Citation: Nasiru BABBA & Jamilu KABIR (2020). Nazarin Jigo A Waqar “Furan Gero” Ta Aliyu Namangi. Yobe Journal of Language, Literature and Culture (YOJOLLAC), Vol. .8 Department of African Languages and Linguistics, Yobe State University, Damaturu, Nigeria. ISSN 2449-0660
NAZARIN JIGO A WAQAR “FURAN GERO” TA ALIYU NAMANGI
Nasiru BABBA DA Jamilu KABIR
Abstract
The paper entitled “NAZARIN JIGO A WAQAR “FURAN GERO” TA ALIYU NAMANGI” attempt to analyse the central theme of the poem titled “Furan Gero” written by a famous Hausa poet Alhaji Aliyu Namangi. The Close Reading theory is used as theoretical framework of the analysis. Both written and oral literature (cassette) of the poem were employed to ascertain the originality of the poem and to avoid misrepresentation of the poet`s original wordings. Finally, the paper finds out that the Poet made use of some sub-themes such as “Mu`jiza” (Miracles), “Sunna” (Prophetic actions and sayings), “fifiko” (superiority of Prophet Muhammad SAW over other messengers) etc in order to deliver his main theme which is ‘Madahu’’ praise.
1.0 Gabatarwa
Waƙoƙin Madahu waƙoƙi ne da suka faro tun kafin ƙarni na 20. Waƙoƙi ne da ake yi domin a nuna yabo da bege ga mafificin Talikkai Annabi
Muhammadu, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi. Waɗansu masanan na ganin waƙoƙin madahu sun haɗa har da waƙoƙin da aka yi wa Waliyyai, amma ta la’akari da sauran jigogin da suka gina
jigon ya fi dacewa waƙoƙin su ta’allaƙa ga fiyayyen halitta, manzon Allah (SAW).
Jigon Madahu ya ƙunshi bayyana matsananciyar ƙauna ga Annabi Muhammadu (SAW), da bayyana buƙatar mawaƙi ta kusantarsa, wato kai
ziyara zuwa ƙabarinsa, da kuma fatan samun cetonsa a gobe ƙiyama. Haka ma mawaƙi kan bayyana kwaɗayinsa na samun ceto a gobe lahira. Bugu da ƙari mawaƙan kan bayyana mu’ujizar Annabi
(SAW) da ababen ban mamakin da suka faru da shi tun yana ƙarami. Sannan sukan bayyana
Isra’insa da Mi’irajinsa da Haskensa Halayensa da ma Sunnar da ya bar mana don
ta zamo abin koyi a gare mu.
Aliyu Namangi ya yi
waƙoƙi da dama a kan haka.
Wannan waƙa tasa ta “Furan Gero” ya yi ta ne don yabo da begen
Annabin Rahama (SAW), wannan jigo shi ake kira da madahu. A baiti na 305
mawallafin na cewa:
Waƙar raunana gazajje, da
yai na yabon gwarzon gwaraje,
Mafi darajan bayi na Dije, musayar waƙar ƙi-garaje,
Na
Ahmadu bai saba gudu ba.
A wannan baiti
mawallafin ya bayyana waƙar tasa da cewa, waƙa ce da ya yi don ya
yabi manzon Allah (SAW), wannan manufa tasa ita ce ake kira madahu, wato yin waƙa don a yabi ko a
nuna ƙauna ko bege ga Annabin rahama.
2.0 Taƙaitaccen Tarihin
Aliyu Namangi
Masana da ɗalibai da dama da
suka yi ayyuka a kan waƙoƙin Aliyu Namangi, sun kawo tarihinsa da ayyukansa. Daga
cikin waɗanda suka gudanar da
waɗannan ayyuka akwai;
Birniwa (1981) da Yakawada (1987) da Sankalawa (2005) da Babba (2011) da
Sulaiman (2011) da Kawu (2013) da Lawal (2016) da dai sauransu. Dukkan waɗannan sun kawo
tarihin Aliyu Namangi, don haka a taƙaice dai za a iya
cewa:
An haifi Aliyu
Namangi a garin Zariya a ƙauyen Mangi a shekara ta 1315 A.H, wadda ta yi dai-dai da
1894 A.D zamanin Sarkin Zazzau Kwasau. Asalin iyayensa mutanen Jibiya ne ta ƙasar Katsina.
Kakanninsa sun baro Katsina ne suka zo birnin Zazzau da zama a zamanin sarkin
Zazzau Hammada wajen shekarar 1846, kakansa Malam Atammu shi ne ya fara zuwa
Zariya da zama.
Bayan haihuwarsa da
shekara ɗaya, a watan safar
sai idanunsa suka tsiyaye a sanadiyyar cutar ƙyanda da ta agana. An
yi masa kaciya yana da shakara bakwai. Ya fara karatun Alƙur’ani a hannun Malam
Ibrahim, sai Malam Gambo, da ya shekara ashirin da ɗaya (21) sai
mahaifinsa (Malam Ishaƙa) ya yi masa aure.
