Article Citation: Yusuf, J. & Sani, A-U. (2025). Yarfe a tarihin siyasar jam’iyyu a ƙasar Hausa: Duba cikin rubutaccen zube. Scholars International Journal of Linguistics and Literature, 8(10): 234-246. https://doi.org/10.36348/sijll.2025.v08i10.001.
YARFE A TARIHIN SIYASAR JAM’IYYU A ƘASAR HAUSA: DUBA
CIKIN RUBUTACCEN ZUBE
Na
Jibril
YUSUF, Ph.D.
Department
of Nigerian Languages and Linguistics,
Kaduna
State University, Nigeria
Email:
yusuf.jibril@kasu.edu.ng
Phone:
+2347030399995
Da
Abu-Ubaida SANI, Ph.D.
Department of Languages
and Cultures,
Federal University Gusau,
Zamfara, Nigeria
Email: abuubaidasani5@gmail.com | abu-ubaidallah@fugusau.edu.ng
ORCID: https://orcid.org/0000-0001-6447-4334 | WhatsApp: +2348133529736
Tsakure
Manufar wannan takarda ita ce nazartan
yadda ‘yan siyasa suke amfani da abubuwa na ɓatanci ga abokan hamayyarsu na
siyasa. Tunanin wannan takarda ya taso ne duba da yadda ‘yan
siyasa suka mayar da wannan abu tamkar in babu shi to siyasar ma ba za
ta yiwu ba. Wannan ya sa aka ga dacewar a
shiga cikin ayyukan adabi na rubutaccen zube a gani shin ‘yarfe’ yana da asali ne tun kafuwar siyasar
jam’iyyu ko kuwa bai daɗe da samuwa ba? An
yi nazarin yarfe a cikin tarihin siyasa da aka kundace a cikin ayyukan
rubutaccen zube. An ɗora binciken kan ra’in ‘Tarihanci’ inda ya yi jagorancin
zaƙulo tarihin yarfe a harkokin siyasar ƙasar Hausa. Takardar ta
gano cewa, yarfe abu ne da ya ginu a cikin siyasar jam’iyyu tun daga farkon
lamari. Bugu da ƙari, har yanzu ana amfani da shi domin
neman ƙarin mabiya da kuma shafa wa abokan
hamayyar siyasa kashin kaji, wanda hakan kan taimaka ga samun nasara ko faɗuwa
a zaɓe.
Fitilun Kalmomi: Yarfe, Siyasa,
Jam’iyyun Siyasa, Ƙasar
Hausa
1.0 Shimfiɗa
Samuwa da bunasar siyasar
jam’iyyu a asar Hausa ya zo da wasu abubuwa da suka zama tamkar gishiri a cikin
miyar siyasar a ƙasar Hausa. Tun a farkon siyasar jam’iyyu, a ƙasar
Hausa an riƙa samun musayar yawu daga magoya bayan jam’iyyu
masu hamayya da juna. An samu rubuce-rubuce cikin jaridu da wasiƙu
da jawaban siyasa waɗanda suke ƙunshe
da al’amuran siyasa da suka faru a wancan
lokacin. Yarfe yana daga cikin irin waɗannan abubuwa da
suka zama tamkar ruwan dare a cikin siyasar jam’iyyu, kuma ya ci gaba da gudana
har zuwa wannan jamhuriya da ake ciki, wato jamhuriya ta huɗu. Ayyukan adabi sun riƙa fito da hoton
yadda al’amuran suka shafi yarfen suka riƙa gudana, inda aka
riƙa amfani da su domin shaf wa jam’iyyu
da ‘yan siyasa kashin kaji, ta hanyar manna
masu wani aibu da ba su ji ba, ba su gani ba. Irin waɗannan al’amura na ɓatanci ga jam’iyya da magoya bayansu shi ne wannan takarda ta ƙuduri
aniyar yin nazarinsu domin ganin yadda suka ginu a cikin tarihin siyasar jam’iyyu
a ƙasar Hausa.
Nazari a kan ayyukan adabi da suka haɗa da rubutattun waƙoƙi da rubutattun wasannin
kwaikwayo da kuma rubutattun zube ba sabon abu ne a fagen nazarin Hausa ba,
musamman idan aka yi la’akari da irin
gudummawar da masana da manazarta suka bayar wajen fito da muhimman abubuwan da
suka ƙunsa. Masana da manazarta irin
su Mashi (1986) da Birniwa (1987) da Funtua (2003) da Ɗangulbi (2003) da Ɗan’illela (2010) da
Sani (2012) da Adamu (2019) da Adamu (2021) sun yi waɗannan nazarce-nazarce ne ta la’akari da yadda
adibai suka baje kolin basirarsu kan al’amuran siyasa a cikin ayyukansu na
adabi. Yawancin nazarce-nazarce da ayyukan da aka gudanar sun shafi nazarin zubi
da tsari da salo da kuma jigo ne; sai aikin Idris (2016) ya yi nazarin bijirewa
a waƙoƙin siyasa da Yusuf (2018)
wanda ya yi nazarin tarihin Jam’iyyar PDP a cikin
rubutattun waƙoƙin siyasa.
Dangane da batun
samuwa da bunƙasar
siyasar jam’iyya kuwa, za a iya alaƙanta shi da cuɗanyar da aka samu tsakanin Turawa da al’ummar ƙasar Hausa. Birniwa,
(1987 sh. 27-28) ya bayyana cewa tun a wuraren shekarun 1930-1940 ne aka fara
jin ƙamshin samuwar ƙungiyoyin siyasa a
Arewacin Nijeriya. An samu ɓullar ƙungiyoyi
da dama duk da cewa ba su fito fili ƙarara a karon farko sun kira kansu da jam’iyyun siyasa ba, amma dai
sun samar da cibiyoyin da sukan riƙa
haɗuwa lokaci-lokaci
domin tattauna al’amuran siyasa. Su kuwa Dudley (1968 sh. 78-79) da Idris (2016 sh. 51)
suna da ra’ayin cewa, an fara samun ɓullar ƙungiyoyi
ne a tsakanin shekarar 1943-1944. Ƙungiyoyin
da aka samar wannan lokacin sun haɗa da; Ƙungiyar
Inganta Rayuwar Mutanen Bauchi (BGIU) wadda Sa’adu Zungur ya kafa a 1943, da Ƙungiyar Tattaunawa ta
Mutanen Bauchi (BDC) a 1944, da Ƙungiyar
Zumunta ta Sakkwato (YSC) a 1945, da Ƙungiyar Matasa ta Kano (KYA) a 1948 da Ƙungiyar Matasan
Zariya (ZYA) ita ma a 1948 da sauransu. Waɗannan ƙungiyoyi da ma wasu duk an kafa su ne a tsakanin 1943 zuwa 1948, waɗanda su ne suka narke
suka zama jam’iyyar NPC a shekarar 1951, daga baya kuma wasu suka ɓalle suka kafa
jam’iyyar NEPU. Waɗannan Jam’iyyun da aka samu wato NEPU da NPC su ne suka kasance manyan
jam’iyyun siyasa guda biyu masu hamayya da juna a ƙasar Hausa.
Duk da cewa masana da manazarta sun bayar da
gagarumar gudummawa kuma suka cancanci yabo, amma ba a samu wani aiki na
nazarin ilimi da hannu ya kai kansa wanda aka yi nazarin yarfe daga cikin
rubutaccen zube na Hausa ba. Wannan ne ya sa aka ga dacewar tattauna wannan
batu a cikin wannan takarda domin ganin yadda yake da kuma yadda ake gudanar da
shi a cikin siyasa.
2.0 Bitar Muhimman Kalmomi
A
nan an kawo ma’anonin muhimman kalmomin taken maƙalar ne. Yin hakan zai ba da haske wajen fahimtar inda maƙalar ta dosa da kuma abubuwa da nazarin ya
tattauna a kansu.
2.1 Ma’anar Yarfe[1]
Ƙage da Ƙazafi
kalmomi ne da suke da makusantan ma’anoni da juna ko ma a ce ma’anarsu guda,
sai dai kowacce da asalinta, kuma ana iya amfani da wata a maimakon wata.
Kalmar Ƙage Bahaushiyar kalma ce, tana ajin suna ne mai ɗauke da jinsin namiji. Tana nufin a ce mutum ya yi abin da bai
ji ba, bai gani ba ko kuma a ƙulla masa sharri (CNHN, 2006 sh. 273).
Ƙazafi kuwa kalma ce
da take da asali daga Larabci wato ‘Ƙazaf’, wadda Hausawa suka
ara suka yi mata ƙarin -i a ƙarshenta ta koma ƙazafi. Ma’anar kalmar a Hausa
da Larabci duk abu guda take nufi. Kalmar Ƙazafi suna ne mai ɗauke
da jinsin namiji, kalmar tana nufin laƙa wa mutum laifi ko yi masa sharri
(CNHN, 2006 sh. 279).
Kalmar Yarfe Bahaushiyar kalma ce, tushen
kalmar shi ne [yarf-], da aka yi
mata ɗafin [-a] a ƙarshenta sai ta koma [yárfà] wadda take kalmar aikatau ce mai
ɗauke da karin sautin sama-ƙasa, daga gare ta ne aka samo kalmar [yarfe] bayan an shafe wasalin ƙarshe [-a] aka yi wa tushen kalmar ɗafin [-e] a ƙarshenta, sai ta koma
[yárfé] wanda ya sa karin sautinta
ya sauya zuwa sama-sama maimakon sama-ƙasa a kalmar ‘yarfa’, sai kuma sauyawar
karin sautin ya haifar da sauyawar ajin nahawun kalmar daga aikatau zuwa suna[2].
Ƙamusun CNHN (2006 sh.
479-480) ya bai wa kalmar yarfe ma’anoni guda biyar kamar haka:
i- Maka ko daka
ii- watsa
iii- ƙaga
iv- aika da, musamman
na zagi
v- amfani da hannu
don share wani abu.
Daga cikin waɗannan
ma’anonin, ma’ana ta biyu da ta uku
ne suke da alaƙa kai tsaye da wannan
takardar, domin a ƙarƙashin ma’ana ta biyu an ba da
misali da ‘na watsa masa taɓo’ kuma duk abin da aka
watsa masa taɓo to an ɓata wannan abin, domin zai nuna alamomi a wurare da dama
a jikinsa. Ita ma ma’ana
ta uku daga cikin ma’anonin
an ba da misali ƙarƙashinta
kamar haka: ‘Sun ƙaga masa laifi’. Ke nan kalmar yarfe
tana nufin ƙaga wa wani mutum
wani laifi kamar yadda aka bayyana ta a sama. Idan aka ƙaga wa wani mutum
wani laifi wanda bai ji ba, bai gani ba yakan zubar masa da ƙima ko ya rage masa ƙima a idon mutane.
Idan magoya bayansa ne sai a samu wasu su dawo daga rakiyarsa.
Don haka, kalmar tana
nufin a sanya wani baƙon
abu a jikin wani ta yadda zai iya yin ɗigo-ɗigo a jikinsa har ya fito a gani.
Alal misali, kamar a samu farar tufa a yarfa mata manja ko wani baƙin mai wanɗa zai zama
an ɓata wannan tufar. Manufar yarfe a siyasance ita ce ɓatawa, kamar yadda aka
yarfa wa wannan farar tufar wasu launuka don a ɓata ta.
