Ticker

6/recent/ticker-posts

Nazarin Nau’o’i Da Salon Rubutattun Wakokin Gazal Na Larabci Da Na Hausa

Citation: Abdulrahman, Aliyu (2024) “Nazarin Nau’o’i da Salon Rubutattun Waƙoƙin Gazal na Larabci da Hausa” Algaita Journal of Current Reseach in Hausa Studies, Volume 17, No 1, May 2025. Department of Nigerian Languages, Bayero University, Kano. ISSN: 2141-9434.

NAZARIN NAU’O’I DA SALON RUBUTATTUN WAƘOƘIN GAZAL NA LARABCI DA NA HAUSA

DAGA

Abdulrahman Aliyu
Sashen Koyar Da Harsunan Nijeriya

Jami’ar Umaru Musa Yar’adua, Katsina
ksarauta@gmail.com
08036964354

Tsakure

‘Waƙoƙin Gazal’ sun samo asali ne daga ‘waƙoƙin Larabci, inda suka kasance kamar shimfiɗa ne ga duk wanda zai yi waƙar ƙasida, baitukan da ke ɗauke da waƙoƙin Gazal ba su wuce biyar zuwa sha biyar ba. Suna  ɗauke da bayanin irin kewar da mawaƙi ke ji game da wata masoyiyarsa da ta yi masa nisa ko ya rasa ta. Kamar yadda irin waɗannan waƙoƙin suke a Hausa ma an tusgo su ne daga cikin waƙoƙin soyayya da kuma waƙoƙin da suka shafi kaɗaita Allah da Sufaye ke aiwatarwa da fuskar yaba kyau ko zatin mace. wannan maƙala za ta yi duba ne kan nau’o’i da salo tsakanin waƙoƙin Gazal na Larabawa da na Hausawa. Manufar ƙasidar ita ce, yin kwatancin nau’oi da salon waƙoƙin Gazal na Larabci da na Hausa ta fuskar gano yadda kowane ɓangare suke shirya nasu waƙoƙin tare da yin duba ga waƙoƙin na Larabawa da na Hausa. An bi hanyoyi da yawa wajen ganin an samu nasarar wannan binciken da suka haɗa da tattara waƙoƙin Gazal na Larabci da fassara su zuwa Hausa, da ganawa da masana da yin tambayoyi ga wasu mutane da ke da alaƙa da waɗannan waƙokin. Sannan an yi amfani da kafafen sadarwa na zamani wajen samo bayanai da suka taimaka aka gina kwatancin ta yadda aka riƙa musayar bayanai daga Larabci zuwa Hausa. Ganin yadda wannan nau’i na waƙa ya samu karɓuwa a faɗin duniya, shi ya sa wannan nazarin  ya yi amfani da Ra’in Kwatancin Adabi (Comparative Literary Theory)  wanda Hugo Meltzl ya samar a shekarar 1877, wanda ra’i ne da ya samu goyan bayan masana irin su H.M Posneet a wani fitaccen aikinsa mai suna “Comparative Literature (1886. Wannan ra’i ana amfani da shi wajen kwatancen adabin al’ummomi, waɗanda  ake  ganin  suna  da  wata  dangantaka  ko  kuma  wasu  kamanni  a  wasu ɓangarori  na  adabi  ko  al’adu  domin  a  tabbatar  da  alaƙarsu. A ƙarshen wannan maƙala an gano cewa akwai bambance-bambance tsakanin nau’in waƙoƙin Gazal na Larabci da na Hausa, a ɓangaren salo kuma maƙalar ta gano cewa yawanci irin salon da ake samu a waƙar Larabci ana samunsa a waƙar Hausa. Har ila  yau, nazarin ya gano irin yadda Hausawa suka ari wani reshe na Gazal  suka samar da nasu a Hausa.

1.0     Shimfiɗa

An yi tunanin yin wannan aikin ne ganin yadda            da yawa Hausawa suke kallon kamar waƙoƙin Gazal ba su da muhalli a Hausa. Wasu kuma suna yi musu kallon fanɗararru ne. Wasu kuma suna kallon bayan waƙoƙin Soyayya a Hausa babu wasu waƙoƙi na Gazal. Shi ya sa aka yi wannan bincike domin a yi kwatancen siga da fasalin waƙar Gazal tsakanin Larabawa da Hausawa, da kuma faɗakar da cewa akwai waƙoƙin Gazal a Hausa masu zaman kansu.

Tushen kalmar ‘Gazal’ asalinta daga Larabci ne. A lugga, ‘Gazal’ na nufin “Tufafin da aka saƙa da auduga”. A ma’ana ta zahiri kuwa ‘Gazal’ na nufin mai da hankali a kan hirar mata da nuna matsananciyar soyayya ko yawan raɗaɗin rabuwa da mace a lokacin da ake tafiya cikin tawaga. A fagen waƙa, kalmar tana nufin, wani nau’in waƙa da ke bayyana tsananin raɗaɗin ciwon rashi ko rabuwa a ɓangare guda, da kuma nuna matsanancin kyawo na masoyi ko masoyiya duk a lokaci guda tare da yaba kyan hali ko ɗabi’a. (Badr Ibn Ali: 2007)

A taƙaice dai ‘Gazal’ wani nau’in waƙa ne da mawaƙi yake bayyana tsananin ƙaunarsa ga abin da yake wa waƙar ta hanyar yabo da siffanta kyawun jiki da na hali da ɗabi’a. Wani lokaci ma har da yanayin mu’amular soyayyarsu.

Siga a wannan aiki shi ne bayyan yadda waƙokin Gazal suke da kuma yadda za a iya gane su da rarrabe su da waɗanda ba na Gazal ba. Sai kuma fasali wanda shi ne yake fayyace irin saƙo ko kuma ƙunshiyar da waƙoƙin Gazal na Larabci da na Hausa suka ƙunsa, domin suna da fasalinsu wanɗanda da zaran an sauka daga gare shi, to an fita maganar waƙoƙin Gazal.

Babbar manufar wannan maƙala ita ce gano sigogi da fasalolin waƙoƙin Gazal a Larabci da na Hausa da kuma fito da kwatancin da ke akwai tsakanin rubutattun waƙoƙin Gazal na Hausawa da na Larabawa.

An bi hanyoyi da dama wajen gudanar da wannan bincike. Hanyoyin da aka bi sun haɗa  da fassara matanoni waƙoƙin Gazal na Larabci zuwa Hausa, da ganawa da masana da kuma yin tambayoyi ga waɗansu mutane da suke da dangantaka da waƙoƙin da aka yi amfani da su.