Kasancewar Aliyu
Namangi Makaho, ana rubuta masa ne kuma a karanta masa sai ya haddace, idan ya
je gida ya ji ya manta sai ƙanensa Abdulƙadir ya tuna masa.
Bayan karatun Alƙur’ani ya yi karatun litattafai da dama da suka haɗa da Ahalari,
Ishimawi, Risala, Askari, Muhutasar, Hadisan Manzon Allah (S.A.W), Ishiriniya
Alburda da dai sauransu. Daga cikin malamansa akwai Malam Muhammadu Gwandu,
Malam Na’iya Zariya, Malam Ramalan Limamin Wushishi, Malam Yahuza Zariya, Malam
Sa’idu Kusfa, Malam Abdulƙadir Banufe, da dai sauransu.
Malam Aliyu Namangi
ya rubuta waƙoƙi da dama da aka ɗauka a kaset ko kuma waɗanda sakatarorinsa
suka rubuta. Daga cikinsu akwai; Kanzil Azim (Babbar Taska) da Tarjimul Sharari
(Jifan Shaiɗan) da Waƙar Infiraji da Waƙar Katifa da Waƙar Nafisa da Furan
Gero da Tsarabar Madina da Kuntugin Shaiɗan da Waƙar Ƙazama da Waƙar Basukur da kuma Waƙar Murnar samun
Digirin Girmamawa da dai sauransu.
Malam Aliyu Namangi
mabiyin ɗariƙar Tijjaniyya ne,
kuma ɗan Mazhabar Malikiyya
ne. Ya rasu bayan wata rashin lafiya (Matsalar fitar fitsari) ta tsawon sati
biyu. Ya rasu ranar 27/4/1994, yana da kimanin shakaru ɗari (100) ko ɗari da biyu (102)
wato (1894 – 1994), ya rasu ne a gidansa da ke Unguwar Nufawa da ke birnin
Zariya, ya bar ‘ya’ya ashirin da ɗaya (21), maza goma sha huɗu (14), mata kuma
bakwai (7). Ya kuma bar matansa na aure guda uku da suka haɗa da Khadija, Mariya,
da kuma Zainab.
Yawancin waƙoƙin da ake ji a
kasasuwa ba muryar Aliyu Namangi ba ce, muryar Abdulmumini Makaho ce (Wazirin
Aliyu Namangi). Wannan bawan Allah ya haddace yawancin waƙoƙin Aliyu Namangi,
kuma ya rera su. Daga cikin masu rubuta waƙoƙin Aliyu Namangi
(wato Sakatarorinsa) akwai; Ahmadu Tijjani, Umaru Na Malam Balarabe Kusfa, Ɗalhatu Muhammad
Zariya, da Magaji Tsoho Yakawada.
3.0 Ma’anar Jigo
“Abin da ake nufi da
jigo shi ne saƙo, manufa ko abin da waƙa ta ƙunsa, wato abin da
take magana a kai. A taƙaice jigo yana nufin dunƙulalliyar manufa...”
(Ɗangambo,
2008, sh. 12).
Ɗangambo ya ci gaba da
cewa; “kafin mutum ya ɗauki alƙalaminsa ya yi wani
rubutu ko wani furuci, lallai ne ya kasance yana da wata manufa a ransa. To
wannan manufa ita ce jigo”.
Yahya (1997) ya kawo
ma’anar jigo da cewa; “jigo a fagen waƙa yana nufin saƙo ko manufa ko bayani
ko ruhin da waƙa ta ƙunsa wanda kuma shi ne abin da waƙar ke son isarwa ga
mai sauraro ko karatu ko nazarinta” (sh. 75).
Ta lura da waɗannan ma’anoni, za a
iya cewa, Jigo saƙo ne ko manufa da waƙa ta ƙunsa wanda mai
sauraro ko nazari zai iya fitarwa daga waƙa, kuma jigon ya
ratsa waƙa ne daga farkonta har zuwa ƙarshe.
3.1 Jigon Waƙar ‘Furan Gero” ta
Aliyu Namangi
Yahaya (1997) yana
cewa,
Waƙoƙin madahu waƙoƙi ne da aka rubuta
domin yabon Annabi Muhammadu tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi.” Ya
ci gaba da cewa, “kamata ya yi wannan suna ya keɓanta ga irin waɗannan waƙoƙi, kar ya haɗa da waƙoƙin da aka rubuta
domin yabon waliyyai. Dalili kuwa shi ne galibin jigon da waƙoƙin madahu suka ƙunsa sun shafi Annabi
ne kurum ban da waliyyai” (p.92).