Kalmomi biyu na farko
wato ‘ƙage’ da ‘ƙazafi’ dukkansu kalmomi ne
da ake amfani da ma’anarsu
a cikin harkokin yau da kullum, kuma in aka yi amfani da su suna iya dacewa da
ko wa aka jefa da su. Akan iya cewa an yi wa wane ƙage, ko an yi wa wane
ƙazafi, amma kalmar
yarfe ta kasance kalma ce da ta keɓanci siyasa. A siyasance ba a cewa an yi wa
mutum ƙage ko ƙazafi, sai dai a ce
an yi masa yarfe[3]. Ke nan, daga
bayanan da suka gabata za a fahimci cewa, kowane yarfe, ƙage ko ƙazafi ne, amma ba
kowane ƙazafi ko ƙage ne yarfe ba.
Yarfe wani yanayi ne
da abokan hulɗar siyasa sukan ɗauko wani abu su ɗora wa wani wanda bai ji ba
bai gani ba don kawai a ɓata shi a siyasance. Yarfe zai iya kasancewa a
tsakanin ‘yan jam’iyya guda masu hamayya da juna, waɗanda sukan ƙirƙiri wani abu su
jingina shi ga wani abokin hulɗar siyasarsu na jam’iyya guda don su
musguna masa. Akan kuma samu yanayin da jam’iyya guda ake, amma
ana ƙarƙashin wani uban gida
na siyasa, sai a yi wa juna yarfe don neman samun gindin zama a wajen iyayen
gidan nasu. A wani gefen kuma yakan iya zama ba jam’iyya guda ‘yan siyasar suke ba,
sai a ƙirƙiri wani abu a jefa
wa abokin hamayya don mutane su dawo daga rakiyarsa, don neman samun nasara a
kan jam’iyyar da ake hamayya
da ita[4].
Alal misali an ga yadda aka riƙa yamaɗiɗi da wani batu da ake cewa wai
‘ɗan takarar
shugabancin Nijeriya a jam’iyyar PDP, Alhaji Atiku Abubakar ya ce,
Allah ba ya karɓar addu’ar
talakawa’. Kuma duk wanda aka
tambaye shi yaushe ya faɗa? A ina ya faɗa? Babu wanda zai iya kawo hujjar
muryarsa, ko hoto mai motsi, ko kuma a rubuce, sai dai a ce kawai haka aka ce.
Wa ya ce? Shi ma a nan sai kuma a fara ‘yan kame-kame. Ma’ana dai yarfe ne aka
yi masa wanda kuma ya yi tasiri ƙwarai a zukatan al’ummar ƙasa. Akwai ire-iren
waɗannan misalai da dama da aka riƙa samu a cikin siyasar jam’iyya, sai dai waɗanda
wannan bincike ya taƙaita
a kansu su ne waɗanda aka samu a cikin rubutaccen zube kaɗai ban da na baka.
A taƙaice, kalmar Yarfe
bisa fahimtar wannan nazarin tana nufin faɗin wani abu da bai tabbata ba, tare
da danganta shi da abokan hamayyar siyasa ko jam’iyyar siyasa ko ɗan siyasa,
wanda zai sa jama’a su ga baƙinsu.
2.2 Tarihi
Kalmar tarihi Balarabiyar
kalma ce wato (At-tarikh) kamar yadda ƙamusun harshen
Larabci Lisan Al-Arab ya bayyana,
wanda yake nufin abubuwan da suka shuɗe. CNHN (2006 sh. 428)
ya bayyana kalmar tarihi da cewa labarin abubuwan da suka wuce.
Ta fuskar ma’ana ta ilimi
kuwa, Carr (1961 sh. 8) ya nuna cewa, tarihi shi ne bin diddigin abubuwa da
suka faru na gaskiya ta hanyar samun tabbas daga masanin tarihi. Ya nuna cewa,
ana samun tabbas a kan labarin da ya shuɗe ne ta hanyar
wanda ya ga abin da ya faru ko ya ji, ko samun kayayyakin tarihi ko rubutaccen
bayani da masana tarihi kan rubuta tare da duba lokaci da bigire da jerantuwar
tunani a kan labarin, da dai sauransu.
Lawal (2018 sh. 47) ya ce,
kafin tarihi ya amsa sunansa na tarihi sai ya cika wasu sharuɗɗa, kamar bayani daga wanda ya ji ko ya gani (oral tradition)
ko samun kayan tarihi (Archaeological source) ko rubutaccen bayani daga masana
tarihi (written decument). Kuma ana la’akari da bigire da lokaci da jerantuwar
tunani a labarin.
Ta la’akari da ma’anonin
da ka kawo a sama, wannan binciken yana da fahimtar cewa, tarihi yana nufin
tabbataccen bayani kan faruwar wani abu a wani ayyanannen lokaci da ya shuɗe. Yana iya kasancewa na baka ko rubutacce.
2.3 Ma’anar Siyasa
An bayyana kalmar siyasa
da cewa, Balarabiyar kalma ce wadda asalinta daga kalmar “saasa” ne, amma
saboda ƙa’idar tasarifi na
nahawun Larabci sai kalmar ta koma “siyaasa”,
wadda take nufin juyawa a kan wani lamari ko kuma yarda da wani ko jiɓintar al’amarin al’umma tare da saninsu ko ba tare da saninsu
ba (Idris, 2016 sh. 49).
A cikin Ƙamusun
CNHN, (2006 sh. 397) an kawo ma’anoni huɗu da suke bayyana siyasa kamar haka:
a. Tafiyar
da al’amuran jama’a ta hanyar neman ra’ayinsu da shawarwari da su.
b. Rangwame,
musamman a ciniki.
c. Dabara
ko wayo.
d. Iya
hulɗa da jama’a.
A ma’ana ta ilimi kuwa,
masana da dama sun bayyana fahimtarsu dangane da ma’anar siyasa, inda suka dubi
kalmar ta fuskoki mabambanta. Daga cikinsu akwai:
A
ra’ayin Mashi, (1986 sh. 16) ya bayyana siyasa ne ta fuskoki uku: Hanya ta
farko ya bayyana ta da ma’anar salo. Sauran hanyoyin kuwa wato ta biyu da ta
uku, ya bayyana siyasa da cewa sulhu ko sauƙi. Waɗannan ma’anoni
da ya bai wa siyasa ba za su rasa nasaba da yadda siyasa ta kasance hanyar
lallashi ko lallaɓa mutane domin
neman goyon bayansu ba. Haka kuma ya kalli siyasa a matsayin yaudara ko ƙarya, saboda yadda ‘yan siyasa kan tsara wani lamari na yaudara domin neman biyan buƙata.
A ra’ayin Funtua, (2003
sh. 19-20) ya nuna siyasa da cewa, ararriyar kalma ce ta Larabci wadda take
nufin sauƙi ko rangwame ko jin ƙai. A da, da zarar
an ce wa mutum ɗan siyasa to ana nufin mutum mai jin ƙai,
kuma mai rangwame, wato dai mutum mai jin tausayin al’umma.
Shi
kuwa Idris,
(2016 sh. 49) ya bayyana siyasa da cewa hanya ce ta tafiyar da mulkin jama’a a
zamanance ko a gargajiyance. Haka kuma dabara ce ta jawo hankalin mutane ta
hanyar karkata ta inda suka sa gaba a kowane fage. Misali idan ɗan siyasa ya lura da abin da
mutane suka fi so,
to shi ma sai ya karkata ta can ko da kuwa da gaske har cikin zuciyarsa ba yana
nufin hakan ne ba.
A
taƙaice dai, idan aka
dubi waɗannan ma’anoni
da aka bai wa siyasa za a iya cewa, siyasa tana nufin neman ra’ayin jama’a ta
hanyar amfani da lafuzza masu daɗi da suka ƙunshi
tausasawa da nuna jin ƙai
da rangwame da ƙarya, domin samun
biyan wata buƙata wadda kan iya
kasancewa ta neman shugabancin al’umma ko cimma wani buri na rayuwa.
3.0 Ra’in Bincike
An
ɗora wannan
bincike a kan Ra’in Tarihanci (Historicism Theory), wanda masanin falsafa Karl
Wilhelm Fredrich Schlegel (1772-1829) ya samar. Masana da manazarta irin su,
Blackburn (1994) da Barry (1995) da Habib (2008) da kuma Lawal (2018) sun ba da
ma’anar tarihanci daidai fahimtarsu kamar haka:
A
fahimtar Blackburn (1994 sh. 167) ya bayyana ma’anar tarihanci hanya ta fahimtar abubuwan
zahiri na zamantakewa ta yadda za a iya bin diddigin faruwarsu da haɓakarsu, domin ba a iya gane abubuwan zahiri na rayuwa, kamar
dimokuraɗiyya ko sassaucin ra’ayi ta la’akari da
yadda suke a yanzu, ba tare da kallon tarihinsu ba. Masanin ya nuna cewa sanin
tarihin abubuwan da suka faru a cikin al’umma musamman abin da ya shafi salon
shugabanci kamar na dimokuraɗiyya ko wasu
ra’ayoyi na rayuwa, ba a iya fahimtarsu ta hanyar duban halin da ake ciki a
yanzu, dole sai an koma ga tarihi.
Shi kuwa Barry (1995 sh. 170)
a tasa fahimtar ya bayyana tarihanci da cewa, wata hanya ce ta ƙulla
alaƙa tsakanin matanin adabi da wanda ba na matani ba,
sau da yawa masu ɗauke da lokacin tarihi iri ɗaya. Ya nuna cewa, a cikin nazarin adabi ta fuskar tarihanci
akan ƙulla alaƙa ne tsakanin
matanin adabi wato rubutaccen adabi da wanda ba rubutacce ba. A nan idan aka
lura za a ga cewa ta hanyar tarihanci ne ake tabbatar da wani abu da ya faru a
cikin tarihi da zamanin da ya faru ta hanyar amfani da matanin adabi.
Habib (2008 sh. 147) a
tasa ma’anar ya bayar da wasu siffofi ne da za a iya tantance tarihanci da su,
inda ya nuna cewa, dole ne a karanci adabi ta muhallin al’adarsa, da sauran
muhallan tattaunawa waɗanda suka kama tun daga
siyasa da addini da ƙawa ko kwalliya, da kuma
tattalin arziƙi. A nan masanin yana nufin idan har za a yi
nazarin adabi ta mahangar tarihanci to wajibi ne a dubi wasu mihimman abubuwa
waɗanda akan tattauna a kansu kamar siyasa da
addini da tattalin arziƙi da sauransu. A wata
ma’ana da Lawal (2018 sh. 34) ya kawo, ya ce, tarihanci
yana nufin duba yadda al’amuran tarihi suke a cikin matanin adabi ta hanyar
la’akari da rubutaccen tarihi domin samun tabbas.
Ke
nan, idan aka dubi waɗannan
ma’anonin da aka kawo sama za a iya cewa tarihanci ba wani abu ba ne illa,
nazarin wasu al’amuran da suka shafi rayuwa waɗanda suka danganci al’ada da addini da siyasa da tattalin arziƙi da sauran gwagwarmayar rayuwa a cikin matanin
adabi ko ba na matani ba ta hanyar duba zuwa ga ingantaccen tarihi.
An
fara amfani da ra’in tarihanci ne tun a ƙarni na 18. Ra’in
yana bayani ne a kan yadda tarihi yake bayyana hanyoyi da tsarin rayuwar al’umma. Haka kuma, yana bayyana yadda wasu al’amurra suka faru a cikin wani zamani, da irin ci
gaban da aka samu cikin al’adu na can dauri da kuma bayanin wurin zaman wata al’umma.
