sarkin Musawa Yero.An kuma haifi shi ne a unguwar sanyinawa a cikin garin
Musawa a ƙasar Katsina a wajen
shekarar mutuwar shanu. Sunan mahaifinsa Alhaji Ibrahim Yaro, sunan
mahaifiyarsa Lariya. (Attahiru, 2012:22)
A lokacin kuruciyar
Alhaji Mamman Shata bai tashi a cikin halin rashi ba domin shi ɗangata ne, iyayensa na da hannu da shuni irin na
zamaninsu. A wajen shekara ta 1928, lokacin da Alhaji Mamman Shata ya cika
shekara biyar da haihuwa, sai aka sanya shi a Makarantar Allo a cikin Musawa
domin ya koyi karatun Alkur’ani ilimin addinin Musulunci kamar
yadda ’Yaýan Hausawa ke yi tun suna ƙanana (Sheme, 2006).
A wajen shekara ta 1932,
bayan sana’ar da ya gada ga iyayensa ta noma da harbi da kuma kiwo, sai ya fara
tallace-tallace na kayan masarufi. Babbar sana’ar Shata da aka fi saninsa da
ita, ita ce Tallar goro kafin ya soma wannan
sana’ar sai da ya fara tallar alewa. A duk lokacin
da ya je talla a dandali ko kasuwa sai ya riƙa ciko hannunsa da goro yana ba duk wanda ya zo saye,
maimaikon ya ba mutum na daidai da ƙuɗin da ya bayar ba tare da ya ƙidaya ba. Wannan shato goro da yake yi ga masu saye ba
tare da ƙidaya ba, shi ne asalin
sunansa na Shata wato daga shato goro ne ya sami laƙabin shata. (Attahiru 2012:25)
Mamman Shata ya fara waƙa ne a dalilin wata gasa da ake shiryawa ta waƙe-waƙe musamman lokaci ne ake
waƙoƙin Asauwara. A wannan gasar a kan shirya wasanni
iri-iri. Duk lokacin da aka shirya gasar waƙa da Mamman Shata ne ke zama zakaran gasar saboda haka
sai ya zama Sarkin Waƙa na musamman. A wannan
lokacin kuma a gidansu ake sauke Zabiya wato sarauniyar waƙa ta ɓangaren mata. Wata rana a fagen wasa
Mamman Shata da baƙuwarsa Zabiya za su riƙa takara, amma wannan ba zai ɓata alaƙarsu ta mutunci ba. Ana rera wannan waƙa ce a lokacin da aka zo wasan kwaikwayo a tsakanin
samari da ýan mata. Mamman shata yakan yi waƙa ne domin sha’awa, ko mutane sun ba shi kuɗi ba ya karɓa. Amma da tafiya ta yi tafya sai ya
kasance yana karɓar kuɗi da wasu kyautuka. Yana a kan hakan sai waƙa ta ɗore gare shi ta zama mawakin baka mai
hikima.
2.0 Sarakuna
Kalmar Sarakuna, kalma
ce ta jam’i, Sarki kuma tilo ke nan. Sarauta ta Sarakuna ta kafu a ƙasar Hausa a kan halayen girma da mutuntaka wato
halaye da ke mai da ɗan’adam mutum na gari mai amfani ga kansa da al’ummar
da yake rayuwa a cikinta. (Mashi 2013:438) kamar yadda masana da manazarta suka
ce:
Sarauta kuma tana nufin
“Shugabanci” ko “Jagoranci” cikin tafiyar da al’amuran jama’a. (Mashi 2013:
439)
Zai a iya cewa Sarauta
tana nufin Shugabanci musamman irin na gargajiya (CNHN, 2006:391)
Sarki kuma, mutumin da
aka naɗa ta hanyar gargajiya don ya shugabanci mutane ta
hanyar mulki ko sana’a ko wani abu (CNHN, 2006:392)
Haka kuma karamci hali
ne na kyautatawa ko nuna alheri. Yana daga cikin karamcin sarakuna amsar baƙi da sauƙar da su idan suka shigo ƙasarsu (Ɗanmaigoro, 2013:535)
A wata ma’anar ta sarki:
Sarki shi ne babban jagora ga al’ummar gari. Haka kuma, shi ke da iko ga ƙasa da duk abin da ke cikinta (Ainu 2013:467)
A tsarin Sarautar
gargajiya, sarki shi ne shugaba, duk sauran jama’ar da ke ƙasarsa suna bin umurninsa ne. wannan tsarin shi ne ake
bi tun kafin zuwan Musulunci da da na Turawa, har zuwa wannan lokaci. An ɗauki sarakuna a matsayin iyayen ƙasa.