Wannan bayani yana
nuni da cewa jigon Madahu jigo ne da ya mamaye waƙoƙin da aka tsara a kan
yabo da tsananin ƙauna ga Manzon tsira Annabi Muhammadu (S.A.W). Don haka
wannan waƙa ta “Furan Gero” ta ƙunshi wannan jigo na
“Madahu”, domin kuwa waƙa ce da ya tsara a kan yabo da begen Annabi Muhammadu
(S.A.W), kuma ya tsara ta ne babi-babi, ya waƙe Annabi tun daga
samuwar cikin “Haihuwarsa” (S.A.W) har ya zuwa “aiko shi Duniya da Jin ƙan masu ban gaskiya”.
Tun a babi na farko
“Yabo” ya ambaci jigonsa da kansa a baiti na huɗu, inda ya bayyana aniyarsa cewa yabo
zai yi ga Annabi Muhammadu (S.A.W). Ga dai abin da yake cewa;
B.4
A bai baicin na cika basmalata, ga Allah na
dafa salsalata,
Ga Annabi na cika hamdalata, ga Allah amma
aniyata,
Yabo ga Muhammadu ɗan Suwaiba.
A wannan baiti a ɗangon ƙarshe, mawallafin ya
fitar da jigonsa a taƙaice cewa yabo zai yi ga Annabin ƙarshe Muhammadu
(S.A.W).
Wannan jigo na madahu
akwai ƙananan jigogi da suka haɗu suka gina shi. Don haka wajen fito
da jigon za a rinƙa lalubo ƙananan jigogi ne da suka haɗu suka gina wannan
jigon. Za a riƙa yi ana kawo misalan baitocin waƙar “Furan Gero” a
matsayin warwarar jigo.
3.1.1 Ƙauna
Ƙauna kalma ce da ke nuna
tsananin so ga wani abu. Duk abin da mutum ke ƙauna to yana matuƙar son sa. Haka kuma babu yadda za a yi mutum ya ƙaunaci abin da ba ya so.
Jigon ƙauna ya shafi bayyana
tsananin son da mawaƙi ke yi ga Annabi (S.A.W). Mawaƙi yakan ambaci wasu
abubuwa da suka keɓanta ga Manzon
(S.A.W), domin su tsaya a matsayin hujjojinsa na son da yake yi ga Annabi. Haka
kuma mawaƙi kan faɗi wasu siffofi da suka keɓanta ga Annabi (S.A.W), duk dai don ya
nuna tsananin son sa ga Annabi Muhammadu (S.A.W).
Ga dai abin da Aliyu
Namangi ke faɗa dangane da ƙaunar da yake yi wa
Annabi Muhammadu (S.A.W).
B. 21
Ma’aikin Allah shugabana, izan na tuna ka
saboda ƙauna,
Nakan yi kamar in sai da raina, in san guzuri
tun mai kirani,
Zuwa ƙabarina bai kira ba.
B.51
Ina son wannan Annabi ni, Aliyu Muhammadu mai
mazauni,
A’alal iliyina minal janani, daɗa jirgin sama zo ka kai ni,
In ga
kushewar ɗan Suwaiba.
Mawallafin a waɗannan baitoci ya nuna
tsananin son sa ga manzon tsira, fiyayyen Halitta, Annabi Muhammadu (S.A.W).
Hausawa idan suna so su nuna tsananin son da suke yi ma wani abu, sai su ce,
‘kamar su sayar da kansu’, ya nuna irin kwaɗayinsa na so ya je Makka ne tun kafin ya koma
ga mahaliccinsa. Dubi yadda Aliyu Namangi ke magana da jirgin sama duk da ba ya
jinsa, duk don tsananin son sa ga zuwa Makka. Haka kuma da bakinsa ya furta
cewa yana son Annabi, wannan furuci ya fassara abin da zuciyarsa take ɗauke da shi, kuma ta
daɗe da ƙudurtawa.
3.1.2 Fifiko
Fifiko kalma ce da ke nuna wani ya fi wani ta wani ɓangare na rayuwa. Kalmar na nuna tazarar da ke akwai
tsakanin wani da wasu ta ɓangaren sifa ko launi ko ƙirar jiki ko kuɗi ko ilimi ko ɗaukaka ko nasaba ko ma dai wani abu daban.
Jigon fifiko shi ma
muhimmi ne a waƙoƙin madahu. A wannan jigo, mawaƙi kan bayyana zamowar
Annabi (S.A.W) mafificin dukkan abin da Allah maɗaukaki ya halitta. Ta ƙoƙarin bayyana wannan
fifiko ne mawaƙi kan shiga zayyana abubuwan da suka keɓanta ga Annabi
(S.A.W). tare da cewa sun rinjayi na sauran Annabawa. Yahya, (1997 sh. 95).