George
Hegel (1770- 1831) yana ganin cewa tabbatuwar ‘yancin ɗan Adam shi ne maƙasudin adana tarihi, wanda kuma hakan kan samu ne kaɗai ta hanyar samar da
tabbatacciyar ƙasa. A ganin wannan
masani, sanin abin da ya faru a baya shi ne yake ba da damar rayuwa cikin ‘yanci da fita daga ƙangin bauta, domin yakan ba da damar fahimtar inda aka fito don a ƙara ɗaura ɗamara zuwa
inda aka dosa.
Ƙarƙashin wannan ra’in an sake samun wani sabon tunani a wuraren
shekarun 1980 da aka kira shi da suna “Sabon Tarihanci” wanda
wani Ba’amirke matarki mai suna Stephen Greenblatt ya samar a shekara ta
(1980). Greenblatt ya samar da Sabon Ra’in Tarihanci ne a sakamakon wasu
nazarce-nazarce da ya gudanar, sai aka buƙaci ya tattara
ayyukan ya nazarce su ta fuskar wani ra’i na musamman, sai
ya samar da wannan ra’i da ya kira Sabon
Tarihanci “New Historicism” a shekarar 1980.
(Lawal ,2018 sh. 35).
Nazari ta mahangar ra’in
tarihanci, shi ne dubi zuwa ga al’amura na tarihi a cikin adabi ta hanyar
danganta wannan adabin zuwa ga tarihi na haƙiƙa
daga masana tarihi, kuma wannan tarihin ya kasance tabbatace ta sigar rubutu.
Greenblatt
(1980 sh. 47) ya tabbatar cewa, tarihanci yana ɗauke da manyan ginshiƙai ko tubala guda biyu da ake dubawa a wajen
tarken adabi. Ga su kamar haka:
a. Matsayin
Tarihi a Cikin Matani(Historisity of a Text)
b. Sahihancin
Tarihi a Rubutaccen Labari(Textuality of history)
Ke nan, a duk lokacin da ake tarken adabi ta
mahangar tarihanci, sai an dubi yadda adabin yake ɗauke da zantuttuka na tarihi a cikinsa, wato yadda
aka gina zantuttukan tarihi da nuna su a bisa tarihin na gaskiya. Na biyun
kuwa, shi ne a nazarci yadda labarai ko bayanai da aka rubuta suke ɗauke da tarihin da su marubutan suka sarrafa da
irin sahihancin wannan tarihin daga tunanin marubutan, wato ya kasance
tabbatacce ne ta sigar bayar da labari. A ƙarƙashin waɗannan
manyan tubala guda biyu ne ake tarken adabi ta mahangar ra’in tarihanci kamar
yadda Greenblatt (1980 sh. 47) ya bayyana.
Idan aka dubi ra’in da
kyau za a fahimci cewa, da farko an kira shi tarihanci ne kawai, sai bayan
tatttara ayyukan da Greenblatt ya yi ne ya sake nazarinsu bisa ra’in na
tarihanci sai ya kira su “Sabon Tarihanci”.
Dangane da bambanci
tsakanin Tarihanci da Sabon Tarihanci kuwa, Habib (2008 sh. 147) ya ce, mafi
yawan abubuwan da suka gabata a ƙarƙashin
jagorancin “Sabon Tarihanci” ba wani sabon abu
ba ne, sai dai za a iya cewa yana wakiltar salon nazari da bunƙasar
tarihanci na gargajiya da ya gabata ne. Idan aka lura za a fahimci cewa, Sabon
Tarihanci ba wani sabon abu ne na daban ba, sai dai za a iya cewa Sabon
Tarihanci ci gaban Tsohon Tarihanci ne kawai, domin duk manufarsu ɗaya ce a fagen nazari.
Mabiya
wannan mazahaba sun haɗa
da: Louiz Montrose da Michael de Montaigne da G. B. Vico da George Hegel. Wasu daga cikin
nazarce-nazarce na adabin Hausa da aka gudanar ta mahangar ra’in tarihanci sun
haɗa da: Usman (2016) da Yusuf
(2018) da Lawal (2018) da Bunza (2018) da Ali (2020)
Wannan
ne ya sa aka ga dacewar zaɓen wannan ra’in domin ɗora shi a kan wannan takarda, kasancewar tana bayani ne kan abin da ya
shafi yadda abokan hamayyar siyasa suka riƙa amfani da yarfe a cikin tarihin siyasar ƙasar Hausa, wanda ya fito a cikin rubutaccen zube na Hausa.
4.0 Nazarin Yarfe a Siyasar Ƙasar Hausa
Jam’iyyun siyasa sun
shahara ƙwarai wajen yi wa
juna yarfe, kasancewar kowacce tana so ta ɗaukaka a kan abokiyar hamayyarta,
wannan ya sa abokan hamayyar siyasa sukan riƙa ƙaga aibu ga
‘yan’uwansu suna faɗa wa jama’a don su guje su, ko da kuwa daga baya za a
fahimci cewa wannan abin da aka danganta jam’iyyar ko ɗan siyasar da shi ba
gaskiya ba ne.
A lokacin da aka fara
siyasar jam’iyyu a ƙasar
Hausa, jam’iyyu biyu ne aka kafa
a ƙasar Hausa kuma suka
yi tashe, sannan kuma dukkansu sun yi gwagwarmayar neman mulki, inda ɗaya ta yi
nasara, ɗaya kuma ta zama jam’iyyar hamayya. Al’adar siyasa ce dole
in za a tallata jam’iyya ko ɗan takara, bayan an yi amfani da yabon abin da ake
tallatawa, wajen faɗin ingancinsa, sai kuma a kushe abokin haɗinsa ko abokin
hamayyarsa domin a sake fito da hasken abin da ake tallatawa ya fito fili,
al’umma su karɓe shi, su kuma guji wanda ba shi ba. A wurin wannan kushen ne
ake samun yarfe ga jam’iyyun siyasa.
Tun daga jamhuriya ta
farko an riƙa samun irin waɗannan
bayanai a cikin rubutaccen zuben Hausa, inda jam’iyyu biyu masu hamayya suka yi
ta yi wa juna yarfe a tsakaninsu. A wasu lokutan ma ba tsakanin jam’iyyun kaɗai
yake tsayawa ba, har ma da ‘yan jam’iyya, inda akan kama
suna, wani lokaci kuma sai dai a yi ishara. Jam’iyyar NEPU da Jam’iyyar NPC sun
yi suna wajen irin wannan siyasar, wadda za a iya cewa daga gare su ne tsarin
siyasar jam’iyya ya ginu a ƙasar Hausa. Irin waɗannan misalai na
yarfe sun fito a cikin rubutaccen zube na Hausa, waɗanda suka yi nuni da irin
wainar da aka toya a fagen siyasar Jam’iyyu a wancan lokacin. Daga bisani, an
ci gaba da samun yarfe a cikin rubutattun ayyukan zuben Hausa waɗanda suka ci
gaba da fito da hoton yadda siyasar jam’iyyu ta gudana har zuwa yau.
Dangane da wannan
nazarin an raba yarfen siyasa zuwa gida uku, sannan an ɗauki kowanne an yi
bayaninsa tare da misalan da suka dace kamar haka:
1. Yarfe
na addini
2. Yarfe
na ƙima/halaye
3. Yarfe
na tafiyar da shugabanci
4.1 Yarfe Na Addini
Kalmar addini tana
nufin hanyar bauta wa Ubangiji (CNHN, 2006 sh. 3). A mana ta ilimi kuwa, Farouk
(2006 sh. 49) ya nuna cewa, kalmar addini ararriyar kalma ce daga Larabci,
wadda take nufin hanyar da ɗan Adam yake dogara a gare ta domin bauta wa
mahalicci da kuma bin hukunce-hukuncen shari’a domin kwaɗayin
kyakkyawar sakamako duniya da lahira.
Shi kuwa Muhammad
(2006 sh. 6) ya ce, addini yana nufin yadda mutum ya fifita wani abu, ya kuma
bauta masa, ko dai suna ganinsa ko kuma ba su ganin sa. Ɗan Alhaji (2006 sh. 17)
ya nuna cewa, addini wata babbar hanya ce da ɗan Adam yakan bi domin ganawa da
ubangijinsa, yarda da shi da muƙa wuya a gare shi da kuma kiyaye ƙa’idoji da kuma dokokin
wannan hanya kamar yadda Allah ya shimfiɗa. Idris (2010 sh. 7) ya bayyana
addini da cewa, hanyar bauta ce da yarda da Allah a bauta masa ta yin abin da
ya ce da barin abin da ya ce a bari. Haka kuma Hanya ce ta bauta wa wani abu saɓanin
Allah don neman biyan buƙata.
A fahimtar wannan
takarda, addini hanyar rayuwa ce ta ɗan Adam, wadda ake bi ta hanyar yarda da
saudaukar da kai da kuma bauta domin samun biyan buƙata ko kariya ko kuma
tsira a gaban Ubangiji. A siyasance addini yana taka muhimmiyar rawa wajen
neman shugabanci da kuma tafiyar da shi, kasancewar shi ne hanyar rayuwar da
‘yan Adam suke bi kuma suka amince da shi. Ita kuwa siyasa ta kasance ginshiƙi a rayuwar ɗan adam
wadda yake gudanar da ita da saninsa ko ba da saninsa ba. Wannan ya sa ‘yan siyasa suka riƙa amfani da addini
wajen cimma burikansu na siyasa ta fuskoki da dama.
Yarfen siyasa yana
daga cikin abubuwan da aka riƙa amfani da addini wajen gudanar da
shi, inda aka riƙa amfani da wasu
abubuwa na addini domin daƙile tafiyar abokan hamayya. Kasancewar
addini yana da tasiri ƙwarai
a wajen masu shi ko mabiyansa akan samu wasu ‘yan siyasa su yi
amfani da shi wajen shafa wa abokan hamayya wani mummunan abu wanda zai sa a ga
baƙinsu, a ƙyamace su.
Tarihi ya nuna cewa
‘yan siyasa sun riƙa
yi wa abokan hamayyarsu yarfe ta hanyar amafani da addini kamar yadda Paden (1973 sh. 122) ya kawo bayanai a kan irin
rikice-rikicen da aka riƙa samu a tsakanin mabiya aƙidun Tijjaniyya da Ƙadiriyya har suka riƙa yi wa juna yarfe
kamar haka:
The Sultan of Sakkwato later denied that the riot was between Qadiriyya
and Tijaniya, throughout the country and more especially in big towns, live
amicably without interference in each other’s religious belief. He referred to
the rioters as ‘Yan Wazifa’ who are going beyond their bounds... to them even
prayer five time a day was forbidden.
Fassarar marubuci:
Sarkin Musulmi ya ƙaryata batun rikicin da ya faru tsakanin Tijjaniyya da Ƙadiriyya, waɗanda suke zaune lafiya a duk faɗin ƙasar musamman ma a manyan garuruwa, inda ya bayyana cewa waɗansu masu
neman wuce gona da iri ne; masu cewa sallah biyar a wuni haramun ne, waɗanda
ake kira ‘yan wazifa
suka tayar da rikicin.
A farkon kafuwar
siyasar jam’iyyu aƙidun
Addinin Musulunci sun taka muhimmayar rawa a a cikin siyasar ƙasar Hausa, duk kuwa
da cewa shaihunnan waɗannan ɗariƙu ba ‘yan siyasa ne ba,
kuma ba su da alaƙa da ita, amma an yi
amfani da darajarsu da na aƙidunsu a cikin siyasar wancan lokacin,
inda suka kasance tamkar ma su ne jam’iyyun a karon farko. Idan aka yi la’akari da magoya bayan
kowace jam’iyya za a ga cewa
akasarinsu mabiya aƙida
guda ne, duk da cewa akan samu wasu ‘yan kaɗan da suke da bambancin aƙidar. Alal misali,
Jam’iyyar NPC ta su Ahmadu Bello Sardauna kaso mafi tsoka na mabiyanta ‘yan Ƙadiriyya ne, haka ma
dukkan manyan masarautun ƙasar Hausa ɗariƙar Ƙadiriyya suke bi in
ban da fadar Kano a wancan lokacin zamanin Sarki Abdullahi Bayero wanda shi
mabiyin ɗariƙar Tijjaniyya ne[5].