Su sarakuna suna tafiyar
da mulki ne ta wani tsari na hawa- hawa. Watau, suna da mataimakansu masu muƙamai, wannan na gaba da wannan. Tun daga Hakimi na
kusa da sarki, zuwa Dagaci na ƙasa da Hakimai, zuwa masu Anguwanni masu bin umurnin
Dagatai (Yahaya da wasu 2001).
Don haka bisa yadda
masana da manazarta suka ce game da mene ne Sarki za mu iya cewa Sarki shi
ne, jagoran al’umma ta yadda zai iya sa doka da yin hukunci, da kuma kare
mutunci al’ummarsa ta kowace fuska.
3.0
Karamci
Karamci baiwa ce da
Allah yake ba wa wasu mutane na musamman. Hanyoyin karamci suna da yawan gaske,
kama daga zumunci da kyauta da saukar baƙi da kuma girmama magabata da sauransu. Karamci
a ƙasar Hausa abu ne da aka saba da shi tun
fil azal. Ba a abu ne sabo ba, fada daman can dauri Sarakunan ƙasar Hausa an sansu da karamci da girmama al’umma.
Domin an yi zamanin da a ƙasar Hausa duk wani baƙo da ya zo ƙasar fada yake tafiya kai tsaye nan ne gidansu, a nan
ne za a ba shi muhalli da abinci da zai ci wani lokaci ma har da wurin noma da
matar da zai aura.
Kamar yadda Kamusun
Harshen Hausa na Jami’ar Bayero ya bayyana, karamci yana nufin kyautatawa ko
nuna alheri. (CNHN, 2006:233)
Don haka, za a iya cewa
karamci kyautatawa ne da nuna halin dattaku ga al’umma baki ɗaya.
4.0
Wasu Tubalan Karamci a Wasu Waƙoƙin Shata Karamci
Daga ilimin tubulin
karamci da Shata ya yi amfani da su ya zuba ya ƙarfafa wasu waƙoƙinsa da su, akwai kyauta
ta girmama jama’a da sauƙar baƙi da kuma sa da zumunci. Ga wasu misalai daga ɗiyan waƙoƙin Shata kamar haka:
4.1
Kyauta da Girmama Jama’a
Dr. Mamman Shata, ya
tabbatar da Sarakuna masu karamci ne wanda ya danganci kyauta, waƙar da Shata ya yi wa Sarkin Rano Alhaji Abubakar ya
ayyana shi da Sarki mai yawan kyauta, kamar haka:
Jagora :Idan ya tashi
kyautar doki,
:Danda fari biyar ya miƙa min,
‘Y/Amshi :Mai Rano Garba
autan Bawo.
Jagora :kuma ya ban
sirdin Turawa,
:Wanda suke kira H.L.D,
‘Y/Amshi :Mai Rano Garba
autan Bawo
Jagora :Ga hular darar
mulki,
:Ga harsa na bai mai
ganga,
‘Y/Amshi :Mai Rano Garba
autan Bawo
(Gusau 2014:441-442)
A waɗannan ɗiyan Mamman Shata ya faɗi an ba shi kyautar doki da sirdi da kuma hula irin ta
masu mulki. Wannan yana daga cikin hali da ɗabi’a ta girma da
Sarakunan ƙasar Hausa suke yi wa
jama’arsu.