Mawallafin waƙar “Furan Gero” ya
kawo baitocin da suke nuni da fifikon Annabi Muhammadu (S.A.W) a kan duk wani
ma da Allah (S.W.T) ya halitta. Ga dai abin da yake cewa:
B.5
Ma’aiki ne shi wanda kowa, ya zamo ƙashiyansa shi ke
tsayawa,
Ya fi Annabi Adamu ya fi Hauwa, fikon daraja
balle daɗewa,
Da akai
shi ba ai yo duniya ba.
Mawallafin ya fito da
fifikon ma’aikin Allah ƙarara ta yadda ya bayyana fifikonsa a kan Annabi Adamu da
Hauwa’u, kasancewarsu su ne farkon waɗanda Allah ya halitta a bisa doron ƙasa. Tarihi ya
bayyana mana tarihin waɗannan bayin Allah da
suka fara zama a cikin aljanna, haka duk al’ummar duniya baki ɗayanta da ma waɗanda za su zo nan
gaba har ya zuwa tashin duniya ana danganta su da ‘ya’yan Adam. Amma duk da
haka Aliyu Namangi ya bayyana ma’aiki da wanda ya fi su daraja har ma da
kasancewarsa, domin ya ce an halicce shi tun kafin a halicci duniyar.
B.23
Don haka ne kowa ya saɓe, ka za shi wuta ba
raɓe-raɓe,
Da Albarka Allah ya keɓe, Ka Sidi Muhammadu
ka ci zaɓe,
Ta fiko
ba da Mahawara ba.
Kasancewar Annabi
Muhammadu (SAW) zaɓaɓɓe cikin zaɓaɓɓun mutane, shi ne
dalilin da ya sanya Aliyu Namangi ya bayyana shi a matsayin wanda ya yi zarra
ta fuskar fifiko, ba shi ma da waɗanda za a iya kwatanta shi balle a ce
mahawara aka yi.
B. 71 Marhaba zaɓaɓɓen mutane, da aljannu
hasken birane,
Mun shaida kai Annabi ne, na Allah kai Manzon
kira ne,
Zuwa
rahama ba hallaka ba.
Hausawa na cewa,
‘Idan ana babbakar Giwa ba a jin ƙaurin Ɓera’’. Fifikon manzon
Allah (SAW) ba ma ga mutane ba ne kaɗai, Aliyu Namangi ya bayyana fifikonsa a kan
duk mutanen da Allah ya halitta a bisa doron ƙasa, har ma da
aljannu baki ɗaya. Dukkan waɗannan baitoci suna
nuna irin fifikon Annabi Muhammadu (S.A.W) ga sauran Annabawa da mutane da
aljannu.
3.1.3 .Mu’ujiza
Wannan balarabiyar kalma ce. Tana nufin aukuwar wani abu wanda ya
wuce fahimtar hankalin ɗan’adam. Mu’ujiza na nuna ɗaukaka da gaskiyar kowane Annabi.
Wannan jigo na
bayyana abubuwa na al’ajabi da Allah ya ba wa Annabi (S.A.W). Mu’ujiza ita ce
aukuwar wani abu wanda ya shige fahimtar hankalin ɗan’adam. Takan ɗauro abin ya auku ba
tare da wani aiki ko magana daga Annabi, ko kuma shi Annabi ya aikata wannan
abu. Mu’ujiza na nuna ɗaukaka da gaskiyar
Annabi. Babbar mu’ujizar Annabi (S.A.W) ita ce Alƙur’ani sauran kuwa kaɗan daga cikinsu
akwai; Nishi da kututturen dabino ya yi da Annabi (S.A.W) ya hau shi, zubowar
ruwa daga yatsun Annabi (S.A.W), magana da Dabbobi ko tsuntsaye, tafiyar
girgije da sauransu. Yahya (1997, sh. 96).
Mawallafin waƙar “Furan Gero” ya
kawo wasu daga cikin mu’ujizojin Manzon Allah (S.A.W) da suke tabbatar da ɗaukaka da gasgata
Annabi (S.A.W). ga dai abin da mawallafin ke cewa:
B.12
Damo da barewa sun yi zance, da Annabi ya yi
kiran itace,
Ta tumɓuka ta je ta yi kwance, gaba nasa Annabi ya
yi zance,
Da yaro
tun bai yi shekara ba.
Damo da Barewa
dukkaninsu halittu ne (dabbobi) da Allah ya halitta, kuma suna rayuwa ne a
cikin daji, mafarauta kuma na shiga dazuka su farauto su, amma sai ga shi
dukkaninsu sun yi magana da manzon Allah (SAW). Wannan abu da ya faru abin
mamaki ne matuƙa, don ko ga masu sihiri abu ne mawuyaci su yi magana da
dabba. Haka kuma wani abun mamakin shi ne, manzon ya kira itaciya ta amsa kiran
ta kuma tumɓuko ta zo ta same
shi. Sannan kuma manzon har ila yau, ya yi magana da yaro ɗan ƙarami tun bai ƙulla shekara ɗaya ba. Dukkan waɗannan abubuwa ne na
ban mamaki (mu’ujiza) da suka ƙara tabbatar da manzancinsa (SAW).