Sannan an yi amfani da wallafaffun Litattafai da kundayen bincike wajen samun bayanai da suka taimaka wajen gudanar da wannan bincike. Haka kuma, an yi amfani da kafafen sadarwa na zamani domin neman bayanai da suka taimaka wajen kammaluwar wannan aiki.

2.0  Ra’in Bincike

A wannan maƙala an yi amfani da Ra’in Kwatancin Adabi, (Comparative Literary Theory) Wannan Ra’i na Kwatancin Adabi ya fara ɓulla ne a yankin Hungarian a ƙarni na 18 daga wani masani mai suna Hugo Meltzl (1846-1908), wanda ya kasance shi ne edita kuma mamallakin mujallar Journal Acta Comparationis Litterarum Universarum (1877) an sami kuma wani masani mai suna H.M Posnett wanda ke zaune a yankin Irish, wanda shi ne ya fara samar da littafin kwatancin Adabi mai suna‚ Comparative Literature (1886)Wannan tunani na H.M Posnett ya samo asali ne daga shawarar Johann Wolfgang von Goethe ƙwararren masanin adabin duniya.

Wasu daga cikin waɗanda suka biyo bayan waɗannan masana wajen amfani da wannan ra’i akwai Alexander Veselovsky (1838-1906) da Viktor Zhirmunsky (1891-1971). Wannan ra’i ya fara zama da gindinsa a ƙarni na 19 daga rubuce-rubucen Zhirmunsky  Rachel Polonsky, da littafinsa mai suna English Literature and the Russian Aesthetic Renaissance. Wannan ra’i ya wanzu a yankin ƙasar Jamus a a ƙarshen ƙarni na sha tara (19), bayan kammala yaƙin duniyan na biyu ta hannun masana irin su Peter Szondi (1929–1971) wanda ya rubuta littafin kwatanci adabi na waƙoƙi da wasan kwaikwayo mai suna "General and Comparative Literary Studies" har zuwa lokacin da Tübingen, Wuppertal. Ya rubuta littafinsa na kwatancin Adabin da Jamusanci mai suna Der kleine Komparatist (2003).

A ƙasar Hausa, wannan ra’i ya samu tagomashi sosai, inda aka samu ayyuka da suka yi magana kan kwatancin adabi kamar haka: Sankalawa (2005) da aikin sa mai suna “Kwatanta waƙoƙin Aliyu Namagi da Takwarorinsu na Sani Yusuf Ayagi” da aikin Rabi’u (2018) “ Kwatancin Habarcen Nijeriya da Nijar: Tsokaci A Kan Tatsuniya” da aikin Adamu (2019) ”Kawatanci Tsakanin Rubutattun Waƙoƙin Siyasar Jumhuriya Ta Uku Da Na Jumhuriya Ta Huɗu A Nijeriya” da aikin Salihi (2020) na “Kwatanta Littafin Kitsen Rogo Da Jatau Na Kyallu Dangane Da Dabarun Jawo Hankali” da aikin Yahya (2021) mai taken “Kwatanta Jigo Da Zubi Da Tsarin Waƙoƙin Bello Muhammad Aji Mai Karama Da Na Sani Abubakar Hotoro”  da sauransu da dama. 

Wannan ra’i na kwatancin Adabi yana da manufofi da suka haɗa da:

  1. Kwatanta wasu ayyukan adabi da sauran ɓangarori na rayuwar Al’umma
  2. Kwatanta wasu ayyukan adabi masu alaƙa da juna, misali kwatanta wata waƙa da wata makamanciyarta daga mabambanta marubuta
  3. Kwatanta wasu ayyukan adabi da ke sajewa a cikin al’adu domin fito da abubuwan da suke tattare da su na adabi da kuma na al’adun.
  4. Nuna bambancin da ke akwai tsakanin wasu ayyukan adabi masu kama da juna, domin a rarrabe su.
  5. Samar wa ayyukan adabi mazauni na kwatanci tsakanin wasu mabanbanta ɓangarori na duniya da ake ganin suna da alaƙa da juna. Da sauransu

2.1 Dangantakar Manufar Ra’in da Manufar Aikin da Aka Aiwatar

Kamar yadda aka gani daga cikin manufar wannan ra’i akwai kwatanta wasu ayyukan adabi masu alaƙa da juna. Misali kwatanta wata waƙa da wata makamanciyarta daga mabambantan marubuta ko al’umomi mabanbanta.

Ita ma wannan maƙala daga cikin manufar ta akwai kwatanta nau’o’i da salon waƙoƙin Gazal na Hausa da na Larabawa domin gano inda suke da alaƙa da kuma inda suka sha bamban a tsakanin al’umomin guda biyu.

Haka kuma, manufar wannan ra’i ita ce a  samar wa ayyukan adabi mazauni na kwatanci tsakanin wasu mabanbanta ɓangarori na duniya da ake ganin suna da alaƙa da juna. Ita ma wannan maƙala zata duba mazaunin waƙoƙin Gazal ta fuskar nau’o’insu da salonsu tsakanin Larabawa da Hausawa domin ganin irin kamanci da bambanci da suke ɗauke da shi.

Kazalika  manufofin wannan ra’i da na wannan maƙala sun tafi  daidai ta fuskar kwatancin waƙoƙin Gazal na Larabawa da na Hausawa.

3.0 Kamanci da Bambancin Nau’o’in Waƙoƙin Gazal na Larabci da na Hausa

A tsawon zamani, tun daga ƙarni na 7 har zuwa na 13, waƙar Gazal ta Larabawa ta ci gaba da samun bunƙasa, har ya kasance aka karkasa ta zuwa nau’o’i daban-daban, waɗanda suka haɗa da:

1        Al-Ghazal Al-Sarhi (Umarite Ghazal/Ghazal Al-Majun)

2        Al-Ghazal Al-Afif al-Badawi

3        Al-Ghazal Al-‘Udhri

A Hausa ma akwai nau’o’in waƙoƙin Gazal guda kamar haka:

  1. Waƙoƙin Gazal na Soyayya
  2. Waƙoƙin Gazal masu zaman kansu
  3. Waƙoƙin Gazal na cikin sauran waƙoƙi
  4. Gazaliyya

3.1 Al-Ghazal Al- Sarhi ya samo asali ne daga lokacin jahiliyar Larabawa, lokacin da babu wayewa ko kuma bayyanar ilimin addinin Musulunci ga Larabawan. Al’adar Larabawa ta  kiwo ta na daga cikin dalilin samuwar wannan kaso na Gazal. 