Haka kuma, ya sake kawo
irin karamci da kyauta ta sarakunan Hausawa inda yake cewa:
Jagora :Ga ka ina
kallo ɗan umaru,
:ban rashin sutura ko
kurɗi,
’Y/Amshi :Lafiya zaki,
:Mamman baban
Galadima ɗan umaru.
Jagora :Ga ka ina
kallo ɗan Musa,
:ban rashin doki ɗan Musa,
’Y/Amshi :Lafiya zaki,
:Mamman baban
Galadima ɗan Musa.
Jagora :Ga baba da rai
Bashari ɗan Musa,
:ban rashin mota ɗan Musa,
’Y/Amshi :Lafiya zaki,
:Mamman baban
Galadima ɗan Musa.
Jagora :Ni yanzu wajen
kyauta Bashari,
:Ka ba da kasha sai
gyara,
’Y/Amshi :Lafiya zaki,
:Mamman baban
Galadima ɗan Musa.
Jagora :Komai ka yi
yanzu gyara ne ɗan Musa
’Y/Amshi :Lafiya zaki,
:Mamman baban
Galadima ɗan Musa.
Jagora :Komai ka yi
yanzu gyara ne ɗan Musa,
’Y/Amshi :Lafiya zaki,
:Mamman baban
Galadima ɗan Musa.
(Gusau 2014:430)
Idan aka kalli waɗannan ɗiyan waƙa za a ga karamci na kyautar Sarkin Daura, Alhaji
Bashir ya ɓulla a fili ƙarara, mussaman ta haƙiƙanin da ya yi idan Baba
ya yana nan bai rasa sutura da doki ko kuma mota. Saboda irin karamcinsa da
kyautatawarsa.
4.2 Kula da Iyaye
Haka kuma, Shata yana
nuna hali na karamci irin na sarakuna ta fuskar girmama da ɗauke musu nauyin abin da suke yi. Alal misali, ya kawo
yadda ya yi ta bin sawun ayyuka na alheri na magabatansa ya ci gaba da aiwatar
da shi: yana cewa Sarkin Kano Alhaji Ado Bayero.
Jagora :Akwai zance da
mukai ni da Ado,
:Ado Sanusi jikan Sarki
Abdu,
:Ado babban jikan
Sarki Abdu,
:Lokacin da Ado ya
sami Sarauta,
:Ya tafi ya durƙusa gaban tsohonsa,
:Da dai ya gai da
sanusi Mamman,
:Ya ce Sanusi waɗanda kake wa aure,
:Waɗanda ban ni da su nai musu,
:Waɗanda kake ba wa ragon suna,
:Waɗannan ban ni da su na ba su,
:Mamman wanda kake
ba wa kuɗi,
:Waɗannan ban ni da sun a ba su ka tuna,
:Da waɗanda kake ba wa ragon suna,
:Wannan ban ni da
sun a ba su,
:Ka tuna da waɗanda kake ba wa gero,
:Waɗannan ban ni da su na ba su,
:Sanusi ban ni da
su na ba su,
:Tuna da waɗanda kake ba wa dawa,
:Su ma ban ni da
su na ba su,
:Af waɗanda kake ba wa ragon layya,
:Su ma ban ni da
su na ba su,
:Can sai Sunusi y
ace, Allah ma albarka,
:Duk wanda ubansa
y ace sambarka,
:Yaya za ai ya
rasa yin albarka,
‘Y/Amshi :Sadauki Shehu
magajin Mamman.
(Gusau 2014:440)
4.3 Sauƙar Baƙi
Haka dai, ya ci gaba da
kawo karamci na Sarakuna ta fuskar sauƙar baki da ba su masauƙi mai kyau. Kamar haka:
Jagora :Ranar saukarmu
cikin Bauchi,
:An ba mu masauƙi mai kyauwo,
:Komi na karɓa nan Bauchi,
:ƙarshe kuma har an ban mota,
:Ni babu abin da
ya ƙonan rai,
:Na so in ga sarki ban
ga shi ba.