Ita kuwa jam’iyyar NEPU ta su Malam Aminu Kano mafi yawa na mabiyanta a wancan
lokacin ‘yan Tijjaniyya ne. Wannan dalilin ne ya sa ko da aka riƙa samun rikice-rikice
tsakanin aƙidun biyu sai aka riƙa danganta shi da
siyasa.[6]
Dangantakar siyasar da take tsakanin aƙidun biyu ya sanya suka riƙa yi wa juna yarfen
siyasa a tsakaninsu.
Idan aka dubi bayanin
da yake sama za a fahimci cewa, kasancewar Sarkin Musulmi Baƙadire kuma a wancan
lokacin dukkan sarakuna suna goyon bayan jam’iyyar NPC ne, wannan
ya sa ya yi wa ‘yan NEPU waɗanda suke
‘yan Tijjaniyya ne
galibinsu yarfe da cewa sun ce sallah biyar a wuni haramun ne kamar yadda
misalin ya nuna. Duk da cewa a cikin bayaninsa bai fito ƙarara ya ce ‘yan Tijjaniyya ba,
amma ya yi amfani da kalmar “Yan Wazifa” wadda kalma ce ta ƙasƙanci da ake faɗa wa ‘yan Tijjaniyya a
wajen Lardin Kano[7]. Idan aka duba
za a ga cewa wannan yarfe ne na addini domin kuwa ‘yan Tijjaniyya ba su haramta
sallah ba, sai dai kawai za a ga hakan a matsayin wanin salo ne na rage wa aƙidar da ma mabiyanta
magoya baya waɗanda suka kasance ‘yan NEPU a wancan lokacin domin raunana
siyasarta.
Irin wannan ya ci
gaba da bayyana a cikin ayyukan adabin Hausa na zube, inda ‘yan siyasa suka riƙa yi wa abokan hamayyarsu
yarfe don mabiya su ji cewa jam’iyyar da suke bi ba ta cancanci su bi ta ba.
Galibi a siyasa irin waɗannan abubuwa da akan yi yarfe da su ƙaga su ake yi ba tare
an ji ko an gani ba, abin nufi babu tabbas a faruwarsu. Alal misali, jamiyyar
NPC ta ce jam’iyyar NEPU jam’iyyar kafirai ce, don
ɗabi’unsu irin na Kirista
ne. Dubi abin da suka ce:
... tsakanin ‘yan NPC da na NEPU waɗanne
ne ɗabi’arsu irin ta Kirista ce? Har wasu daga
cikinsu sukan ce ba sa bin addinin Musulunci? (Nadabo, 1960).
Duk da cewa tambaya
ce aka yi, amma dai ta sigar yarfe ce aka yi ta domin dai amsar a ƙarshe za ta faɗa kan
NEPU ne, domin kuwa ‘yan
NPC ne suke tambayar, kuma a jaridar gwamnati wadda ba a sanya bayanan ‘yan hamayya
a cikinta, balle kuma abin da ya shafi yarfe. Idan aka duba a cikin wannan
misali za a ga cewa an yi wa ‘yan hamayya ne yarfe cewa ɗabi’unsu irin na
Kiristoci ne, wanda an san dai cewa kaso mafi tsoka na al’ummar ƙasar Hausa Musulmi
ne, kuma addinin Kirista yana takin saƙa ne da na Musulunci. Wannan ya sa ‘yan jam’iyyar NPC
suke ganin idan suka jefi NEPU da mummunar kalma irin wannan zai haifar masu da
koma-baya. Haka kuma ba wai ɗabi’unsu ne kaɗai irin nan Kirista ba,
domin ana iya samun wani Musulmi mai yin wasu ɗabi’u irin na Kirista,
sai suka ƙara masu da cewa ai
wasu ma daga cikin ‘yan
hamayya sukan ce su ba Musulmi ba ne, wato dai sun ma yi ridda, sun bar addinin
Musulunci ke nan. Idan aka duba za a ga cewa wannan ba ƙaramar magana ba ce,
domin kuwa jifar ‘yan jam’iyya da kafirci ba ƙaramin illata jam’iyyar zai yi ba don
al’ummar ƙasar Hausa akasarinta
Musulmi ne.
Kamar
yadda ‘yan NPC suka riƙa nuna cewa, jam’iyyar NEPU jam’iyya ce ta kafirai maƙiya addini, su ma NEPU sun yi amfani da wannan yarfen ta
hanyar nuna cewa shiga jam’iyyar NPC ko AG tamkar shiga kafirci ne, kamar dai yadda
wannan misalin ya nuna:
...domin ni har abada ba zani shiga AG
ko NPC ko wata jam’iyya ba illa NEPU wadda na dade kuma nake ciki a yanzu.
Domin shiga NPC ko AG shiga uku ne, saboda haka Allah ya tsari Musulmi da shiga
waɗannan jam’iyyu... (Alasan, 1961).
Wannan misalin ya
nuna cewa duk jam’iyyar da ba NEPU ba to shigar ta tamkar shiga uku ne. Idan
aka ce mutum ya shiga uku kuwa ana nufin ya shiga masifa da bala’i ke nan. Babu
kuwa wata masifar da ta kai kafirci, wannan ya sa a cikin misalin da yake sama aka
ƙarasa da addu’ar neman tsarin duk
wani Musulmi da shiga Jam’iyyar NPC da AG, wato duk Musulmi bai
kamata ya shiga jam’iyyun
ba, to wanda ya shiga fa? Ke nan, ba Musulmi ne shi ba.
A siyasance, idan aka
lura cewa mutum yana da muhimmanci a cikin tafiyar wata jam’iyya to za a yi duk
yadda za a yi domin karkato hankalinsa don ya bi wata jam’iyyar da ba ita ba,
kuma kowace jam’iyya za ta so ya kasance a cikinta domin irin amfanin da zai
jawo mata. Idan aka bi duk hanyar da za a bi domin raba shi da jam’iyyar da
yake ba a yi nasara ba, sai kuma a nemi hanyar da za a ɓata shi don dai a yi
irin abin nan da ake cewa a fasa kowa ya rasa, wato a bi shi da yarfe don a
karya lagon siyasarsa. Irin wannan ne ya faru da Hassan a cikin littafin Tura Ta Kai Bango, inda abokan hamayya
na jam’iyyar hamayya suka yi masa yarfe cewa ya shiga jam’iyyar kafirai. Dubi
misalin da yake a ƙasa:
Eh to lafiya, amma ba lau ba. Hassan ne na ga yana neman ya shiga hanya
ta Allah wadai, wadda sharrinta ba shi kaɗai zai shafa ba, har da danginsa da
mutanen gari. A taƙaice dai
yana neman kawo jam’iyyar siyasa ce ta kahurai a nan garin.’
‘Kahurai ɗan nan?’
‘Kahurai Inna! Mu kuma muna ganin yadda mai gidan nan ya nuna masa
hanyar makaranta bai kamata ba a ce karatun da ya yi ya zo ya tafi a banza ke
nan. (Katsina,
1983 sh. 43-44)
A wannan misalin idan
aka duba za a ga cewa, magoya bayan jam’iyyar Riƙau ne suka tafi suka
samu mahaifiyar Hassan suka ce ai jam’iyyar da su Hassan ɗin suke son kawowa
garinsu jam’iyya ce ta kafirai,
kuma yana neman shiga. Wannan ya sa hankalin mahaifiyarsa ya tashi don ta ji
zancen cewa ɗanta zai shiga mummunar hanyar da ba shi kaɗai sharrinta zai shafa
ba har da danginsa da sauran mutanen gari. Domin Hassan ɗan gidan
malamai ne, kuma ya samu tarbiyya irin ta malanta bai kamata a ji shi ya shiga
irin wannan hanya ba. Idan aka duba za a ga cewa yarfe ne aka yi wa Hassan na
addini, inda aka danganta jam’iyyarsa da ta kafirai don kawai a ɓata
shi a wajen mahaifiyarsa don ta hana shi bin jam’iyyarsa ta Sauyi.
Kasancewar
al’ummar Hausawa suna girmama shugabanninsu matuƙa, wannan bai sa sun
girmama wani sha’ani na siyasa fiye da addini ba. Hakan
ya sa abokan hamayyar siyasa, musamman na jam’iyyar
hamayya ta NEPU suka riƙa amfani da wannan wajen yi wa magoya
bayan NPC yarfe ta hanyar nuna cewa ai sun fi girmama Sardauna da shugabanninsu
na siyasa fiye da Ubangiji. Sun nuna cewa yadda suke tsoron Sardauna ba su jin
tsoron Allah haka. Dubi dai abin da suke cewa a cikin wannan misalin:
Kai wawa, jahili, daƙiƙi, sususu, bari in gaya
maka duk cikin Shari’ar Islama ba inda aka ce a nuna bambanci, ba inda aka ce a bada kuɗi
don neman galaba, ba inda aka ce a girmama Sardauna a wulaƙanta gyartai. In kuwa
akwai, ka gaya mani ayar da ta ce a yi kukan masallaci na ƙarya don jin daɗin
Sardauna da jam’iyyarsa... (“Addinin
Musulunci a Mazahabar Maliki”, 1960).
Idan
aka dubi wannan misalin da yake sama za a fahimci cewa, mayar da martani ne aka
yi ga kalaman abokin hamayya. A cikin wannan martanin an yi wa shugabannin
jam’iyyar NPC yarfe ta hanyar ƙaga masu wasu batutuwa munana da kuma danganta su da su
ba tare da ƙwaƙƙwarar hujja ba. A cikin
misalin an nuna cewa ‘yan NPC suna aikata wasu abubuwa na addini ne domin ganin
idon Sardauna ko don su faranta masa. Misali, ɗaukaka Sardauna saboda samun duniya da
wulaƙanta
talaka. Haka kuma an nuna cewa suna yin kuka a masallaci ne ba don tsoron Allah
da ya cika zuciyarsu ba, sai don Sardauna da jam’iyyarsa su ji daɗi.
Idan
aka dubi waɗannan bayanan da misalan da aka kawo za a fahimci cewa, ‘yan siyasa suna
amfani da addini wajen yi wa abokan hamayya yarfe domin nuna wa al’umma cewa ba
su cancanci a bi su ba.
4.2 Yarfe Na Ƙima/Halaye
Ƙima yana nufin hali
na ban girma (CNHN, 2006 sh. 244). A siyasa ana la’akari da halaye da ɗabi’un ‘yan siyasa wanda dole
ne a zahiri su kasance na ƙwarai domin magoya bayansu samu dalili
da ƙwarin guiwar goya
masu baya da kuma tallata su domin zaɓensu. Samun ‘yan siyasa da wasu
munanan ɗabi’u ko wasu miyagun
halaye ko tarihin wani abin kunya yakan sa a yi wa jam’iyyarsu suka da
mummunar shaida ta hanyar danganta su da wannan halin wanda zai iya raunana
farin jinin jam’iyyar ga magoya
bayanta.