A lokacin Larabawa matasa maza da mata duk suna da al’adar yin kiwo. Wannan al’adar ce ta sa aka samu waƙoƙin Gazal suka fara ɓulla daga waɗannan makiyayan na Larabawa.  A wannan kaso akwai ƙananan rassa guda biyu da ake gina waƙar Gazal ɗin da su.  Na farko shi ne ɓangaren waƙar Gazal ta cikin ƙasida wadda ake samun baiti biyar zuwa sha biyar. Irin waɗannan waƙoƙi an same su da yawa kuma suna ɗauke da fasali da ya bambanta su da sauran kason, na farko waɗannan waƙoƙin na Gazal  a waƙa ɗaya za a iya yi wa mace fiye da ɗaya, kuma mafi yawan mabuɗin waƙar ana fara wa ne da ambatar kufai ko sararin fili ko hanya ko wani rafi.  Misali in aka ɗauki waƙoƙin Imru’al Qais  za a ga cewa sun faɗo wannan kason na waƙar Gazal ta gargajiya. A ƙarƙashin wannan kason, akwai ƙananan jigogi kamar haka:

1         Udhari (Qawa Zuci)

2.   Hassi (Bayyana ƙirar jikin mace)

  1. Tamhidi ( wasa mace da zugata ta siffar nuna wasu halayenta na kirki ko akasin haka).  (Muqbil, Badr ibn Ali:2007)

Waɗannan su ne fitattun jigogin waƙoƙin da ke ƙarƙashin wannan jigo na Ghazalul Sarhi. Misalan waɗannan waƙoƙin sun haɗa da waƙoƙin Imru’al Qais irin su;

i.                    Kifa nafki min zikira habibi wa Irfani

ii.                  Liman ɗalalu Afsartu fashajani

iii.                Kifa nafki min zikiri habibi wa munzali

iv.                Ayana Hindu la tankihi bwat’an da sauransu

Misali waƙar Imru’al Qaisa mai suna Liman ɗalalu Afsartu Fashajani ya samar da ita ne bisa irin wannan nau’i na Gazal Al-Sarhi, ga misalin wasu baituka daga cikin waƙar.

لِمَنْ طَلَلٌ أبْصَرتُهُ فَشَجَاني

كخط زبور في عسيب يمانِ

 

دِيَارٌ لهِنْدٍ وَالرَّبَابِ وَفَرْتَني

ليالينا بالنعفِ من بدلان

 

ليالي يدعوني الهوى فأجيبهُ

وأعينُ من أهوى إليّ رواني

 

Fassarar mai bincike

Wannan kufan  gida na wanene? Da ya sa man baƙin ciki,

Gidan ya zama kamar rubutu ne a kan gindigirin[1] dabinon Bayamane[2].

 

Waɗannan gidaje ne na Hindu da Rabab da Fartana,

Ka tuna dararen mu a kan wani tudu a Badalani.

 

Ka tuna dararenmu a lokaccin da soyayya ke fisga ta, sai na amsa ma ta,

Idanun waɗanda na ke so ɗin suna duba ya zuwa gareni.

 

A Hausa ba a samu wannan nau’i kai tsaye ba saboda bambancin al’adu da ke akwai tsakanin al’umomin guda biyu, musamman abin da ya shafi al’adar kiwo wadda a nan ne aka fi samun waɗannan waƙoƙin sai dai an samu wani nau’in waƙar Gazal mai ɗan kamanceceniya da wannan nau’i, wato nau’i na na uku daga cikin nau’o’in waƙoƙin Gazal na Hausa wanda ake samun waƙoƙin Gazal na cikin sauran waƙoƙi, inda mawaƙi zai yi baituka biyar zuwa goma ga masoyiyarsa ko masoyinsa a farkon waƙar sannan sai mawaƙi ya cigaba da waƙarsa. A mafi akasari irin wannan kason an fi samunsa ga waƙoƙin da aka shirya na zambo ko habaici ga wani. Sannan a waƙoƙin siyasa ma ana samun irin wannan kaso na waƙar Gazal. misaln irin waɗannan waƙoƙin sun haɗa da;

i.                    Wasiƙar So ta M.B Umar

ii.                  Tsarabar Masoyi ta Bello Sa’id

iii.                Mun shaƙu mun gama Zautuwa ta Binyaminu Zakariyya Hamisu da sauransu.

Irin wannan misalin shi ne waƙar Binyaminu Zakari mai suna mun Shaƙu mun gama Zautuwa ga kadan daga cikin waƙar.

Har Muntaha mun je ga Dal,

Maleji ma na  ƙarar  tuni.

 

Ni nata  ne  ita  tawa  ce,

Ruhinmu dai ne ba hani.

 

Don ni a kai ta ya Adamu,

Gun Hauwa, ba ma yin kini.

 

Hankalina ya tashi ƙoli ma,

Zan yi rashinta a zamani.

 

Ko da ganinta ta fi ni ma,

Ga shi har za ta cutar da ni.

 

Zuciyata sai tafasa take ta yi,

Za mu rabu da mai zamani.

 

Wayyo Allah ni ya za ni yi?

Wata kil sai dai a sa likkafani.

Bambancin da ke akwai a Hausa ba samun waƙar Gazal da ake yi wa fiye da mace ɗaya waƙa, kamar yadda ake samu a nau’in waƙoƙin Gazal na  Al-Sarhi, wanda shi a Hausa na fi mayar da hanakali ne ga mace ɗaya.

3.2 Al-Ghazalul Afif al-Badawi,  shi wannan ya yaɗu ne a ƙauyen Hijaz a wata ƙabila da ake kira Bani Uzratu da Kuza’a a tsakanin matasan da suka kasa yin hijira da tafiya jihadi, amma waƙoƙinsu na Gazal  ba su yin ƙarya a ciki, kuma ba su zuwa da kalmomin nuna batsa ƙarara, wanda bai kamata a siffanta mace Musulma da su ba. Mafi yawan jigogin waƙoƙin wannan kaso ba su wuce:

·         Yabo

·         Gwarzantawa, da sauransu.

Misalan waƙoƙin sun haɗa da irin   waƙoƙin Umar Bin Abi Rabi’ata waɗanda suka haɗa da:

i.                    Amin ali nu’umi anta gadi fa mubakur

ii.                  Hiya shamsu tasri da sauransu.