’Y/Amshi :Mai Bauchi
Sulaimanu Adamu
(Gusau 2009:268)
Wannan halayya ta
sarakuna ta saukar baƙi da ya nuna tana daga
cikin hanyoyin karamci. Ya ce ranar da suka sauka Bauchi an ba su masauƙi mai kyawo ga kuma, kyautar mota.
A wani wurin ya kuma
kawo yadda Sarakuna suke saukar baƙinsu, kamar haka:
Jagora :Idan Sallah ta
taho mu tarbi baƙinmu in sun zo,
’Y/Amshi :Lafiya zaki,
:Mamman baban
Galadima ɗan Musa
(Gusau 2009:253)
Haka yake a sallah ana
samu baƙi suna zuwa daga yankuna na karkara, waɗanda sukan zama baƙi na Sarakuna kuma ake yi musu masauƙi da abinci da tsaraba.
4.4 Alheri na Mazauwa
Fada
Dubi abin da yake faɗi na zumunci da alherin Sarki Ado:
Jagora :Ga alheri ga sa
da zumunci,
:Ado San Kano ɗan Bello ,
‘Y/Amshi :Ado San
Kano ɗan Abdu
Jagora :Ga alheri ga sa
da zumunci,
:Ado San Kano ɗan Bello
‘Y/Amshi :Ado San
Kano ɗan Abdu.
Jagora :Dattawa suna
sambarka,
:’Yan yara suna sun
gode,
‘Y/Amshi :Ado San
Kano ɗan Abdu.‘
(Gusau 2009:276-277)
Baya ga sarakunan kansu
na ƙarƙashinsu ma na yin kyauta da alheri saboda Sarki. Ga
yadda ya nuna haka:
Jagora :Na ce mashi
Ashahura Allah ma albarka,
‘Y/Amshi :Alhaji Sarkin
Zazzau Shehu.
Jagora :Haji Ashahura
Allah ma sakayya,
‘Y/Amshi :Alhaji Sarkin
Zazzau Shehu.
Jagora :Cif naira metan
yab ba ni,
:Saboda Sarkin Zazzau
Shehu,
‘Y/Amshi :Alhaji Sarkin
Zazzau Shehu.
Jagora :Na ce da shi
Allah ma sakayya,
‘Y/Amshi :Alhaji Sarkin
Zazzau Shehu.
(Gusau 2009:266)
Wannan shi ya ƙara tabbatar da fada gidan karamci da alheri ce. Ga
kuma wani misali:
Jagora :Na gode Filani,
:Domin San Kano ɗan Ali
‘Y/Amshi :Ado San
Kano ɗan Abdu
Jagora :Alhaji Garba nag
ode mai,
:Domin San Kano ɗan Ali
‘Y/Amshi :Ado San
Kano ɗan Abdu,
Jagora : Babban doki
manya kaya,
:Ga jikkunan nan an ba
Mammam,
:Domin San Kano ɗan Abdu,
‘Y/Amshi :Ado San
Kano ɗan Abdu
Jagora :Saboda Ado San
Kano ɗan Abdu
‘Y/Amshi :Ado San
Kano ɗan Abdu
Jagora : Alhaji zo ga
Naira metan,
:Ga Naira dubu a b aka,
:Domin San Kano ɗan Ali,
‘Y/Amshi :Ado San
Kano ɗan Abdu.
Jagora :Kyautar doki sai
mai mulki,
;Babbar riga sai mai
mulki,
:Manya kurɗi sai mai mulki,
:Komi na karɓe shi a birni,
:Dimin San Kano ɗan Ali,
‘Y/Amshi :Ado San
Kano ɗan Abdu
Jagora :Mun ce mun gode,
:Ya Allah shi yi ma
sakayyya,
:Baba na Garba wane yaro
‘Y/Amshi :Ado San
Kano ɗan Abdu.