B.22
Rasulu mafificin ma’aika, da kai aka ma ƙirga iyaka,
A kai maka laima girgije ka, fi Manzanni
sauran maɗauka,
Amana
sun shaida ka babba.
Wata mu’ujizar da
Aliyu Namangi ya bayyana Annabi da ita ita ce, tafiyar da giza-gizai ke yi don
yi wa manzon Allah inuwa a duk inda zai je, wanda wannan wata alama ce da wani
malamin kiristoici (Rahibu Bahira) ya gane manzon da ita, don ya karanta hakan
a cikin litattafansu. (Abduljabbar, sh. 8 da 12). Wannan ma wata mu’ujiza ce da
ta keɓanta ga manzon Allah
(SAW).
B.42
Ya tsagu da yac ce mai shi tsage, Mutane kowa
na ta hange,
Fage nasa ya tsere fagage, Ma’aikin Allah ba
da waige,
Shi kan
ga abin da ke zuwa ba.
B.43
Da ya ce rana koma da baya, ta kusanci ta faɗa sai ta juya,
Kamar kibiya domin biyayya, ta je la’asar haka
ya buwaya,
Ba aji
ta ga dukkan Annabi ba.
A waɗannan baitoci ma
Aliyu Namangi ya bayyana wasu mu’ujizoji da suka keɓanta ga Annabin.
Allah ya halicci kowane ɗan’adam ne da idanu
biyu da zai ga abin da yake fuskanta da su, ya kuma ga abin da ke bayansa idan
ya juya. Amma sai ga shi Manzo na kallon abin da ke gabansa da kuma bayansa.
Haka kuma ya bayyana yadda Manzon ya umurci rana kuma ta bi umurninsa da yardar
Allah. Dukkanin waɗannan abubuwa ne na
ban mamaki da suke ƙara gasgata manzancinsa ga waɗanda suke inkarin
hakan.
B.234 Yana nan sai wahayi ya sauka, aka ce masa
tsira na gare ka,
Da aminci kai da mataimakanka, ta’ala Jalla ba
za shi bar ka,
Da
kunyar kowa duniya ba.
Wata mu’ujizar kuwa
kuma da ta zarce kowace ita ce, wahayi da ake masa. Wannan wahayi shi ne al’ƙur’ani da ake saukar
masa ta hanyar turo masa mala’ika Jibrilu don ya karanta masa wasu ayoyi.
3.1.4 Haske
Hausawa kan ce, ‘Haske maganin duhu’’. Haske wani yanayi ne da yake zuwa
domin ya yaye duhu. Idan aka ce duhu ya yaye, to haske ya bayyana ke nan. Yahya, (1997, sh. 97)
yana cewa, “Mawaƙi yana bayyana Annabi (S.A.W) a matsayin hasken da ya
fitar da duniya daga cikin duhu. Haske ne na ilimi mai dushe jahilci. Haske ne
mai fitar da ɗan’adam daga ɓata ya sa shi cikin
shiryuwa. Mawaƙi kan bayyana Annabi (S.A.W) a matsayin mutum mai
tsananin kwarjini wanda ke da jiki mai haske”
Ya kuma ci gaba da
cewa, “Wasu mawaƙa masu zurfin ilimi musamman na sufanci sukan fito da
wannan jigo ta ambaton wanzuwar wani haske tun kafin Allah maɗaukaki ya halitta
wani abu. Wato wannan haske shi aka fara halittawa. To wannan haske shi ne
Annabi (S.A.W), kuma ya zauna cikin Annabawa tun daga Annabi Adamu har zuwa ga
mahaifan Annabi (S.A.W) waɗanda suka haife shi”.
Mawallafin waƙar “Furan Gero” ya
kawo wasu baitoci da suka shafi wannan jigo, kasancewar sa mai zurfin ilimi da
tunani da basira. Ga dai abin da Aliyu Namangi ke faɗa:
B.15
A gai da abokaina fataken, zuwa Makka Jalla ya
sa a sauke,
Ku tare da albarka cikakke, ku iyar da
jawabina ga haske,
Da ya
zo bai bar wanjin duhu ba.
A wannan baiti
mawallafin ya bayyana manzon Allah (SAW) da hasken da ya zo duniya a lokacin da
duniyar ke cikin tsananin duhu. Shiriyar da ya zo da ita ita ce ta tsaya a
matsayin haske, duhu kuwa shi ne jahilci da ɓata da al’umma ke ciki a zamanin. Ga kuma
wani baitin:
B. 54
Izan ka gane shi cikin mutane, suna tafe ne
koko a zaune,
Sai ka gane shi kamar wata ne, cikin taurari
mai sifa ne,
Da bai
yi gajarta ko tsayi ba.