Misalin irin wannan waƙa dake wannan nau’i akwai waƙar  Umar Bin Abi Rabi’ata mai suna Hiya shamsu tasri, ga kaɗan dagab cikin baitocin waƙar;

أَمِن آلِ زَينَبَ جَدَّ البُكورُ

نَعَم فَلِأَيِّ هَواها تَصيرُ

 

أَلِلغَورِ أَم أَنجَدَت دارُها

وَكانَت قَديماً بِعَهدي تَغورُ

 

هِيَ الشَمسُ تَسري عَلى بَغلَةٍ

وَما خِلتُ شَمساً بِلَيلٍ تَسيرُ

 

وَما أَنسَ لا أَنسَ مِن قَولِها

غَداةَ مِنىً إِذ أُجِدَّ المَسيرُ

 

أَلَم تَرَ أَنَّكَ مُستَشرَفٌ

وَأَنَّ عَدُوَّكَ حَولي كَثيرُ

 

فَإِن جِئتَ فَأتِ عَلى بَغلَةٍ

فَلَيسَ يُؤاتي الخَفاءَ البَعير

 

Fassarar mai bincike

Shin daga iyalan gidan Zainab ake yin sammako?

Eh! To wace irin soyayya ce take zama irin haka?

 

Shin gidanta yana kwari ne ko a tudu?

Har ta kasance tuntuni tana gafala daga Alƙawari na.

 

Ita rana ce tana tafiya a cikin dare a saman alfadari,

Ban taɓa tsamanin cewa rana tana tafiyar dare ba.

Ban natsu da maganarta ba, kuma bana natsuwa da maganarta,

A safiyar Mina lokacin da nike ƙoƙarin tafiya.

 

Tace shin baka gani mutane sun sa maka ido,

Kuma maƙiyanka suna da yawa a gefena.

 

To in za ka zo ka zo bisa alfadara,

Domin in ka zo kan raƙumi ba zai iya ɓoyuwa gare su ba.

 

Akwai kwatancin Wannan nau’i a waƙoƙin Gazal na Hausa wanda aka ba shi suna Nau’i “Waƙoƙin Gazal ma su zaman kansu”, dukkanin waɗannan nau’o’i guda biyu ba a saka ƙarya a cikin su. Shi wannan nau’i ya samo asali ne daga malaman sufaye da suke shirya waƙar Gazal da sunan mace, amma a matsayin nuna kusanci da kuma kaɗaita Allah tare da nuna irin ƙudirarsa, sai dai su waɗannan waƙoƙin duk da sunan an yi mace su ne. Wannna nau’i kacokam an ɗauki nau’in Al-ghazalul Afif al-Badawi ne wanda kai tsaye ke nuna rabuwa ne ya ke nunawa tsakanin mace da namiji. Misali waƙoƙin Ibrahim Sodang da suka haɗa da:

i.                    Ƙarshen Tafarkin hankalina

ii.                  Ku kirani Majanuni

iii.                Zuciyata ko kin mace

iv.                Idan ni bana ganinki...

v.                   Muna son juna amma to ba zamu faɗi ba da sauransu.

Misalin wata waƙa a wannan nau’i ita ce waƙar Ibrahim Sodangi mai suna “Ku kirani Majnuni” a wasu baituka ya na cewa;

Ni da Allah muna son ki,

Shi Ya riga yi son ki gaban zamani.

 

Ni wallahi ina kewar ki,

Idan ƙarya nake Allahu Ka ƙone ni.

 

Ina hawaye cikin tausanki,

In ba haka ba Rabbu Ya azabce ni.

 

Wani so ne na ban mamaki,

Ya zarcewa zuhuri wane ya buɗuni.

Bambancin da ke akwai a wannan shi ne ita waƙar Gazal mai zaman kanta ta Hausa galibi bata cika wuce baiti sha biyar ba, saɓanin nau’in Al-ghazalul Afif al-Badawi wanda ana iya samun baituka fiye da hamsin, kuma a nau’in na Gazal Al-Afif ana musayar zance ne tsakanin samari da ‘yanmatansu, wanda a Gazal  mai zaman kanta ba haka abin ya ke ba.

3.3 Al- Ghazal Al’udhari: wadda ke wakiltar soyayya ta gaskiya ita ce da Larabci ake kira  'Udhrit’. Mawaƙa ne masu taƙawa da masu tsoron Allah ne suke shirya waƙoƙin wannan nau’in. Yawancin lokaci mawaƙan da ke shirya wannan fasalin su ne waɗanda ba su yi nasara ba a cikin harkokinsu na soyayya, saboda  yanayin zamantakewa da al'ada ko kuma bambancin addini ko rashin hallacin auren wadda yake so ɗin a ɓangaren addininsa.

Wannan rashin da suka yi da kuma abin da suke ji shi ne suke bayyanawa a cikin waɗannan waƙoƙi masu wannan fasali. Sannan kuma baki ɗaya irin waɗannan waƙoƙi babu batsa a cikinsu ko kuma fayyace ni’ima ko sigar mace, tsananin kewa ce kawai a cikinsu.

Wannan nau’i ya samo sunansa ne daga ƙabilar Udhrah, wadda mutanenta ne suka samar da wannan aji sakamakon shahara da suka yi da soyayyar gaskiya wadda ba a cika rabuwa ba sai dai mutuwa. Daga cikin mawaƙan wannan ƙabilar da suka bayyanar da wannan fasali a sarari akwai mawaƙi Jamil b. 'Abdallah b. Ma’mar, wanda aka fi sani da Jamil Buthaynah (d.82\701), wanda ake ganin shi ne jagoran assasa  wannan nau'in. Amma duk da haka, akwai mawaƙa ‘udhri’ daga wasu ƙabilu, kamar Majnun Layla, wanda ɗan ƙabilar Banu  ‘Amir ne. Wannan nau’in na  Udhri ya kasance an yi amfani da shi sosai  a dukkan makarantar mawaƙan Hamadar Larabawa ta tsakiya.

'Soyayyar Udhri soyayya ce mai mutuƙar tsafta  wacce take kaiwa ga mutuwa.  A Udhri mutum na son mace ɗaya ne kawai, ya sadaukar da rayuwarsa da waƙoƙinsa gare ta; sai da kyar ake haɗa baitukan da wasu nau'i, kamar yabo (madh}. An siffanta masoyiya a cikin  udhri a matsayin mace ta gari, kuma mai son mawaƙinta a matsayin shahidin soyayya. Wannan nau’in na Gazal  an yi amfani da shi lokacin da Manzon Allah (SAW) ya yi hijra daga Makka zuwa Madina sai aka samu wasu daga cikin mawaƙan Larabawa suka riƙa amfani da wannan nau’i wajen waƙe ‘yan matansu da suka yi hijira, wanda a lokacin wannan nau’i ya yi tashe sosai. Misalan waƙoƙin wannan kaso sun haɗa da waƙoƙin Antarah Bin Shadda da na Qais Ibn Muwallah. Daga cikin waƙoƙin akwai:

i.                    A ya Shibaha Laila

ii.                  Hal gadarar Shu’ara’i min mutaraddami

iii.                Khalilayya la wallahi la’amliku lazi da sauransu.