Jagora :Mun gode Ado san
Kano ɗan Bello,
‘Y/Amshi :Ado San
Kano ɗan Abdu.
(Gusau 2009:280-281)
Kamar yadda Dr. Mamman
Shata ya nuna ba lallai sai Sarki ne yake da karamci kawai ba, har ma da sauran
mutanen fada. Kamar ‘ya’yan sarki da bayin sarki da barorinsa a fada da duk
wani wanda ya shafi fada shi ma za a tarar da shi yana da karamci da kyautatawa
irin tasa.
5.0 Kammalawa
A wannan takarda an yi
magana ne dangane da yanayi na yin karamcin Sarakunan Hausawa. Aƙalla an
yi bayani da misalai a kan hanyoyin guda huɗu da suka ƙumshi kyauta da girmama
magabata da kulawa da iyaye da saukar baƙi da kuma
yin alherai na sauran majiɓanta
fada. An kuma ƙarƙare waɗannan
hanyoyi na karamci da misalai na ɗiya daga wasu waƙoƙin Mamman
Shata Katsina.
A wannan nazari an fahimci
ba sarakuna kawai suke yin karamci a fadodinsu kawai ba, har da sauran majiɓanta fada tun daga Hakimai
da Fadawa da wasu Sarauta duka su ma sun sami tasiri da Sarakunansu a yin
Karamci
Manazarta
Ainu, H. A (2013)
Yanaye- yanayen Zamantakewar Hausawa a Mahangar Littafin Ruwan Bagaja.
Unicairo/Umyuk Special Research In humanities: Ruwan Bagaja In Perspectiɓes
Alhassan, H. Ibrahim, U.
Zarruk, M. R. 1982. Zaman Hausawa. Lagos: Academy Press Limited.
Bugu na biyu.
Attahiru, R. (2012)
“Wa}o}in Shata na Mata ”kundi BA: Sakkwato, Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo
Ɗanmaigoro, A. (2013). Karamcin Sarakuna a Cikin
Littafin Ruwan Bagaja. Unicairo/Umyuk Special Research In humanities: Ruwan
Bagaja In Perspectiɓes
Gusau, S. M
(2009). Diwanin Waƙoƙin Baka: Zaɓaɓɓun Matanoni na Waƙoƙin Baka na Hausa,
Kano: century Research and Publishing Limited.
Gusau, S. M
(2014). Diwanin Waƙoƙin Baka: Juzu’I Na biyu,
Kano: century Research and Publishing Limited.
Mashi, A. A (2013)
“Al’adun Hausawa a Tsarin Sarautar Gargajiya a Yau” Eɗcerpts of international
Seminar on Taɓarɓarewar Al’adun Hausa (the Deterioration of Hausa
culture) Organized by Katsina State History and Culture Bureau, in
Collaboration with: Umar Musa Ýar’adua Uniɓersity, katsina
Safana, (2007) Gudumuwar
waƙoƙin Alhaji (Dr.) Mamman Shata Katsina, a fagen bunƙasa sana’o’in gargajiya
Sheme, (2006) Shata Ikon
Allah Rayuwar Alhaji (Dr.) Mamman Shata Katsina
Wurma, G.A. (1991),
“Tasirin Hausawa A Tarihin Afrika Ta Yamma Fassara Littafin: The Hausa Factor
In West African History Na Mahdi Adamu. Kundin Digiri Na Biyu. Sashen Nazarin
Harsunan Nijeriya Da Afrika. Jami’ar Ahmadu Bello, Zaria.
Yahaya da Wasu, (2001)
Darussan Hausa Don Manyan Makarantun sakandare Littafi Na Uku. Ibadan Uniɓersity Press
Zarruk, R. M;
Kafinhausa, A.A; Alhassan, B. S 2009. Sabuwar Hanyar Nazarin Hausa
Don ƙananan
Makarantu Sakandare. Ibadan University Press
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.