A cikin tarihin
ginuwar siyasa an riƙa
samun inda ‘yan siyasa suka riƙa yi wa abokan
hamayyarsu yarfe don nuna cewa ba su da halin kirki, ko kuma ba za a samu wani
abin kirki da al’umma za ta amfana ba
in aka zaɓe su. Alal misali, a cikin jaridar Sodangi an ga inda aka yi wa jam’iyyar NEPU yarfe da cewa cuta take
yaɗa wa magoya bayanta kamar haka:
...amma NEPU ta zama tunku da ƙararrawa mai jawowa dangi cuta koyaushe, ita ko kujera ɗaya ba za ta
samu ba, sai ta koma Kudu wajen Enugu ko ta lasa a can. (“A.G. Na Maganin
Mutuwa a Arewa”, 1959).
A nan ɗaya daga cikin
magoya bayan NPC ne yake nuna cewa Jam’iyyar NEPU babu alheri tattare da ita,
inda ya kwatanta jam’iyya
da wani dabba mai suna tunku, wanda ya ce ba ya kawo wa ‘yan’uwansa alheri,
kullum sai sharri. Don haka magoya bayan jam’iyyar ba za su samu wani alfanu
daga gare ta ba sai dai cutuwa da za su yi. Ya nuna cewa ba za ta samu ko
kujera ɗaya ba a Arewa idan aka yi zaɓe, sai dai ta koma Kudu ko za ta samu a
can. Idan aka dubi yadda ya nuna cewa Jam’iyyar NEPU tana yaɗa wa ‘ya’yanta cuta za a fahimci
cewa lallai yarfe ne ya yi wa jam’iyyar ta hanyar amfani da wani hali mummuna
na yaɗa cuta, don dusashe haskenta ga mogoya bayanta. Duk da cewa babu wanda
aka ji cewa jam’iyyar ta sa masa wata cuta ko kuma ta jawo masa wani sharri,
illa dai ya ƙaga zancen ne don ya
sanya wa jama’a shakku a kanta.
A wasu lokuta akan
nemi abin da za a shafa wa ɗan siyasa domin ya zubar masa da mutunci a idon a
jama’a. Irin wannan ya
bayyana a cikin littafin Dambarwar Siyasa
kamar haka:
Ganin cewa haƙarsu ba ta
cim ma ruwa ba... sai suka ƙudurci ko ta wane fanni sai sun dakushe farin jinin Farfesa tare da
zubar masa da mutunci a idon jama’a. Ranar wata Lahadi tarkonsu ya kama kurciya, domin a ranar ne suka
samu nasarar shigar da wata yarinya ‘ya shekara goma sha biyu cikin gidan gonar Farfesan, a daidai lokacin
da ya je duba wani aiki da aka gudanar. Bayan ‘yan iskan sun yi mata rubdugun fyaɗe, sai suka lallaɓa suka sulale ba
tare da wani ya gan su ba, tare da yada ta a bakin hanyar shiga da fita ta
gidan gonar. Tun daga nesa Farfesan ya hango ta a yashe, cikin hanzari ya yunƙura da niyyar kai mata agaji, tabbacin da ya samu tana da sauran
numfashi a jikinta ya sa ya yunƙura tare da cicciɓar ta da niyyar sa ta a mota ya kai ta asibiti, a
daidai wannan lokacin ‘yan sanda suna zuwa. Abin ka da ture, take suka zargi Farfesa da aikata
wannan aika-aika. (Aminiya-Trust, 2021 sh. 41).
A cikin wannan
misalin za a fahimci cewa yarfe ne aka shirya wa Farfesa a matsayinsa na mutum
mai gaskiya da riƙon amana da kuma
mutunci a cikin al’umma
wanda gaskiya da mutunci suka sanya jama’a suke ƙaunarsa, kuma suka
tsayar da shi takarar gwamna a wata jam’iyya, inda ‘yan hamayya suka
lashi takobin ko ta halin ƙaƙa sai sun tabbatar bai kai labari ba.
Bayan tsallake dukkan makirce-makircen da aka riƙa ƙulla masa ne aka yi
tunanin a shirya masa yarfen da zai taɓa mutuncinsa ya sa al’umma su dawo daga
rakiyarsa. Idan aka duba za a ga cewa, fyaɗe mummunan abu ne a cikin al’umma, wannan ya sa
aka danganta ɗan takarar da shi ta hanyar jefar da yarinyar a bakin gidan
gonarsa, kuma aka jira sai da ya zo inda take aka ce ana zargin shi ya yi mata.
Irin wannan yakan faru a cikin siyasa, inda za ka ji an zargi wani ɗan takara
da yi wa wata cikin shege, ko wani makamanci haka, a yaɗa don a sanya masa baƙin jini a cikin al’umma. Irin wannan ya
fito a cikin jaridar Gaskiya Ta fi Kwabo
wadda ta ruwaito wani yarfe da aka yi wa mataimakin shugaban ƙasa a jamhuriya ta
biyu cewa ya yi wa wata mata cikin shege kamar haka:
Wata mujallar kasar nan mai suna ‘The
Week’ ta taɓa buga wani labari, inda ta nuna cewa, wata
matar aure ta shaida wa kotu cewa Alex Ekwueme ne ya yi mata ciki har Allah ya
sa ta sami ƙaruwa...
Amma shi Ekwueme ya ce abin da Adeline ta fada karya ne kuma bata suna ne. (“Ekwueme zai ba mu
kunya”, 1999).
Alex Ekwueme shi ne
mataimakin shugaban ƙasa
a jamhuriya ta biya, kuma shi ne aka yi wa wannan yarfen a lokacin ana
shirye-shiryen sake zaɓen su a karo na biyu a shekarar 1983. Wata matar aure ce
mai suna Adeline ta yi iƙirarin cewa shi ne ya yi mata cikin
shege har ta haifi ‘ya’ya biyu, inda shi
kuma ya ƙaryata. Ya nuna cewa
abin da ta faɗa ba shi da tushe, hasali ma yarfe ne kawai aka masa domin a ɓata
masa suna.
Sau da dama an sha
zargin ‘yan NEPU da tsaurin ido ga mahukunta, kasancewar sun yi imani cewa
mahukunta suna danne masu haƙƙoƙinsu. Wannan ya sa duk yadda suka juya
ko suka furta wani abu ‘yan
NPC sukan ɗauke shi a matsayin tsageranci ne maimakon neman haƙƙi. A wata wasiƙa da aka samu a
jaridar Sodangi an nuna yadda ‘yan
jam’iyyar NPC suke jingina wa ‘yan NEPU rashin tarbiyya, inda har a cikin wasiƙar ya kira ‘yan NEPU da cewa sun
raina iyayensu. Dubi wannan misalin:
Ina so Edita ka ban ɗan fili don in bayyana rashin tarbiyyar NEPU. Abin
mamaki, don wanda ya ce mahaifinsa ma ba kowa ba ne, ina ga wani? Kwanan baya
ne can, ranar da suka yi lacca a Tudun Wada, sun taso suna komowa gida... suna
ta ƙetare babban
titi babu tunanin komai, sai ga wata mota ta ɓillo daga Airport. A nan suka
dinga yi wa mai motar tsawa tun yana nesa, wai ya tsaya sai Firimiya ya wuce
wato Malam Aminu Kano... bayan wucewar wannan direba sai wasu jakan ‘yan NEPU suka bi shi da zagi. Wannan kuwa rashin tarbiyya a fili ke
nan. (“Lallai
Babu Tarbiyya”, 1957).
A cikin wannan misalin, an nuna yarfe ne inda
aka bayyana cewa ‘yan NEPU ba su da tarbiyya. An sani cewa tarbiyya muhimmin
abu ne a rayuwar Hausawa, kuma duk wanda ya rasa ta ana yi masa masa kallon
mutumin banza maras ƙima
da daraja a idon mutane. Haka kuma duk wanda ya rasa tarbiyya ana kallon sa a
matsayin wanda ba ya ganin mutuncin kowa. Wannan ya sa a cikin misalin bayan
marasa tarbiyya da aka kira su, sai kuma aka ce sun raina iyayensu, in kuwa
hakan ta kasance to ke nan babu wani mai sauran mutunci a idonsu. Da wannan
‘yan NPC suka riƙa nuna wa al’umma cewa magoya
bayan NEPU tsageru ne marasa kunya da mutunci, don haka kada a bi su ko kuma a
goya masu baya.
Daga cikin yarfe na ƙima wani lokaci akan
danganta shi da wani makusancin ɗan jam’iyya, wanda ake ganin zai iya shafar su
har ya yi tasiri a cikin siyasarsu. Alal misali, wani ɗan siyasa wanda yake
tsohon shugaban ƙaramar hukuma ne, a
lokacin da yake neman kujerar ƙaramar hukuma an yi masa yarfe da cewa
mahifinsa ɓarawon keke ne lokacin yana matashi, don haka ba za a zaɓi wanda
yake da gadon sata ba, bayan kuwa hakan bai taɓa faruwa ba.[8]
Irin wannan yarfen ya yi kama da wanda aka nuna a cikin littafin Tura Ta kai Bango kamar haka:
Ni ai da ma na san wannan yaron bai gaji arziƙi ba. Ubansa fa
Na-Torami har ya mutu itace yake sarowa yana sayarwa. Kwana bakwai ma kafin ya
mutu, sai da na sa shi ya kawo min kai uku har gida... Wani ya ce, Yo shi kansa
Garban fa? Ubansa ba mahauci ba ne, karen lahira? (Katsina, 1983 sh. 21-22)
A
cikin wannan misalin ana an yi wa ‘yan jam’iyyar Sauyi ne yarfe cewa talakawa
ne ‘ya’yan matsiyata ba su da komai, duk da cewa suna da jama’a kuma sun zamar
wa jam’iyyar Riƙau ƙadangaren bakin tulu. An nuna
cewa ai Hassan mahaifinsa sana’ar saro itace yake zuwa ya yi, ya zo gari ya sayar. Shi
kuwa Garba an ce wai mahaifinsa mahauci ne karen lahira. Irin waɗannan abubuwan akan
samu duk yarfe ne don jama’a su ɗauka cewa ai ba wata ƙima suke da ita a cikin al’umma ba. Bayan kuwa
babu ruwan shugabancin siyasa da arziƙinsu matuƙar dai sun cancanta, amma sai a yi amfani da ƙimarsu a yi masu yarfe da
shi.
Yana daga cikin yarfe
a jingina wa mutum wani mummunan aiki wanda bai aikata ba, ko kuma ya aikata
sai a yi ƙoƙarin danganta
mummunar aikinsa ga wasu don a nuna cewa duk haka suke ko kuma halinsu guda.
Wannan ya yi daidai da wani misali da aka samu a cikin jaridar Sodangi wanda aka yanke wa wani ɓarawon
agwagi shekara ɗaya a gidan yari. Dubi misalin:
Mai shari’a ya sami Gambo da laifin satar agwagi bayan an tambaye shi
(Gambo) ya tabbatarwa da shari’a...sai mai shari’a ya yanke masa hukunci da
shekara ɗaya. Har wa yau dai ashe a jikin rigar mutumin nan a gaba da baya duk
tauraro ne a jikinta... To wannan abin kunya ko lallai ya kai a ce da mai
shari’a an ji kunya ko ba ita a ce dai mai riga da tauraro ya sato agwagi... (Mohamed, 1960).
