𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Slm mlm anwuni lfy. Mlm ina yawan kokwanto a cikin sallah ta kuma wlh sai na zo tsakiyar sallah ya zan yi ALLAH ya sakawa mlm da alkairi
HUKUNCIN MAI YAWAN KOKWONTO
A CIKIN SALLAH
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa'alaikumusalam
warahmatallahi wabarakatuh.
Was-wasi acikin Sallah kala
biyu ne:
1. Akwai wanda yake faruwa
ta dalilin sakaci da shagaltuwa da sha'anin duniya da kuma rashin damuwa da Sallar
daga wajen Shi mai sallar. Ta yadda zaka ga mutum yana sallah amma idonsa akan
hanya, ko ta window yana ganin masu wucewa. Ko kuma mutum yana Sallah amma ya
kunna TV agabansa ko radio. (ba yaso labarai su wuceshi). Ko kuma kaga Alhaji
yana Sallah a Masallaci amma zuciyarsa tana kasuwa. Harma wasu lokutan idan
Liman ya yi rafkanuwa a Sallar, da zarar Mamu sunyi Kabbara sai kaga Alhaji ya
firgita. Azatonsa ko yaƙi
aka soma.
Hukuncin irin waɗannan
Was-Wasin, Haramun ne. idan ma basu ɓatawa
Mutum Sallarsa ba, to zasu iya kaishi izuwa Rasa ladan sallar.
2. Was-wasi na biyu kuma Shi
ne irin was-wasin da Shaiɗanun Aljanu suke haifarwa
Mutum idan sun shiga jikinsa, ko kuma su na son su shiga. Zaka ga masu fama da
irin wannan larurar suna da yawan kokwanto acikin yawancin lamura. Musamman ma
asha'anin Ibada. Zaka ga idan sunzo Sallah su na yin iyakar bakin Kokarinsu
wajen Kiyayewa, amma inaa! Zaka ga sun kidime sun rikice sun manta ko raka'a
nawa sukayi. Galibi ma tunane-Tunane irin na Saɓon
Allah ne zasu rika zuwa musu acikin Sallar. Irin wannan babu laifi akan shi Mai
sallan. Domin kuwa yana yin iyakar kokarinsa. Wani ma har kuka zaka ga yana yi.
Kuma abin ya riga ya zama masa chuta ko larura.
MAGANINSA SHI NE:
1. Mutum ya dage da yawan
ambaton Allah acikin dukkan motsinsa. Duk abin da zaiyi ya fara da Basmalah.
2. Yawaita karatun Alƙur'ani. Da kuma sauraron sautin Alƙur'ani.
3. Ya rika karanta Azkar na
safe da yamma. Da na kwanciyar bacci da tashi.
4. Ya dena barin najasa tana
dadewa ajikinsa. Ya yawaita zama cikin tsarki da alwala.
5. Ya gujewa ayyukan saɓo
manya da kanana.
6. Duk lokacin da zaiyi
Sallar ya rika karanta Du'a'ul-Istifta hi Afarkon Sallar. insha Allahu zai samu
saukin abin.
Malamai sunce duk wanda irin
wannan kokonton ya aureshi, ya yi sujjadah ba'adi (duk sanda ya idar daSallar).
WALLAHU A'ALAM.
Zauren Fatawoyi Bisa
Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
Sanin cewa waswasi daga Shaiɗan
ne
Allah Maɗaukaki
ya ce:
﴿مِنْ شَرِّ الْوَسْوَاسِ الْخَنَّاسِ الَّذِي
يُوَسْوِسُ فِي صُدُورِ النَّاسِ﴾
“Daga sharrin mai waswasi mai ɓuya, wanda yake yi wa
zukatan mutane waswasi.”
— Suratul-Nas 114:4-5
Manzon Allah ﷺ ya ce:
«إنَّ الشيطانَ يأتِي أحدَكم فيقولُ: مَن خلقَ
كذا؟ حتَّى يقولَ: مَن خلقَ ربَّكَ؟ فإذا بلغ ذلك فليستعِذْ باللهِ ولينتهِ»
“Shaiɗan
yana zuwa wajen mutum yana ce masa: wa ya halicce kaza?... Har ya ce: wa ya
halicci Ubangijinka? Idan ya kai wannan, to ya nemi tsari ga Allah, ya daina
wannan tunanin.”