Aliyu Namangi ya daɗa bayyana wata sifa
da ake gane manzon Allah (SAW) da ita, idan yana cikin taron mutane. Wannan
sifa ita ce haskensa. Ya bayyana cewa yadda hasken wata ya zarce na taurari a
sama, to haka hasken jikin manzon Allah (SAW) ya bambanta da na sauran mutane,
ta yadda duk yadda jama’a ta taru, sai an gane shi ta dalilin haskensa (SAW).
Akwai ma wasu baitoci
da mawallafin ya kawo da suke nuna irin wannan haske a lokacin da Aminatu ta
sami cikin Manzon Allah (S.A.W), da kuma wani haske da ya bayyana a lokacin da
aka haife shi, da kuma wani hasken da ya bayyana a lokacin da Halimatu ta zo ɗaukar Manzon Allah
(S.A.W) don ta shayar da shi. Ga dai abin da mawalafin ke cewa:
B.83
Amina ta ce da ya zo gare ni, sai na ji ƙamshi ya rufe ni,
Annuri ya baibaye ni, ashe baiwa ce min
ladunni,
Ba ba a
ba kowa duniya ba.
B.101
Suka ce mani to taro jikinki, Amina gare mu mu
taimake ki,
Annura ta haska ɗaki, da ƙamshi sai muryan
dawaki,
Jaha da
jaha ba su bar zuwa ba.
Mawallafin ya daɗa fito da wannan jigo
a inda ya bayyana wani nau’i na haske da Aminatu (mahaifiyar manzon Allah (SAW)
ta rinƙa gani albarkacin cikinsa da take ɗauke da shi da ma
lokacin haihuwarsa. Haka ma abin yake a lokacin da Halimatus Sa’adiyya ta zo
neman shayarwa, ita ma Allah ya bayyanar mata da wannan haske lokacin da ta
shiga wajen Halimatu, ita tsammaninta fitila ce aka kunna a ɗakin, amma sai
Aminatu ta tabbatar mata da cewa ba fitila ba ce, tun da ta haife shi ba ta
kunna wata fitila ba don yaye duhu, haskensa ya ishe ta. Ga abin da Aliyu
Namangi yake faɗa dangane da hakan:
B.143
Da shiga haske na gani jimilla, na ce har
ranar nan na Allah,
Kike kunna ma ɗa fitilla, ta ce da na haifasa har da
Allah,
Ban
kunna fitilla don duhu ba.
3.1.5 Ceto
Ceto shi ne ka taimaka wa wani wajen tsamo shi daga wata
halaka da ka ga zai faɗa. Misali, wanda ruwa zai haɗiye, idan ka kawo masa ɗauki, to ka cece shi. Mawaƙin yana bayyana
matsayin Annabi (S.A.W) na mai ceton bayi a ranar lahira. Bayanin da ya fi
fitowa shi ne jadadda cewa babu wani taliki da Allah zai ba ikon ceton bayi a
ranar lahira in ba Annabi Muhammadu (S.A.W) ba. A nan ne zai bayyana kwaɗayinsa ga samun shiga
cikin waɗanda Annabi zai ceta.
Zai shiga yin addu’a yana roƙon Allah domin darajar Annabawa da
Waliyyai da kuma Annabi Muhammadu (S.A.W) domin Allah ya yarda Annabi ya cece
shi. Yahya, (1997, sh. 102).
Mawallafin waƙar “Furan Gero ya
kawo wasu baitoci da ya fito da wannan jigo kasancewarsa mai tsananin son
Manzon Allah (S.A.W). Ga dai abin da yake cewa:
B.45
Rasulullahi irin mazowa, daraja ɗan’adam da Hawwa,
Tafo ka riƙan ranar cikawa, in
sha ƙamshinka ina natsawa,
A zare
raina ban sani ba.
B. 53 Zuwa nasa
addini ya rayu, ta san matsaya kowa ya shiryu,
Maji kukan ‘ya’ya marayu, riƙa ni a dama ka ce
Aliyu,
Taho
nana tun gu bai matse ba.
Mawallafin ya duƙufa wajen neman
fiyayyen halitta ya kawo masa agaji a lokacin da za a zare ransa, ya yi
tawassuli (neman tsani) da darajar iyayenmu wato Adam da Hauwa’u. Aliyu Namangi
na fatan ya kasance kusa da manzon Allah (SAW) a gidan aljanna, kuma yana fatan
ya kasance a hannun dama. Daga ƙarshe mawallafin ya yi burin cikawa da
imani da samun tsira a gobe ƙiyama albarkacin dukkanin Annabawa da
Manzanni, kamar dai yadda yake cewa:
B. 308 Aliyu yana roƙon cikawa, da Imani
har ran tsayawa,
Da albarkar Adam da Hauwa’u, domin girman
Annabawa,
Da
ma’aika kowa ban rage ba.