An tuhumi wani mai
suna Gambo da satar agwagi, kuma an same shi da laifi. A matsayinsa na wanda
aka samu da laifin sata, sai kawai aka yanke masa hukunci daidai da laifin da
ya aikata. Bayan haka sai aka lura cewa, a jikin rigar ɓarawon akwai hoton
tauraro wanda yake alama ce ta jam’iyyar NEPU, sai aka nuna cewa ai ɓarawon
nan ɗan NEPU ne, don haka sai ‘yan NPC suka ce ‘yan NEPU su faɗa wa mai shari’a sun ji kunya. In
kuwa ba su da kunya to su faɗi cewa an kama mai riga da alamar tauraro ya saci
agwagi. Wannan shi ma zai iya kasancewa yarfe ne kawai irin na siyasa, domin
kuwa da ganin tauraro a jikin rigar ɓarawo ba zai tabbatar cewa shi ɗan NEPU ne
ba, don yana iya kasancewa ma rigar sato ta ya yi a wani wuri ya sanya ta ba
tare da la’akari da alamar da
take jikinta ko na wace jam’iyya ce ba. Don an kama wani ɗan jam’iyya da laifi ba shi
yake nuna cewa duk ‘yan jam’iyyar ne suka yi laifin ba, hasali ma su laifin bai
shafe su ba.
Wani misalin yarfe na
halaye shi ne, yadda za ka ga wata jam’iyya tana faɗin miyagun maganganu a kan
wata, inda za ta riƙa
danganta ta da munanan halaye kamar su hassada da ƙarya da cin amana da
dai sauransu. A wannan misalin da yake ƙasa an samu irin wannan:
...Ofishin ba da labarai na jam’iyyar NEPU ya Zargi Jam’iyyar NPC a kan
sunan nan da ta yi na irin halin nan nata na hassada a kan maganar da awolowo
ya yi cewa babu irin mulkin da ya fi dacewa da Nigeria illa na jamhuriya. (Bai
Kyautu NPC Ta Soki Maganar Da Awolowo Yayi Ba, 1961).
A cikin wannan
Misalin NEPU ta siffanta jam’iyyar NPC da ɗabi’ar hassada, inda ta
nuna cewa da ma halin jam’iyyar ne, domin a ganin NEPU shawarar
da Awolowo ya bayar kan tsarin mulkin da ya kamata a bi shi ne daidai, kawai
dai hassada ce ta sanya NPC sukar wannan batu. Idan aka duba za a ga cewa,
hassada mummunan abu ne, kuma babu wanda zai so a danganta shi da shi, su kuwa
a wurin ‘yan siyasa abu ne da suke amfani da shi don hana abokin hamayya motsi.
Ya zama wani hali na ‘yan siyasa wanda da zarar an ga kuskuren ɗan siyasa aka
nemi yi masa gyara sai a ce hassada ake yi masa. Wannan ya sa abokan hamayya da
zarar sun yi magana sai a ce hassada ce suke yi wa jam’iyya ko ɗan siyasa ba da
zuciya ɗaya suke yi ba.
Samun tababa a cikin
nasabar mutum babban abu ne da kan sa mutum ya rasa ƙimarsa a idon mutane,
wannan ya sa ‘yan siyasa kan riƙa yin yarfe a duk
lokacin da aka samu wata ƙofa wadda ta ba su damar hakan. A baya
an yi ta yaɗa maganganu na yarfe da suke nuna cewa wani mataimakin shugaban ƙasar Nijeriya
tsintacce ko kuma ba a san iyayensa ba. ‘Yan hamayya sun yi ta amfani da wannan
domin dasusashe haskensa. Irin wannan ya fito a ciki littafin Kowa Ya Bi inda aka nuna cewa gwamnan
jihar bai san iyayensa ba. Ga misalin:
... to amma yadda za ku san batun ƙaryar shekarun da takardun da ma uwa uba rashin tabbacin iyayen gwamna
don kowa ya san a gidan marayu ya girma. Sannan har yanzu gwamna ya kasa fitowa
ƙarara ya ƙaryata zarge-zargen a idanun duniya. Sai kame-kame yake yi idan an
tambaye shi. An ma taɓa tambayar mai ba shi shawara a kan batun shari’a sai ya ce wai a je gidan
marayu za a ga tarihinsa a rubuce. To ya ‘yan’uwa mu da Allah (SWT) ya ba mu
wannan babban gari mai tarihi ga manyan bayin Allah da waliyyai wai mun ba wa
jikan Musailamatul-Kazzabi yana mulkarmu ku san ba zai yiwu ba. (Gwammaja, 2007 sh. 30)
Kamar yadda aka riƙa yada cewa wancan
mataimakin shugaban ƙasar
ba shi da iyaye, haka wannan misalin ya nuna cewa gwamnan bai san iyayen sa ba
a gidan marayu ya tashi, kuma ‘yan hamayya ne suka sanya shi gaba suna
yi masa yarfe da wannan. Ba sabon abu ba ne a siyasar Nijeriya a zargi mutum da
rashin takardun karatu, wanda a lokuta mafi yawa akan samu yarfe ne kawai domin
idan aka bincika akan tarar sun yi har ma da shaida. Akan yi wa mutum yarfe da
cewa ba shi da iyaye ne don a rage ƙimarsa a idon duniya musamman idan an
rasa da me za a ɓata sunansa da shi.
Jam’iyyar NEPU ta
kamanta jamiyyar NPC da jam’iyyar gumaka, inda ta yi kira da kada a zaɓe ta.
Kalmar gunki dai an san wani abu ne da aka sassaƙa ko a ƙera ko a gina wanda
yake da sifar mutum ko wani abu mai rai, wanda ba ya iya amfanar da kansa
komai, kuma ba ya iya kare kansa daga cutarwa ko ya kare wani. Gunki ba ya
magana ba ya motsi balle ya iya aiwatar da wani abu. Ga misalin kamar haka:
...ina jan hankalin mutane masu zaben NPC da su manta da ita domin
jam’iyyar gumaka ce... (Gasakas,1961).
A nan ‘yan jam’iyyar hamayya ne suke yi wa
masu mulki yarfe da cewa jam’iyyarsu ta gumaka ce. A nan ɗayan uku ne, ko dai
jam’iyyar ba ta iya tsinana wa al’umma komai kamar yadda gunki ba ya iya
amfanar kansa balle waninsa, ko kuma manyan jam’iyyar NPC ne aka danganta su da
gumaka domin ana yi masu biyayya tamkar yadda ake bauta wa gumaka, ko kuma su
‘yan jam’iyyar baki ɗaya daga shugabannin har mabiyan bautar gunki suke yi ba
Allah suke bauta wa ba. Tun daga taken wasiƙar da jaridar ta buga
za a fahimci cewa, mai wasiƙar yana nufin duk wanda ya bi jam’iyyar NPC ya ɓata
kamar dai yadda mai bautar gumaka yake ɓatacce kamar yadda Musulunci ya nuna.
Bayan faɗuwar jam’iyyar PDP a babban zaɓen
ƙasa a shekarar 2015,
shugaba Muhammadu Buhari ne ya zama shugaban ƙasar Nijeriya a jam’iyyar APC. Bayan
rantsar da shi ya yi fama da rashin lafiya, inda ya tafi jinya ƙasar Birtaniya. Bayan
dawowarsa don ci gaba da gudanar da harkar mulki, sai aka yi ta raɗe-raɗin cewa
ai ainihin Buhari ya mutu, an sauya shi ne da wani mai kama da shi mai suna
Jibril daga Sudan. Wannan zance ya yi tashe a cikin al’umma kasancewar tun
da ya dawo sai karsashinsa ya sauya ya ragu tamkar ba Buharin da aka zaɓa ba.
Wannan ya sa wasu al’ummomi
daga wasu ɓangarorin ƙasar
suka riƙa kiransa da Jibril
na Sudan. Shugaba Buharin ya nuna cewa shi ne da kansa ba a sauya shi da na
bogi ba. Dubi wannan misalin:
A jiya Shugaban
Najeriya Muhammadu Buhari ya bayyana cewa shi ba na bogi ba ne, ya bayyana
hakan ne a ganawar da ya yi da al’ummar Najeriya mazauna kasar Poland a birnin
Krakow a ziyarar da ya kai kasar domin halartar taron sauyin yanayi na
Majalisar dinkin duniya. A yayin ganawar, wani dan Najeriya ne ya yi masa
tambaya a kan cewa shin da gaske ne cewa shi ne Buhari da aka sani ko kuma wani
ne ke kwaikwayon sa da ake kira Jibril daga Sudan. Shugaban ya yi Allah
wadai masu yada wannan jita-jitar tare da cewa, ba su san ya kamata ba... (Adamu,
2018).
Shugaba Buhari ya
fito ne ya tabbatar wa duniya cewa yarfen da ake yi masa cewa shi ba na bogi ne
ba, shi ne dai gangariyarsa, ba wani ne yake kwaikwayonsa ba, kuma ya nuna
rashin jin daɗinsa da wannan labarin da ake ta yaɗawa. Irin wannan yarfe ne na ƙima domin ana nuna
cewa ba shi da nagarta kamar yadda aka san shi a farko kama mulkinsa a matsayin
zaɓaɓɓen shugaban ƙasa.
A jamhuriya ta huɗu
an samu wata hanya ta yarfe wadda za a samu wani ɗan bangar siyasa a biya shi,
sai a kitsa masa abin da ake so ya fito ya faɗa a wata kafar watsa labarai,
kuma in ma wani abu ya biyo baya iyayen gidansa na siyasa su ne za su tsaya
masa don fitar da shi. Irin waɗannan mutane da akan ɗauka haya a siyasance ana
kiran su da ‘sojojin baka’. Aikin irin waɗannan
sojojin bakan shi ne su fito su ƙalubalanci ‘yan hamayya ta hanyar
yarfe ko kuma su kare iyayen gidansu ta hanyar yi wa abokan hamayya yarfe. Irin
wannan misalin na sojan baka ya bayyana a cikin littafin Da Bazarku inda aka bai wa wani sojan baka mai suna Auwalu wasu
bayanai na yarfe a rubuce wanda aka yi wa Farfesa Auta. Ga misalin:
Wai yaro ƙarami kamar
Auwalu wanda mahaifinsa ma almajirinka ne wai shi ne yau zai shiga gidan rediyo
yana faɗar wai Farfesa ma da ake kiranka na je-ka-na-yi-ka ne… kuma wai kai ɗin
nan Bafillatani ne, don haka idan aka yi kyakkyawan bincike wai kai ba ma
mutumin ƙasar nan ba
ne... Farfesa Auta ya yi murmushi ya ce, na saurari duk abin da yaron nan ya faɗa,
amma kai da ji ka san rubuta masa aka yi ya haddace domin haka ka rabu da su ko
ba-daɗe ko ba-jima gaskiya dai ɗaya ce tal kuma siyasa ba da gaba muke yin ta
ba. (Surajo,
2006 sh. 95).
A cikin misalin an
nuna cewa Auwalu ya shiga gidan rediyo ya yi wa Farfesa Auta yarfe ta hanyar taɓa
ƙimarsa da cewa wai
shi ɗin Farfesan bogi ne, kuma wai in ma aka tsananta bincike a tarar cewa shi
ba ɗan ƙasa ba ne don kawai
shi Bafulatani ne. Don a nuna cewa sojan baka ne shi ɗaukar hayansa aka yi, sai
Farfesa Auta ya ce, ai ko da jin yadda yake magana za a fahimci duk bayanan da
yake faɗa rubuta masa aka yi ya haddace su, kuma in aka yi haƙuri gaskiya za ta
bayyana.
Idan aka dubi dukkan
bayanan da aka kawo a wannan ɓangaren za a fahimci cewa, wani nau’in yarfe ne da ake
amfani da ƙima ko halaye wajen
yin sa. Akan yi amfani da irin wannan yarfen ne don taɓa ƙimar wani ɗan siyasa
ko jam’iyyarsa ko kuma nuna
wani mummunan hali tare da danganta shi da shi.