Misalin irin waƙoƙin wannan nau’i sun haɗa da waƙar  waƙar Qais bin Mulawwa ta ‘A ya Shibaha Laila’ wadda ita a cikinta mawaƙin ya bayyana irin yadda aka yi tafiya da shi zuwa aikin hajji domin ya roƙo Allah SWT ya cire masa sonta, amma sai ya ɓuge da ba ta labarin yadda tafiyar ta zama ƙunci a wajensa saboda rashin ta kusa da shi, ga wasu daga cikin baitocin waƙar;

أَيا شِبهَ لَيلى لا تُراعي فَإِنَّني

لَكِ اليَومَ مِن بَينِ الوُحوشِ صَديقُ

 

وَيا شِبهَ لَيلى أَقصِرِ الخِطوَ إِنَّني

بِقُربِكِ إِن ساعَفتِني لَخَليقُ

 

وَيا شِبهَ لَيلى رُدَّ قَلبي فَإِنَّهُ

لَهُ خَفَقانٌ دائِمٌ وَبُروقُ

 

وَيا شِبهَها أَذكَرتَ مَن لَيسَ ناسِياً 

وَأَشعَلتَ نيراناً لَهُنَّ حَريقُ

 

وَيا شِبهَ لَيلى لَو تَلَبَّثتَ ساعَةً 

لَعَلَّ فُؤادي مِن جَواهُ يُفيقُ

 

Fassarar mai bincike

Mene ne abin da yai kama da Laila? Duk duniya babu kamarta,

Ni a yau ko  a tsakanin namun daji ni zan kuɓutar da ke.

 

Ya kai abin da yai kama da Laila ka taƙaita takunka ina kusa da kai,

Idan ka matso kusa da ni zan aboceka da kyawawar ɗabi’a.

 

Duk wani abu da ya dace da kama da Laila zan maida hankalina gare shi,

Zan zama liƙe  da shi kowane lokaci kuma zan haskaka shi.

 

Ya kai mai kama da Lailai kai abu ne da  ake tunawa kuma ba za a manta kai ba,

Zan tsayar da haske wanda zai haskaka ko’ina gareka.

 

Ya kai abin da kai kama da Laila, da ace za a cuɗanyaku a waje guda,

Ita zuciyata za ta iya karkata ga wanda yake na Laila.

 

A Hausa an samu kwatancin irin wannan nau’in da aka ba sunan  ‘waƙoƙin Gazal na cikin waƙoƙin soyayya’, wanda waƙoƙi ne da ake samu cikin waƙoƙin soyayya inda ake tsara waƙoƙi masu ɗauke da sigogin waƙoƙin Gazal, a Hausa irin waɗannan waƙoƙin ana masu kallon waƙoƙin soyayya kai tsaye sai dai sun bambanta da waƙoƙin soyayya domin su za ka same su da fasali da siga na waƙar Gazal misali, zaka same su ƙwar biyu ne aka tsara su kuma ba sa wuce baituka biyar zuwa goma a sha biyar, sannan suna ɗauke da fasalin nuna kewa ko raɗaɗin rasa masoyiyar. Wannan kaso ya na da kamanci da nau’in Gazal na Larabci wato Gazal Al’udhari, domin shi ma a wannan na Hausa yana tafiya ne bisa ƙananan jigogin da suka haɗa da, Kewa da Ƙawa Zuci da kuma zuga mace amma kuma ta fuskar nuna raɗaɗin rasa ta ko kuma yin nisa da ita. Misalan iin waɗannan waƙoƙin un haɗa da wasu da aka samu a cikin littafin Dausayin Soyayya. Daga cikin su akwai;

i.                    Tsarabar Masoyi ta Bello Sa’id

ii.                  Bege ta B.A Salim da sauransu

A waƙar Tsarabar Masoyi ta Bello Sa’id a wasu baituka ga abin da yace;

Ya masu ribbantar zukatan ‘yan Adam,

Na zo ina kamun ƙafa wajjanki,

 

Kin ribace min tawa duk na barka ce,

Na kawo kokena ina roƙon ki,

 

Na faɗa kogi kamfacece na nutse,

Ba wanda ke tsamo ni in baicinki,

 

Wallahi kin harban da kibiyan nan ta so,

Ba magani na tabbata sai naki.

 

Ke ce farar tauraruwa mai haskake,

Sassa da annuri, taho Gamzaki.

Kusan waɗannan nau’i guda biyau a iya cewa suna tafiya ne bisa abubuwa iri ɗaya, ke nan Hausawa ne suka ari wannan kaso na Gazal Al’Udhari suka samar da kasaon nasu Gazal ɗin da suka tsarma su a cikin waƙoƙin Soyayya.

Waɗannan nau’uka guda uku na Gazal a Larabci da kuma Hausa su ne suka taru suka samar da ire-iren waƙoƙin Gazal da ake amfani da su, kuma duk wata waƙar gazal wajibi ne ta faɗo cikin wannan kaso.

4.0 Bambancin Nau’o’in Waƙoƙin Gazal na Larabci da na Hausa

A nan kuma maƙalar ta fito da bambancin da aka samu ne a tsakanin nau’in waƙoƙin Gazal Larabci da Hausa, a Larabci an samu Nau’i uku yayin da a Hausa aka samu Huɗu duk da waƙoƙin Gazal na Larabci da na Hausa suna da matuƙar kamanci da juna, amma hakan bai hana aka samu wasu abubuwa ba da suka bambanta su, wanda ake samun su a Hausa ba bu su a Larabci.

4.1 Gazaliyya (waƙar Gazal ta Hausa)

 A Hausa akwai nau’in waƙar Gazal wanda Yahya (2014) ya kira da suna Gazaliya, wanda ya bayyana cewa ita ce waƙar da aka tsara gaba ɗayanta tana bayyana tsananin so ga masoyi, wani lokaci har da bayani kan raɗaɗin rabuwa ko yin nisa da masoyi. Wannan waƙar namiji ne ke shirya wa namiji dan’uwansa ita ko mace ta shiyra mace ‘yaruwarta. wanda ya kasance uban gida ko malam ko shugaba ko ma aboki, a bayyana irin kyautatawa da karamcin da aka samu a lokacin da ake rayuwa tare da wannan da ya yi wa waƙar, wanda a halin da ake waƙar ba sa tare ko dai an masa nisa ko kuma an rasu. Irin wannan fasalin babu shi a waƙoƙin Gazal na Larabci, sai da a Hausa. Misali waƙar Gudale ta yabon Alhaji Giɗaɗo Ibrahim Yabo, wadda Haliru Wurno ya rubuta ga wasu daga cikin baitocin waƙar:

Na yi kiran Allah shi ishe ni,

Al’amarin ga da yad dame ni.