— Sahih al-Bukhari (3276), Sahih Muslim
(134)
Wannan yana nuna cewa
waswasi bai daga mutum ba, shaiɗan
ne ke yi domin ya ɓata
sallah.
Waswasi na sakaci da shagaltuwa da duniya
Allah ya umurce mu da nutsuwa cikin ibada:
﴿قَدْ أَفْلَحَ الْمُؤْمِنُونَ الَّذِينَ هُمْ
فِي صَلَاتِهِمْ خَاشِعُونَ﴾
“Lalle muminai sun yi nasara — waɗanda suke da nutsuwa a
cikin sallarsu.”
— Suratul-Mu’minun 23:1-2
Wannan nau’in waswasi idan mutum ya yi shagali da TV, waya,
ko kasuwanci, zai rage masa lada ko ya ɓata
masa sallah idan ya kai ga barin rukuni.
Waswasi na cuta daga Shaiɗan — wanda ake yawan mantuwa da kokwanto
Wannan wanda mutum yana ƙoƙari amma waswasi na cigaba, babu laifi a
kansa, saboda yana yaki da sharrin Shaiɗan.
Manzon Allah ﷺ ya ce:
«إنَّ اللهَ تجاَوَزَ لأمَّتي ما حدَّثتْ به
أنفُسَها ما لم تعملْ أو تكلَّمْ»
“Allah Ya yafe wa al’ummata tunanin da
zuciya ke kawowa muddin bai aikata shi ba ko ya faɗa.”
— Sahih al-Bukhari (6664), Sahih Muslim
(127)
Hukuncin wanda ya yi kokwanto a sallah
Manzon Allah ﷺ ya koyar cewa:
«إذا شكَّ أحدُكم في صلاتِه فلم يدرِ كم صلَّى
ثلاثًا أم أربعًا، فليطرَحِ الشَّكَّ وليبنِ على ما استيقنَ...»
“Idan wani ya yi shakka a sallarsa bai
san uku ko huɗu ba, to
ya watsar da shakkar ya dogara da abin da yake da tabbaci…”
— Sahih Muslim (571)
👉 Misali:
Idan ya yi shakka tsakanin raka’a 3 da 4, ya ɗauki 3, ya cika, sannan:
«ثم ليسجدْ سجدتينِ قبلَ أن يسلِّمَ»
“…sai ya yi sujjadar sahu kafin
sallama.”
Maganin Waswasi da Manzon Allah ﷺ ya koyar
Neman tsari ga Allah
«فليستعِذْ
باللهِ» — Bukhari da Muslim
Ƙin yarda da tunanin
«ولينتهِ»
— Bukhari da Muslim
Yawaita addu’o’i da zikiri
Allah ya ce:
﴿أَلَا بِذِكْرِ اللَّهِ تَطْمَئِنُّ الْقُلُوبُ﴾
“A, da ambaton Allah zukata sukan
nutsu.”
— Ar-Ra’d 13:28
Yawaita karatun Al-Kur’ani da sauraro
Kiyaye tsarki da alwala akai-akai
Gujewa ayyukan saɓo
domin suna buɗe ƙofa ga
Shaiɗan
Shawara ta ƙarshe
Duk wanda waswasi ya yi yawa gare shi:
Ya yi gaba da sallar sa kamar yadda yake iya
Kada ya biye wa shaiɗan
da sake maimaitawa
Ya yi sujjadatul-sahw bayan kammalawa
Ya dage da karatun ruqya shar’iyya
Kammalawa
Waswasi gwajin shaiɗan
ne. Idan mutum ya dage da ibada da zikiri:
Allah zai ce:
﴿إِنَّ كَيْدَ الشَّيْطَانِ كَانَ ضَعِيفًا﴾
“Lalle makircin shaiɗan ya kasance mai rauni
ne.”
— Suratun-Nisa 4:76
Allah Ya ba ka lafiya, Ya tsare maka sallar ka, Ya kare ka
daga waswasi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.