4.3 Yarfe Na Tafiyar Da Shugabanci
Tafiyar da shugabanci
wani nauyi ne na al’umma wanda akan ɗora wa shugabanni domin gudanar da al’amuran al’umma yadda ya dace
bisa tsarin doka. Tsarin shugabanci na siyasa ya tanadi wasu tsare-tsare na
dokoki waɗanda ake amfani da su wajen warwarewa da kuma daidaita abubuwan da
suka shafi gudanar da al’amuran jama’a, ba tare da sanya
son zuciya ko kuma bai wa wani ɓangare fifiko a kan wani ba. Bin ire-iren waɗannan
dokoki sau da ƙafa galibi shi ne
yake haifar da daidaito da adalci da kuma zaman lafiya. Sau da dama duk wanda
ya bijirewa irin wannan tsarin doka akan kalle shi a matsayin mara gaskiya.
Duk da cewa bin waɗannan
dokokin tsarin mulki shi ne daidai kuma abin da ya dace, amma wasu kan yi
amfani da wannan don ganin wallen masu so su ɗabbaƙa su, har ma a wasu
lokuta a zarge su da rashin yin abin da ya dace tun da ba su bar kowa ya yi
yadda ya ga dama ba. A cikin siyasa akan yi wa ɗan siyasar da ya nuna cewa in
ya hau mulki zai riƙe
gaskiya da adalci ba tare da nuna sani ko sabo ba yarfe da cewa zai wulaƙanta manya ko zai ci
mutuncin wasu. Alal misali, a lokacin da tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari
yake gudanar da yaƙin
neman zaɓe ya yi ta bayyana cewa zai hana cin hanci da rashawa da almundahana
da dukiyar ƙasa, kuma duk wanda
ya saci dukiyar ƙasa za a ƙwato, sai aka riƙa yi masa yarfe cewa
yana da niyyar cin mutuncin manya ne. Wannan ya sa abokan hamayya suka dage don
ganin bai kai labari ba. Irin wannan misali ne na yarfe na tafiyar da
shugabanci, domin ana nuna cewa ga hanyar da zai bi ne wajen tafiyar da jama’a
idan ya samu ya ɗare karagar mulki. Irin wannan misalin ya bayyana a cikin
littafin Da Bazarku... Ga misali:
...a cikin wannan jaridar tabbas na
karanta wata hira da aka yi da Farfesa Auta a kan gyaran kundin tsarin mulkin ƙasar nan …Ya dai so ya yi taɓargaza
ne, tun da cewa ya yi shi fa har yanzu bai iya faiyace takamaiman aikin da
sarakuna suke yi ma talakawansu. Saboda haka wai shi yana ganin ya kamata a
faiyace wannan lamari a cikin sabon kundin da ake shirin tsarawa... Lauya ya
ce, ‘to a nemo mana ita daga nan zuwa
jibi ko gata, mu kuwa za mu yi farfaganda mu birkita abin da ya faɗa a ciki,
shafa masa kashin kaji a idanun talakawa da sarakuna. Kai kuwa tauraruwarka ta
haskaka hasken da ba wanda ya isa ya dusashe ta. (Surajo, 2006 sh. 50-51).
A cikin wannan misalin an nuna yadda
ɗan takarar shugabancin ƙasa Farfesa Auta ya yi hira da ‘yan Jarida ne kan batun
yi wa kundin tsarin mulki gyaran fuska, inda ya nuna cewa ya kamata a fayyace
aikin sarakuna a cikin kundin tsarin mulki. Wannan ya sa aka shirya nemo
jaridar a birkita zancen a shigar da abin da za a yi masa yarfe da shi don a shafa
masa kashin kaji. Idan aka duba wannan yarfe ne na tafiyar da shugabanci, domin
ya nuna idan ya samu dama zai yi gyara ga kundin tsarin mulki ta hanyar bayyana
irin aikin da ya kamata sarakuna su riƙa yi wa talakawa, amma sai aka nuna za a shafa masa kashin
kaji da wannan don al’umma su dawo daga rakiyarsa, kuma tauraron abokin takararsa ya
haskaka.
Wani lokaci idan ana so a yi wa ɗan
siyasa yarfe sai a yi masa riga-malam-masallaci ta hanyar aikata wani abu don
nuna cewa shi ya kasa, ko kuma a yi kira gare shi ko jam’iyyarsa kan aikata wani
abin da ya dace ba don ana son a aikata ɗin ba, sai don al’umma su yarda cewa jam’iyyar hamayya ba ta kan
tsarin da ya dace ko ba ta bin doka da oda. Alal misali, jaridar Leadership Hausa ta buga wani labari
wanda ta ce jam’iyyar hamayya ta PDP ta yi kira ga gwamnan jihar Kebbi da ya miƙa ragamar mulki a hannun
mataimakinsa bayan bayyana cewa gwamnan yana shirin tafiya aikin Hajji. Ga
misalin:
Mataimakin
gwamnan jihar Kebbi, Sanata Umar Abubakar Tafida, ya nesanta kansa da sanarwar
da jam’iyyar hamayya ta PDP ta fitar na neman a miƙa ragamar mulkin jihar biyo bayan gwamnan jihar na shirin tafiya aikin
Hajji 2024.
Tun da farko dai jam’iyyar PDP ce
ta fitar da sanarwa a ranar Laraba 5 ga watan Yuni a Birnin Kebbi inda ta buƙaci
Gwamnan Jihar da ya miƙa ragamar mulki ga mataimakinsa tun da yana shirin
tafiya Saudiyya domin gudanar da aikin Hajjin bana. (Birnin-Kebbi,
2023).
Idan aka duba za a ga cewa a doka idan gwamna zai yi tafiya
irin wannan zai bar ragamar tafiyar da al’umma a hannun mataimakinsa ne, amma
sai aka jiyo jam’iyyar hamayya tana yin kira ga gwamnan jihar da ya yi hakan.
Wannan idan aka kula za a ga cewa yarfe ne na tafiyar da shugabanci, domin yana
nuna cewa kamar gwamnan ba ya bin tsarin doka na tafiyar da mulkin jihar ne,
kuma wannan zai iya yin tasiri ga al’umma wajen ganin wallen gwamnan. Hakan ne
ya sa mataimakin gwamnan jihar ya fito ya mayar masu da martani cewa, ko da
yaushe gwamnan jihar yana miƙa mulki ga mataimakin
nasa ko da tafiyar yini ɗaya ya yi na barin ya jihar. Dubi abin da ya ce:
A cewar Sanata Umar, “Mun yi mamakin
da’awar da ƴan hamayya ke yi na cewa
a miƙa min ragamar mulki,
domin ko da rana ɗaya Gwamna Nasir bai taɓa hanani yin aiki ba. (Birnin-Kebbi, 2023).
Idan aka duba za a fahimci cewa wannan yarfe ne aka yi wa
jam’iyya mai mulki ta hanyar nuna cewa ba su iya tafiyar da shugabanci ba, ko
kuma ba su bin doka a tsarin shugabancinsu.
A lokacin mulkin shugaba Buhari musamman daga 2015 zuwa 2019,
an ɗauka cewa duk wanda ba ya tare da shi to kamar mutum ne da bai yi imani ba,
domin ana ganin kauce wa tsarin tafiyar Buhariyya kamar kafirci ne a siyasance.
Wannan yana daga cikin dalilan da suka sanya da yawan ‘yan siyasa suka bi ɗariƙar Buhariyya ba don suna
so ba, sai don su tsira da imaninsu a siyasance a fuskar mabiyansu. In ba haka
ba za a bi su da yarfe cewa suna hamayya da Buhari ko tafarkinsa. Dubi wani
misali mai kama da wannan a ƙasa:
Saboda mutane sun dauki Shugaba Muhammadu
Buhari tamkar mahadi da saba masa tamkar saba wa Allah ne, sai wasu ’yan siyasa
suke amfani da wannan dama wajen bata abokan siyasarsu don su lalata su. Duk
wanda yake son lalata maka siyasa sai ya ce kana fada da Buhari. (Mustapha, 2015).
Akwai waɗanda aka gurgunta tafiyar
siyasarsu sanadin yarfen da aka yi masu da cewa suna faɗa da Buhari, domin a
lokacin mutane suna yi wa Shugaba Buharin kallon wani waliyyi a siyasance wanda
saɓa masa tamkar saɓa wa Allah ne, shi ya sa idan ana so a ɓata siyasar wani
sai a yi masa yarfe da cewa yana yi wa Buhari zagon ƙasa ko
yana faɗa da shi. Irin wannan ya karya alkadarin ‘yan siyasa da dama a zamaninsa.
Idan aka dubi waɗannan
bayanai da suka shafi yarfen siyasa, za a fahimci inda aka fito a tarihin
ginuwar siyasar jam’iyyu
a ƙasar Hausa, wanda
wannan shi ne ya share hanya zuwa sauran jamhuriyoyin da aka samu bayan ta
farko. Irin waɗannan sun ci gaba da faruwa a cikin siyasar ƙasar Hausa, kuma an
ci gaba da amfani da su a matsayin hanyoyin samun magoya baya da kore wa abokan
hamayyar siyasa mabiya.
5.0 Sakamakon Bincike
Daga bayanan da aka
kawo a sama an fahimci cewa tarihin ginuwar siyasar jam’iyyu a ƙasar Hausa yana cike
da wasu al’amura waɗanda suka
zama tamkar gishiri a cikin miyar siyasar jam’iyyu. Daga cikin waɗannan
abubuwa kuwa akwai yarfe, wanda za a iya cewa yin amfani da shi a zahiri da
kuma tsarin zamantakewa ba za a ce daidai ba ne, domin a wasu lokuta yakan taɓa
mutuncin wani kai tsaye cikin abin da babu tabbas ko ma ba gaskiya ba ne, sai
dai a siyasance ya zama hanyar jawo ra’ayin al’umma ne domin samun
goyon bayansu.
Binciken ya gano
cewa, yarfe ba sabon abu ba ne a cikin siyasar jam’iyyu a Arewacin Nijeriya,
wato suna da asali tun daga farkon kafuwar jam’iyyun siyasa, kuma har yau ana
amfani da shi domin cimma manufofin siyasa.
Wani abu kuma da
binciken ya gano shi ne, yarfe yana taimakawa wajen samun nasara ko akasin haka
a cikin siyasa, domin yakan kore wa wanda aka yi wa yarfen mabiya wanda kan sa
ya rasa mabiya kuma ya yi rashin nasara a zaɓe.
5.1 Naɗewa
Wannan takarda ta tattauna
a kan yadda aka riƙa amfani da yarfe ne a
cikin tarihin ginuwar siyasar ƙasar Hausa. Tun da
farko a cikin gabatarwa an kawo taƙaitaccen tarihin
faruwar siyasar jam’iyyu a ƙasar
Hausa. Daga nan sai aka kawo ma’anar yarfe da
siyasa domin haska inda sunan takardar ya dosa. Daaga bisani sai aka tsunduma
cikin nazarin yarfe a cikin tarihin ginuwar siyasar ƙasar Hausa, wanda
aka riƙa kawo misalai daga rubutaccen zube na Hausa. A ƙarshe,
binciken ya gano cewa siyasar jam’iyyu a ƙasar
Hausa cike take da yarfe wanda ya samo asali tun daga farkonta, kuma ba abin
mamaki ba ne idan aka ga an ci gaba da amfani da shi a fagen siyasar jam’iyyu
a yau matsayin wata hanya ta samun magoya baya da kuma kore wa abokan hamayya
mabiya wanda hakan yakan taimaka wajen samun nasara a zaɓe ko akasinsa.