Na yi salatu ga Hairil halƙi,

Ahmada ya zo man da Mubini.

Na yi salatu dubu da salama,

Alaihi wa alihi ahlid dini.

Na ga rashin abkin kayana,

Don haka tsoro ya ribce ni.

Na ga dare da subahin haske,

Ga kuma rana ta dushe ni.

Na yi farat na sheƙa inwa,

Na ga kwamarci ya kore ni.

Na ga ruwan gulbi na zallo,

Na zo na shiga sun toye ni.

Na tuma na koma can ganga,

Ba wani mai jinya ya fake ni.

In za a lura za a ga cewa tun a baitin farko wannan waƙar ta saɓa da fasalin waƙokin Gazal na Larabawa inda aka fara buɗe waƙar da ambaton Allah, wanda ba a samun haka a waƙoƙin Gazal na Larabawa.

5.0 Kamanceceniyar Waƙoƙin Gazal na Larabci da na Hausa ta Fuskar Salo

A nan an yi ƙoƙarin fayyace irin salon da mawaƙan gazal na Larabci da na Hausa suke amfani da su domin isar da saƙonsu ga masu karatu ko sauraren waƙoƙin. Kamar dai yadda aka riga aka sani, Salo hanya ce da ake gane dabaru  ko hikimar da marubuci ya bi domin isar da saƙo. Kamar yadda Dangambo (2007) ya bayyana, “salo wani yanayi ne na zaɓen yadda mai rubutu zai yi amfani da kalmomi ko lafazi domin ya isar da zance wanda kan bambanta shi da wani marubuci wanda ba shi ba”. Salo yakan ƙara armashi a rubutu saboda akan bi hanyoyi na musamman kamar amfani da karin magana ko kwatanci ko sarƙa kalmomin wani harshe wanda ba harshen da ake amfani da shi wurin rubutun ba da sauransu. Salo yana ƙara bayyanar da hikimar marubuci wajen bin hanyoyin ƙara wa rubutunsa daraja.

5.1  Salon Waƙoƙin Gazal na gabaɗaya

Ga nazarin waƙoƙin gazal na Larabawa da na Hausa, kai tsaye za a ce salon rubutunsu mai armashi ne, saboda yana da sauƙin ganewa, ba salon kwan- gaba kwan- baya ba, domin ana shirya zaren tunanin waƙoƙin daki–daki  yadda mai karatu zai fahimci saƙon nan da nan. Ban da sauƙin gane waƙoƙin, akwai kuma armashi a salonsu na gaba ɗaya, domin ana amfani da salon ƙawata magana wajen rubutu.

5.2 Amfani da Sauran Hanyoyin Salo

Wajen kawo salon gaba ɗaya, an ambaci cewa waƙoƙin gazal ana amfani da salo mai armashi, wanda ke jawo hankalin mutane ga saƙon da yake son isarwa.  A wannan ɓangare an fitar da mafi yawan waɗannan hanyoyi daki–daki gwargwadon abin da zai sa a gane manufa, saboda fitar da hanyoyin da mawaƙan gazal ke amfani da su gaba ɗaya zai yi matuƙar wuya. Don haka abin da za a sa gaba a nan shi ne, kawo gwargwadon bayanai da misalai game da hanyoyin dabarun salo daban – dabam waɗanda aka yi amfani da su a waƙoƙin.

5.2.1 Salon Kwatantawa

 A salon kwatantawa kamar yadda kalmar kwatantawa ta bayyana, ana kwatanta ko auna abubuwa biyu ko fiye, domin a fitar ko a gane dangantakar da ke tsakaninsu. Kwatantawa ta kasu kashi uku akwai kamantawa da siffantawa da kuma jinsintarwa.

5.2.1.1 Kamantawa

 Wannan hanya tana kamanta abu biyu ko fiye ta hanyar amfani da wasu kalmomin awo irin su ‘kamar’ ko ‘tamkar’ ko ‘awa’ ko ‘ya’ ko ‘daidai da’ ko ‘wane’ ko ‘ ya zarce’ ko ‘ɗara’ ko ‘wuce’  ko ‘fi’ ko ‘gota’ ko ‘tsere’ ko ‘gaza’ ko ‘ƙasa’ da sauransu. Dabarar kamantawa ta kasu kashi uku, kamancen daidaito da kamance fifiko da kamancen kasawa.

5.2.1.1.Kamancen Daidaito

A nan mawaƙi zai kamanta wasu abubuwa biyu ko fiye, yana nuna ɗayan daidai yake da wani, ko waɗansu abubuwa daidai suke da waɗansu. Wannan kamanci na iya zama don aibantarwa ko don rage  darajar abin da ake yin kwatanci a kansa. Misali na wanan kwatance ya fito a waƙar Antarah Bin Shaddad mai suna, Hal gadarar shu’ara’u mi mutaradammi, in da yake cewa:

وَكَأَنَّمَا نَظَرَتْ بِعَيْنَيْ شَادِنٍ

رَشَأٍ مِنَ الْغِزْلانِ لَيْسَ بِتَوْأَمِ

 

Fassarar mai bincike

Idonta in ta kalleka kamar tana kallonka ne da idanin ɗan Barewa,

Ƙaƙƙarfa, wanda ba tagwaye ba shi kaɗai aka haifa.

 

A waɗannan baitocin ana daidaita sifa ta masoyiyarsa da wasu sifofi mafi kyau da shahara, an daidaita siffar idonta da idanun ɗan barewar da aka haifa shi kaɗai, wanda idanuwansa sun kasance dara-dara ne masu matuƙar sheƙi da haske.

A cikin waƙar Binyaminu Zakari Hamisu mai suna, ‘Nan yini nan kwana..’  a wasu baituka yana cewa;

Ga kwalliyarta kamar Ɗawisu in ta taho,

Tamkar Agwagwa a ƙasaita saman Ɓauna.

*****

 

A waɗannan baituka da ke sama, za a ga cewa a baiti na farko mawaƙin ya daidaita kwalliyar masoyayarsa da kyau irin na Ɗawisu. Ko shakka babu irin wannan kwatancen ana samun sa sosai a waƙoƙin gazal na larabawa da na Hausa.

5.2.1.2  Kamancen Fifiko

A wannan salon ana kawo kalmomin mizani da ake kwatanta abubuwa daidai ko kwatanta wani abu da wanda ya fi shi ko da wanda ya kasa shi. Don haka a wannan kamance na fifiko akwai kalmomin da ake amfani da su wajen nuna fifikon wani abu ko wasu abubuwa a kan wani ko wasu. Kalmomin mizanin sun hada da ‘zarce’ ko ‘wuce’ ko ‘ɗara’ ko ‘fi’ ko ‘gota’ da sauransu.