3.1.6 Siffofi
Siffofi jam’i ne na Sifa. Sifa kalma ce da take Karin bayani a kan
suna. Idan aka sifanta wani abu, to hoton abin da aka sifantar zai bijiro wa
zuciyar wanda aka bayyana wa sifar. Mawaƙan madahu na amfani
da wannan jigo a waƙoƙinsu. Mawaƙa kan bayyana wasu
siffofi na Manzon Allah (S.A.W), wasu ma saboda karatunsu na addini idan suna
bayyana siffarsa sai ka ga kamar ga shi nan kana kallonsa a zuciyarka.
Mawallafin waƙar “Furan Gero” ya kawo wasu siffofi na Manzon Allah
(S.A.W), kamar dai yadda yake cewa:
B. 57
Ba shi a dogo ba gajere, ga idandunansa biyu
farare,
Annabi yana da tsawon gashin girare, zufa nasa
ya fi ruwan turare,
Ga ƙamshi ba sai na faɗa ba.
Mawallafin ya bayyana
siffofin ma’aiki (SAW), inda ya bayyana shi da siffofi masu ban sha’awa da kuma
tsananin fata da son ganin wanda ya keɓanta da waɗannan siffofi. Hausawa na cewa, ‘mutum tara
yake’’, amma sai ga shi ta lura da waɗannan siffofi da aka bayyana mana mun fahimci
Manzon Allah (SAW) ya cika goma cif. Hausawa na cewa, ‘Goma da goma sai ɗan gata’’! Bayan
siffofin da aka bayyana a wannan baiti, Aliyu Namangi ya faɗa mana yadda gashin
kan ma’aiki (SAW) yake, a inda yake cewa:
B. 60.
Kai nasa ba mai furfura ba, gashinsa baƙi ne bai yi ja ba,
Da kansa geme in ka duba, ba mu ce maka ba
gashi fari ba,
A sha
tara kau ba zai haye ba.
Haka kuma mawallafin
ya bayyana yanayin tafukan hannuwan ma’aikin suke, inda ya bayyana mana cewa
suna da taushi matuƙa. Akaifunsa kuwa suna haske ƙwarai. Dangane da ƙamshin jikinsa kuwa,
wane mutum! Ga dai abin da Aliyu Namangi ke faɗa:
Akwai shi da haskakar akaifa, tafinsa da
taushi sun fi taffa,
In ya yi riƙo ko ya yi shafa,
jikin tutuwa koko ya dafa,
Ba a
rasa ƙamshin shekara ba.
3.1.7 Abin Mamaki
Kalmar na bayyana wani abu da ba a saba gani ba. Ganin abin zai sanya kai
ya kulle har a rinƙa tunani a kan yadda abin ya wakana. Mawaƙan madahu na amfani
da wannan jigo a waƙoƙinsu don su fito da wasu ababe na ban mamaki da suka faru
ga Manzon Allah (S.A.W), wasu daga ciki tun kafin ya zo duniya ne wato sun
bayyana ma tun ga iyayensa, wasu kuma a lokacin haihuwarsa, wasu kuma yana
jariri, wasu kuma yana yaro ƙarami.
Waɗannan abubuwa na ban
mamaki da suka faru ga Manzon Allah (S.A.W) suna da yawan gaske, wasu daga ciki
bayan an ba shi annabta da manzanci sun zamo mu’ujizoji. Mawallafin wannan waƙa ya fito da waɗannan da dama a cikin
waƙarsa
“Furan Gero”. Ga wasu daga ciki:
B.118
Da shansa da yankan cibiya nai, aka haifasa ga
aski a kai nai,
Akwai kwalli ga idaduna nai, biyu ba belo
cikin wuyanai,
Aka
haifasa ba mai datti ne ba.
A al’adance ana
haihuwar mutum ne ba huntunsa, sai bayan ya zo duniyar ne za a yi masa abubuwa
na al’ada da suka haɗa da yankan cibiya da
aski da cire hakin wuya da sauransu. Amma abin mamaki sai ga shi an haifi
manzon Allah (SAW) da dukkan waɗannan, har ma da shayinsa, kuma babu wani datti a tare da
shi. Wani abin mamakin kuma shi ne, lokacin da Halimatus Sa’adiyya ta zo ɗaukar ma’aikin Allah
domin ta shayar da shi, da ta ba shi mamanta na dama sai ya kama, amma da ta
juya ga na hagun sai ya ƙi karɓa, ashe da ma akwai jinjirin da ke shansa a gida. Kuma
duk wannan ya faru ƙasa da kwana ashirin da haihuwarsa. Ga abin da Aliyu
Namangi ke faɗa:
B. 145
Na kawo mamana da dama, na baiwa Ma’aiki sai
ya kama,
Ya tostsa na juyo hagun ma, na bai wa
Muhammadu wai ya kama,
Saboda
adala bai riƙa ba.