Manazarta
Adamu, A. I. (2021). Dabarun Jawo Hankali A
Wasu Waƙoƙin Siyasa A Jihohin Kano
Da Katsina da Zamfara Daga 2007 Zuwa 2018. Kundin
Digiri na Uku, Sashen Koyar Da Harsunan Nijeriya. Kano: Jami’ar Bayero.
Adamu, J. (2018, Disamba 3). Wasu Sun
Jahilce Ni, Ni Ba Na Bogi Ba Ne- Buhari. An samo daga https://aminiya.ng/wasu-sun-jahilce-ni-ni-ba-na-bogi-ba-ne-buhari/
Adamu, M. (2019). Kawatanci
Tsakanin Rubutattun Waƙoƙin Siyasar Jumhuriya Ta
Uku Da Na Jumhuriya Ta Huɗu A Nijeriya. Kundin Digiri na Uku. Katsina: Jami’ar Umaru Musa Yar’adua.
Addinin Musulunci Mazahabar Maliki. (1960, Yuni
4). A cikin Jaridar Daily
Comet, B. Sh.
Alasan, M. (1961, February 11). Alla Ya Tsari
Musulmin Gaskiya Shiga NPC Da AG. A cikin Jaridar Daily Comet, B. Sh.
A.G. Na Maganin Mutuwa A Arewa. (1959, Disamba, 9). A cikin jaridar Sodangi, shafi na 5.
Aminiya-Trust (2020) Dambarwar
Siyasa. Kaduna: Tast and Print Ventures.
Bai Kyautu NPC Ta Soki Maganar Da Awolowo Yayi Ba Ta Neman
Nigeria Ta Zama Jamhuriya Dr Azikiwe Ya Zama Shugaban Farko. (1961, Fabrairu 13).
A cikin Jaridar DailyComet, B. Sh.
Barry, P. (1995). Beginning Theory: An Introduction to Literary and
CulturalTheory. London: Manchester University Press.
Birnin-Kebbi,
U. F. (2023, Yuni 6). Mataimakin Gwamnan Kebbi Ya Nisanta Kansa Da
Kalaman PDP. An samo daga https://hausa.leadership.ng/mataimakin-gwamnan-kebbi-ya-nisanta-kansa-da-kiran-pdp-na-a-mi%c6%99a-masa-ragamar-mulkin-jihar/
Birniwa, H. A. (1987). Conservatism and Dissent: A Comparative Study of NPC/NPN and NEPU/PRP
Hausa Political Verse from
Circa 1946 To 1983. Kundin digiri na Uku, Sashen Harsunan Nijeriya. Sakkwato:
Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo.
Blackburn, S. (1994). Oxford Dictionary of Philosophy.
New York: Oxford University Press.
CNHN (2006). Ƙamusun Hausa na Jami’ar Bayero. Zaria:
Ahmadu Bello University Press.
Dudley, B. J. (1968). Parties and Politics in Northern Nigeria. London: Frank Cass and Co, Ltd.
Ɗan
Alhaji, D. (2006). Jigo, Salo da Tsari a Fina-Finan Sarauniya da FKD. Kundin
Digiri na Ɗaya. Sashen Nazarin
Harsunan Nijeriya da Afirka. Zariya: Jami’ar Ahmadu Bello.
Ɗan’illela,
A. (2010). Rubutattun Waƙoƙin Siyasa: Nazari A
Kan Jihohin Sakkwato Da Kebbi Da Kuma Zamfara. Kundin Digiri na Biyu. Sashen
Harsunan Nijeriya. Sakkwato: Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo.
Ɗangulbi,
A. R. (2003). Siyasa A Nijeriya: Gudunmawar Marubuta Waƙoƙin Siyasa Na Hausa ga
Kafa Dimokuraɗiyya a
Jumhuriya ta Huɗu Zango na
Farko. Kundin Digiri na Biyu. Sashen Harsunan Nijeriya. Sakkwato: Jami’ar
Usmanu Ɗanfodiyo.
Ekwueme Zai Ba Mu Kunya. (1999,
Fabrairu 8). A cikin Jaridar Gaskiya Ta
Fi Kwabo, Shafi na 9.
Farouk, U. B. (2006). Dangantakar
Harshe da Addini: Nazari a kan Ilimin Walwalar Harshe. Kundin Digiri na Ɗaya. Sashen Nazarin Harsunan Nijeriya. Sakkwato:
Jami’ar Usmanu Danfodiyo.
Funtua A.I. (2003). Waƙoƙin Siyasa na Hausa a Jumhuriya ta Uku: Yanaye-Yanayensu da Sigoginsu.
Kundin Digiri na Biyu, Sashen Harsunan Nijeriya. Kano: Jami’ar Bayero.
Gasakas. U. (1961, February 13). Na Fita Daga NPC, Ina
Fata Allah Ya Nunawa Saura Batattu Hanyar Fita. A cikin jaridar Daily Comet B.Sh.
Greenblatt, S.(1980) Renaisance
Self-Fashioning: From More to Shakespeare: Chicago: University of Chicago
Press.
Gwammaja, A. S. I. (2007) Kowa Ya Bi. Kano: ASIN Publishers.
Habib, M.A.R. (2008). Modern Literary Criticism and Theory: A History. UK: Blackwell Publishing.
Idris, Y. (2010). Waƙoƙin Addini na Siyasa: Nazarin Waƙoƙin Emmanuel Wise Mai
Molo. Kundin Digiri na Biyu. Sashen Harsunan Nijeriya da Afirka. Zariya:
Jami’ar Ahmadu Bello.
Idris, Y. (2016). Bijirewa A Waƙoƙin Siyasa: Bincike Kan Waƙoƙin 1903-2015. Kundin
Digiri na Uku. Sashen Harsuna da Al’adun Afirka. Zariya: Jami’ar Ahmadu Bello.
Katsina, S. I. (1983) Tura Ta Kai Bango. Zaria: Northern
Nigerian Publishing Company LTD.
Lallai Babu Tarbiyya. (1957,
Disamba 8).
A cikin jaridar Sodangi, shafi na 8.
Lawal, N. (2018). Adabi da Tarihanci:
Nazarin Wasu Wasanni na Rudolf Prietze. Kundin Digiri na Biyu. Zaria: Jami’ar
Ahmadu Bello.
Malumfashi, I. A. (2013). Taƙaddama Da Gwagwarmayar Siyasar Arewacin Nijeriya
Daga Mawaƙan Siyasa A Bisa Faifan Nazari. Maƙalar Da Aka Gabatar A
Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Cibiyar Harsunan Nijeriya, Jami’ar Bayero Kano, daga 14-16 Ga Watan Janairu 2013.
Mashi, M. B. (1986). Waƙoƙin Baka na Siyasa, Dalilansu da Sababinsu ga Rayuwar Hausawa. Kundin
Digiri na Biyu. Kano: Jami’ar Bayero.
Mohamed. Z. (1960, Janairu 20). Dan Tauraro Da Sata.
A cikin jaridar Sodangi. Shafi na 8.
Muhammad, H. (2006). Tasirin
Al’ada da Addini da Boko ga Suturar Matan Hausawan Zamani. Kundin Digiri na Ɗaya. Sashen Harsunan Nijeriya da Afirka. Zariya:
Jami’ar Ahmadu Bello.
Mustapha,
O. (2015, Satumba 4). Yarfen Siyasa Ce A Ce Muna
Gaba Da Buhari – Ali Wakil. An samo daga https://aminiya.ng/yarfen-siyasa-ce-a-ce-muna-gaba-da-buhari-ali-wakili/
Nadabo, Y. (1960, Janairu 13). Fam Biyar Ta Yi Mana
Kadan. A cikin jaridar Sodangi Shafi na 5.
Paden, J. N (1973). Religion and Political Culture in Kano.
London: University of California press.
Sani, M. M. (2012). Tunanin Siyasa a Waƙoƙin Malam Hassan Nakutama. Kundin digiri na Biyu. Sakkwato: Jami’ar
Usmanu Ɗanfodiyo.
Surajo, B. I. (2006). Da
Bazarku. Kano: Gidan Dabino Publishers.
Yahaya, I. Y. (1988). Hausa A Rubuce: Tarihin Rubuce-Rubuce Cikin Hausa. Zaria: NNPC
Yusuf, J. (2018). Tarihin Jam’iyyar
PDP A Bakin Marubuta Waƙa.
Kundin Digiri na Biyu. Sakkwato: Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo.
Hira
1. Hira
da Farfesa Atiku Ahmad Dunfawa, malami a sashen Koyar da Harsunan Nijeriya
Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo, Sakkwato a
ofishinsa, ranar 10 ga watan Yuni, 2024, da misalin ƙarfe 2:15 na rana.
2. Hira
da Dr. Isa Abdullahi Muhammad, malami a sashen Koyar da Harsunan Nijeriya
Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo, Sakkwato a
ofishinsa, ranar 15 ga watan Yuli, 2024, da misalin ƙarfe 4:33 na rana.
3. Hira
da Dr. Rabiu Bashir, ɗan siyasa, kuma malami a sashen Harsunan Nijeriya da
Kimiyyar Harshe, Jami’ar
jihar Kaduna a ofishinsa, ranar Alhamis 16 ga watan Mayu, 2024, da misalin ƙarfe 2:10 na rana.
4. Hira
da Dr. Dano Balarabe Bunza, tsohon ɗan siyasa kuma malami a sashen Koyar da
Harsunan Nijeriya Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo, Sakkwato a ofishinsa, ranar
10 ga watan Yuni, 2024, da misalin ƙarfe 2:37 na rana.
5. Hira
da Uwargidan Alhaji Ibrahim Lazuru, tsohon shugaban ƙaramar hukumar
Lere, jihar Kaduna, a gidansa da ke Sabon Kawo Kaduna. Ranar 22 ga Maris, 2021,
da misalin ƙarfe 5:40 na yamma.
[1] A mu’amala ko zance na yau da kullum ana iya kiran kalmar da “ƙage” ko
kuma “ƙaƙe”, ta fuskar siyasa kuma akan ce “ƙaƙen siyasa” a karin harshen ƙasar
Sakkwato, kamar yadda aka samu daga tattaunawar da aka yi da Dr. Dano Balarabe
Bunza na sashen Koyar da Harsunan Nijeriya, Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo, Sakkwato.
Ranar 10/6/2024 a ofishinsa.
[2] Hira da Dr. Isah Abdullahi Muhammad malami a sashen Koyar da Harsunan
Nijeriya, Jami’ar Usmanu Danfodiyo, Sakkwato. Ranar 15/7/2024 a ofishinsa.
[3] Hira da Dr. Rabiu Bashir, ɗan siyasa kuma malami a ofishinsa da ke
sashen Koyar da Harsunan Nijejiya da Kimiyyar Harshe, jami’ar Jihar Kaduna,
ranar 16 ga watan Mayu, 2024.
[4] Dubi ɗure na 3.
[5] Hira da Farfesa Atiku Ahmad Dunfawa a ofishinsa da ke sashen Koyar da
Harsunan Nijeriya, jami’ar Usmanu Danfodiyo, Sakkwato. Ranar 15/7/24 da misalin
ƙarfe 2:15.
[6] Dubi Paden, J. (1973:122) Religion
And Political Culture in Kano.
Dubi Scott, P. H. G. (1952:2) A survey of Islam in Northern Nigeria.
[7] Dubi Paden, J. (1973:199) Religion
And Political Culture in Kano.
[8] Hira da Uwargidan Alhaji Ibrahim Lazuru, tsohon shugaban ƙaramar
hukumar Lere, jihar Kaduna a gidansa da ke Sabon Kawo Kaduna. Ranar 22 ga
Maris, 2021.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.