A waƙoƙin gazal wannan salo yana bayyana sosai sakamakon cewa mafi yawan waƙoƙin akwai bayanin fifita masoyiya shi ya sa ake samun wannan salon sosai a waƙoƙin na gazal a Larabci da Hausa. Misalai a waƙar Waƙar Imri’al Qais mai suna “Liman ɗalalun afsartuhu fa shajani”  ga abinda ya ce a wani baiti;

لهَا مِزْهَرٌ يَعْلُو الخَمِيسَ بِصَوْتهِ

أجَشُّ إذَا مَا حَرّكَتْهُ اليَدَانِ

 

Fassara mai bincike

Tana da Molo, yana gagarar hargowa ta runduna mai sassa biyar,

in aka kaɗa shi mai yawan ƙara ne idan hannu ya ƙaɗa shi.

 

A wannan baiti Imru’al Qais ya yi amfani da salon kamance na fifiko ne inda ya daga darajar wannan malo na mawaƙiyarsa fiye da hargowar tarin runduna wadda ke da sassa biyar. Ya nuna cewa duk irin hargowar mutanen da ke cikin wannan runduna, to amom molon mawaƙiyarsa ya fi shi tashi

A Hausa ma mawaƙan gazal sun yi amfani da irin wannan salon a cikin waƙokinsu misali waƙar Ibrahim Sodangi mai suna ‘Abar bauta Majanuni’ ga abinda ya ce a wasu baituka;

Ai ko Ka'abar Rahmani,

Inuwar zatinki ta fi sa shauƙi ya shige ni.

 

Haka taƙarar Ƙur'ani,

Karanta rubutunki ya fi ratsa min uznaini.

 

A waɗannan baituka Ibrahim ya yi amfani da salon kamance na fifiko domin fito da wasu muhimman abubuwa da yake so a cikin waƙarsa, in da tsananin jazaba ta kwasheshi har yake nuna cewa shi a wajensa inwar zatain masoyiyarsa ta fita shauƙin son ya ziyarta  Ka’aba.

 

 

5.2.2  Siffantawa

Siffantawa kwatanci ne na kai tsaye tsakanin wani abu ko wasu, domin a nan  za a ɗau wani abu a ce shi ne wani kai tsaye ba tare da an yi amfani da kalmomin mizani da ake amfani da su a wajen kamantawa ba. Akwai salon siffantawa da dama a waƙoƙin gazal, sai dai za a kawo misalai ne kawai domin tabbatar da wannan magana. Misali a waƙar Umar bin Abi Rabi’a mai suna ‘Layyata Hindu, a wasu baituka yana cewa;

 

أَكَما يَنعَتُني تُبصِرنَني

عَمرَكُنَّ اللَهَ أَم لا يَقتَصِد

                                                                   

                                                                    فَتَضاحَكنَ وَقَد قُلنَ لَها

حَسَنٌ في كُلِّ عَينٍ مَن تَوَد

 

Fassarar mai bincike

“Shin kamar yadda yake siffanta ni wurin kyau,

 ko yana wuce gona da iri?” Allah ya tsawaita rayuwarku.

 

Sai suka yi dariya suka ce mata,

“Ai so makaho ne”.

A wadannan baituka mawaƙin ya yi amfani da salon sifantawa ne kai tsaye inda ya ambaci wuce gona da iri a matsayin kwatancen kyau mafi ƙololuwa, sai kuma aka ƙara bayyana so a matsayin makaho wato wanda bai gani, a taƙaice an siffanata so da makaho, kennan duk yadda shi Umar ke siffantata ma ta wuce haka a wajensa, saboda duk abinda za a faɗi masa game da ita ba zai saurara ba idonsa ya riga da ya rufe kan sonta da kuma bayyaa kyawunta a idon mutane wanda har hakan ya sanya ta a kokwanto.

A waƙoƙin gazal na Hausa ma an samu irin wannan salon na siffantawa misali a waƙar Bello Sa’id mai suna, ‘Tsarabar Masoyi’ a wani baiti ga abinda yace;

Na shekara har uku cur ba hankali,

Duk na ɗimauce na kaɗe dominki.

 

Kullum ina fama da ƙunar zuciya,

Ko na yi barci sai na gano kurwarki.

 

Ko da cikin sallar farilla ne ni ke,

Sai zuciyata ta raya wajjanki. 

A waɗannan baitukan Bello Sa’id ya yi amfani da salon siffantawa inda ya bayyana irin halin ɗimauta da kaɗuwa da ya samu kansa saboda masoyiyarsa, har ya nuna cewa sai da ya yi shekara cur ba hankali a tattare da shi, kullam zuciyarsa cikin ƙunci take saboda rashin masoyiyarsa kusa da shi, shi yasa ma duk baccin da zai yi sai ya fara ganinta a cikin baccin. Kai ƙarshe ma ya bayyan cewa shi saboda rashinta ibada ma na neman susuce masa domin ko sallah yake to zuciyarsa na wajenta. Ko shakka babu wannan salon yana taka rawa sosai a waƙoƙin gazal musamman da ya kasance dama waƙoƙin ne da suke cike da siffantawa da kamance da kuma kwatanci na masoya ta fuskoki da dama.

Waɗannan salalai su ne misalan wasu daga cikin salalan da ake samu a cikin waƙoƙin gazal in an lura za a ga cewa dukkaninsu salalaine na kwatance da kuma siffantawa sai kamantawa, wanda kuma dama waƙoƙin gazal a nan suka fuskanta. Za a iya samun sauran wasu salon, a waƙoƙin gazal na Larabawa da Hausawa, sai dai waɗannan sun fi shahara.

6.0 Sakamakon Bincike

Babu ko shakka duk wani bincike da aka gudanar to daga ƙarshe akwai buƙatar a ga wane irin sakamako wannan bincike ya samar, musamman ga al’ummar da aka yi binciken domin su.

Maƙalar ta gano cewa tsakanin nau’o’in waƙoƙin Gazal na Larabawa da na Hausa akwai kamanci sosai tsakaninsu musamman yadda mawaƙan ke gina waƙoƙin.

Maƙalar ta gano cewa akwai bambanci tsakanin nau’o’in  rubutattun waƙoƙin Gazal na Larabci da na Hausa ta fuskar adadin ɗango da kuma waƙar Gazal da ake shiryawa domin yiwa shugaba ko uban gida, wanda a Hausa ne ake samun wannan fasali, sannan a Hausa ne ake samun adadin ɗango ya wuce biyu.