B. 146
A kai masa ilhami da yaro, a gida mai shan
wannan na waro,
Na bar shi zuwana wanga taro, abin da yake daɗa ba ni tsoro,
Bai
kwan ishirina a duniya ba.
Bayan waɗannan abubuwan mamaki
da suka faru, sai kuma lokacin da Halima da mijinta suka ɗauki ma’aikin Allah a
bisa jakinsu zuwa ƙauyensu Bani Sa’ad, sai ga shi wannan gurgun jaki nasu
ramamme da kowa ya wuce su a kan hanyar su ta zuwa, abin mamaki sai ga shi ya
zabura yana sauri duk ya ma wuce ayarin da suke tafiya.
B. 150
Kuma sai muka hau jakinmu gurgu, ya miƙe sai tafiya awa
guguwa,
Don sauri in ya fisgu, kamar ya fashe ko ko ya
tsagu,
Sabad
da ƙiba
ba ƙanƙani ba.
Abubuwan ban mamaki
dangane da manzon Allah (SAW) ba su ƙidayuwa kuma ba su ƙarewa. Duk jaririn da
aka Haifa zuwa lokacin yayensa akwai wasu abubuwa na al’ada da zai rinƙa yi da dama. Amma
ma’aikin Allah ga yadda ya kasance:
B. 149
Kamar kuka marashin dalili, da ƙyuya ko fetsa da
bauli,
A baya Halima ta ce da gwalli, ba shi kan yi
ba har nai infisalin-
Sa ban
rasa barci na sake ba.
Halimatus Sa’adiyya
ta ce ba ta fuskanci wani abu mai kama da haka ba a lokacin da take shayar da
shi, irinsu ƙuiya da yawan kuka da yawan fitsari da zawo da hana ta
barci, duk ba ta fuskance su ba har ta yaye shi (SAW).
4.0 Kammalawa
Wannan takardar ta
bayyana wanene Aliyu Namangi, da waƙarsa mai suna ‘’Furan
Gero’’ da ya gina a kan jigon madahu. An bayyana yadda masana suka yi bayanin
yadda jigon madahu yake. An kuma fito da ƙananan jigogin da
suka tallafi babban jigon. Takardar ta yi nazarin jigon filla-filla ta hanyar
yin bayani a kan kowane ƙaramin jigo, tare da kawo misalai daga baitocin waƙar, an kuma yin
sharhi daidai gwargwado domin dai a fito da yadda jigon yake fili.
Manazarta
Abduljabbar,
U. (babu shekara). Khulasatu nurul yaƙeen fi
sirati sayyidil mursalin li talamizil ibtida’iyyah. Darul Fikr.
Babba,
N. (2011). Waƙa ko
wa’azi? Nazari da sharhi a kan waƙoƙin ifiraji na Aliyu Namangi ta 2 da ta 3. [B.A. Project].
Umaru Musa ‘Yar’adua Uniɓersity.
Birniwa,
H.A. (1981). The infiraji I and IƁ of Aliyu Namangi. [M.A Thesis]. Uniɓersity of London.
Ɗangambo, A. (2008). Ɗaurayar gadon feɗe waƙa. Amana Publishers.
Namangi,
A. (1978). Waƙar infiraji 1
– 4. N.N.P.C.
Kawu,
B. (2013). Falsafar Bahaushe a waƙoƙin
infiraji, juzu’i na huɗu. [Kundin digiri na farko]. Jami’ar Ahmadu Bello.
Lawal,
G. (2016). Wa’azi da sigar raha a waƙar kuntugin Shaiɗan ta Aliyu Namangi. Takardar Da Aka Gabatar A Taron Ƙara Wa
Juna Sani.
Jami’ar Ahmadu Bello.
Namangi,
A. (1978). Waƙar furan gero da tsarabar Madina. N.N.P.C.
Sankalawa,
D.H. (2005). Kwatanta wasu waƙoƙin
Aliyu Namangi da takwarorinsu na Sani Yusuf Ayagi. [Kundin digiri na
farko]. Jami’ar Bayero Kano.
Sulaiman,
M.S. (2011). Kwatankwacin jiddil ajizi ƙwazon
gajiyayye ta M. Shi’itu da waƙar kanzil azimi babbar taska Ta Aliyu Namangi. [Kundin digiri na
biyu]. Jami’ar Ahmadu Bello.
Tsoho,
M.Y. (1987). Tarkakken matanin waƙar
kanzil azim ta Aliyu Namangi. [M.A Thesis]. Jami’ar Ahmadu Bello.
Yahya, A.B. (1997). Jigon nazarin waƙa. Fisbas Media Services.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.