Wannan panel zai tattauna rawar rubutun Hausa a ƙasashen waje da tasirinsa a kafafen yada labarai da cibiyoyin al’adu, da gudummawar Hausawa mazauna kasashen Afirka wajen raya harshe da adabi.
RUBUTUN HAUSA A
WAJEN ƘASAR HAUSA
1. Muhammad Rabiu (Abu Hidaya) ɗan jarida ne kuma gogaggen
masani a kafafen yaɗa
labarai, wanda ya shahara wajen rubutun Hausa na zamani, wallafe-wallafen yanar
gizo, da tattauna al’amuran da suka shafi rayuwar yau da kullum ta al’umma. Shi
ne Shugaban Kamfanin Muryar Afrika Media Link LTD, kamfani da ke aiki a fagen
yada labarai da taskance tarihi da tallata rubuce-rubucen Hausa ta kafafen
sadarwa na zamani. Kasancewarsa a cikin ƙasar Hausa, tare da gogewarsa a aikin
jarida da kafofin sada zumunta, ya ba shi damar fahimtar halin da rubutun Hausa
ke ciki a yau daga marubuta, masu karatu, zuwa hanyoyin yaɗa labari. A takaice, Abu
Hidaya na daga cikin masu tasiri a rubutun Hausa na zamani, kuma ana yawan
dogaro da shi wajen jagorantar tattaunawa (panel moderation) da sharhi kan
makomar adabin Hausa a cikin gida da waje.
2. ENGR. Alhaji Abdourahaman
Mahaman General Manager, RAKAMS – Jamhuriyar Nijar. Injiniya Abdourahaman Mahaman gogaggen
shugaba ne a harkokin kasuwanci da gudanarwa a Nijar. Kwarewarsa a mu’amala
tsakanin al’ummomi da inganta harshen Hausa zai taimaka wajen karin haske kan
yadda rubutun Hausa ke tsallaka iyaka, da rawar da ’yan kasuwa da kafafe ke
takawa wajen yaɗa
adabin Hausa a ƙasashen waje.
3. Alh. Sule Muhammed Adamu
Sarkin Hausawa Kasar Guinea Bissau.
Shugaban 'yan Nijeriya mazauna ƙasashen waje. A matsayinsa na Sarkin
Hausawa kuma shugaba Alh. Sule Muhammed Adamu na da gogewa a jagoranci da al’adu
da haɗin kan al’umma.
Zai ba da gudummawa mai muhimmanci wajen rawar sarauta da ƙungiyoyi
a kare harshen Hausa, da tallafa wa marubuta da rubuce-rubucen Hausa a kasashen
waje.
4. Alh. Muhammad Bilal CEO/MD,
BILAL SEED. Alh. Muhammad Bilal kwararre ne a harkar kasuwanci, musamman noma.
Kwarewarsa za ta taimaka wajen danganta rubutun Hausa da tattalin arziki, wato
yadda adabi da wallafe-wallafe da
labarai ke tallafa wa ilimi da kasuwanci
da wayar da kai ga al’ummar Hausa a ƙasashen waje.
5. Alhadji Soulemana Yahaya PDG,
Centre Culturel Haoussa Du Togo. Shugaban Cibiyar Al’adun Hausawa na Kasar Togo. Alhadji Soulemana Yahaya jagora
ne a fagen al’adu da harshe. Zai yi bayani kan rawar cibiyoyin al’adu wajen
tallafa wa rubutun Hausa da adana al’ada, da ƙarfafa karatu da rubutu ta hanyar taruka,
baje-kolin al’adu, da
ayyukan ilmantarwa a Togo da kewaye.
Ko shakka babu wannan tattaunawa
za ta samar wa marubuta da manazarta haske da mafita na yadda za su baje
hajarsu a ƙasashen
waje.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.