Ta fuskar Salo maƙalar ta gano cewa kusan duk wasu salalai da ake amfani da su a Larabci to a Hausa ma dai sune, domin tushen waƙoƙin Gazal na Hausa dagha Larabcin aka samo su.

Maƙalar ta gano cewa Al’ummar Hausawa da Larabawa tamkar Ɗanjuma ne da Ɗanjummai kan abin da ya shafi ayyukan adabi na waƙa, domin kwatanta waƙoƙin Gazal na Larabawa da na Hausa ya taimaka ƙwarai wajen sanin yanayin yadda Larabawa ke gudanar da rayuwarsu da kuma abubuwan da suke da alaƙa tsakanin Larabawan da Hausawa.

Maƙalar ta gano cewa babu wani nau’in waƙa da ya kai na Gazal sanya hikima da kuma nuna gwanitar harshe da naƙaltarsa, kasantuwar mafi yawan waƙoƙin Gazal sai an yi fashin baƙinsu sannan ake fahimtar su, saboda yadda ake sanya salo da adon harshe da fasaha da naƙaltar harshe a cikinsu.

7.0 Naɗewa

Wannan maƙala ta bibiyi Nau’oi da salon rubutattun waƙoƙin Gazal tsakanin Larabci da Hausa. An yi bayani ne  inda aka duba nau’o’in waƙokin da suka yi kamanci  aka yi fashin baƙinsu da misalai, sannan aka dubi bambancin da ke tsakanin nau’o’in rubutattun waƙoƙin Gazal na Larabci da na Hausa tare da kawo misalai a tsakaninsu. An kuma yi nazarin ire-iren salon da masu rubuta waƙar ke amfani da shi domin yin kwatanci tsakanin na Larabwa da na Hausa. Sai kuma aka kawo sakamon binciken, ma’ana abinda aka gano bayan da aka kammala binciken.

 

Manazarta

Abdullahi, Y. (2016). Al-Muzanatu baina ƙasidatal ash-shai’raini, amirul-mumina

Muhammu Bello wa Muhammadul-Bukhari firasat’ ammihima Al-Ustazu Abdullahi Bn Fodiyo. A Dissertation Submitted to the Posgraduate School Usman Danfodiyo Unversity.

Ainu, H.A. (2005). Rubutattun waƙƙoƙin addu’a na Hausa: Nazarin jigonsu da salailansu.

[Kundin Digiri na Uku] Sashen Harsunan Nijeriya, Jami’a Usmanu Danfodiyo.

Al-Harthi, M.J. (2010). I have never touched her: The body in al-ghazal al-‘udhri.

[Unpulished PhD, Thesis] University of Edingburgh College of Humanities and Social Science School of Litereatures, Languages and Cultures Department of Islamic and Middle Estern Studies.

Al-askandariya da Wasu (BS) Taikhul Adab. Naqada Printing and Publishing  

Company,.

Al-alamiyya, J.D (2001).  Al-adab Wannusu Wal Balaga wan Nakad. Jami’atul Da’awatul

Islamiyya.

Adamu, M. (2019). Kawatanci tsakanin rubutattun waƙoƙin siyasar jumhuriya ta uku da na jumhuriya ta huɗu a Nijeriya [Kundin Digiri na Uku] Jami’ar Umaru Musa Yar’adua.

Babangida, A.Y (2011). A comparative literary study of the hamziyya panegyric poetry of 

the prophet ( p.b.u.h) by Ahmad Shawqiy and Aliyu Jarim. [Unplished Masters Degree] Department of Arabic. Bayero University.

Baffa, S.A (2021). Sabon zubin waƙoƙin Hausa a ƙarni na ashirin da ɗaya. [Unpublished

Ph.D Dissertation] Usman Danfodiyo Unversity.

Funtua, A.I (2002). Waƙoƙin Siyasa na Hausa a Jamhuriya ta Uku: Jigoginsu da Sigoginsu”.

Takardar da aka gabatar a taron ƙara wa Juna Ilimi, Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya, Jami’ar Bayero.

Ibrahim, A. (2004). Nazarin jawo hankali cikin rubutattun waƙoƙin soyayya na

Abdullahi Bayaro Yahaya. [Kundin Digiri na Ɗaya] Jami’ar Usman Ɗanfodiyo.

Ibn Khutaiba (BS). Kitab Al-shi’r Wa-al-shua’ara. Dar-Alma’arifa.

Isah, H (2021). Salon tsakuren nassi cikin waƙoƙin Umaru Nassarawa Wazirin Gwandu.

[Unpublished Dissertation of  Masters of Arts] Department of Nigerian Languages. Usman Danfodio University.

Jalajel, D (2007). “A short history of Ghazal” Ghazalpage

Jangebe, M.M (1991). Nazari kan rubutattun waƙoƙin yabo na garin Sakkwato [Kundin

Digiri Na Biyu] Sashen Harsunan Nijeriya, Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo.

Nuhu, A  (2012). Sauye-sauye a tsarin waƙoƙin zamani: Nazari a kan waƙoƙin finafinan

Hausa [Kundin Digiri Na Biyu] Sashen Harsunan Nijeriya Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo.

Ojolowo, S.A (2013). A comparative study of erotic poetry of Imru’ul Qais and Umar bn abi

Rabi’ah. [Unpublished  Dissertation Masters Degree] Submitted to the Department of Arabic Bayero University.

Ramlatu, M.A. (2015). Fannu al-rasa’ilada al-sha’ir al-shaikh Usmanu Naliman: Dirasah

adabiyyah tahaliliyyah [Unpublished  Dissertation of  Masters of Arts]  Department of Arabic. Usman Danfodio University.

Sa’id, B (1982). Dausayin Soyayya. Northen Nigerian Publishing Company.

Satatima, I.G (2009). Waƙoƙin baka na ɗarsashin zuciya: Yanaye-yanayensu da sigoginsu.

[Kundin Digiri na Uku] Sashen Nazarin Harsunan Nijeriya, Kano: Jami’ar Bayero.

Yahaya, A.B (2014). Gudale WaƘar Soyayya: Misalin Ghazal a cikin rubutattun waƙoƙin

Hausa. Cikin Feschcript na Farfesa Abdulqadir Ɗangambo.

Zaiti. A (2007). Tarikhul Adbil Arabi. Dar-al-ma’arifa.


[1] Fallen ganyan dabino da ake yin rubutu a cikinsa domin adana shi

[2] Mutumin ƙasar Yaman

Waƙoƙin Gazal

Post a Comment

0 Comments