𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu Alaikum malam. Idan mutum ya samu wani abu a hanya, shin ya Halatta ya ɗauka ya yi amfani da ita?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa'alaikumusalam
warahmatallahi wabarakatuh.
Tsintuwa ya rabu kashi uku:
1. Na farko: Tsintuwan abin
da bashi da ƙima mai yawa, kamar
tsintuwar Sanda, ko wani abin sha kaman lemu misali, ko Biredi misali. Ko irin tsintuwar
naira ashirin. Dai duk abin da a al’adance
an san mai ita bazai damu da ita ba idan ta ɓace.
To idan mutum ya tsinci irin wannan abu to zai yi amfani dashi babu laifi.
Saboda Hadisin da Abu dawud ya rawaito
Annabi (Sallallahu alaihi
Wasallam) ya yi rangwame game da tsintuwar sanda, ko igiya ko makamancin su.
Wanda ya samu ya yi amfani dasu Abu Dawud: 1717. (Sheikh Nasirud-din Albani ya
raunata Hadisin.).
2. Na biyu: abin da idan aka
barshi bazai salwanta ba har mai shi ya zo ya same shi. Kaman raƙumi, ko kujera, da makamantansu. Shi
wannan baya halatta a ɗauka. Domin an tambayi
Annabi Tsira da Amincin Allah su tabbata a gare shi game da tsintuwar Raƙumi sai ya ce: Ina ruwanka da ita? Tana
tare da ruwan shanta da abin da zai tsare mata ƙafafun
ta, tana zuwa wurin ruwa tasha, sannan tana cin bishiya har ta kai ga mai ita.
Sahihul Bukhari: 2372
Wannan Hadisi yana nuna cewa
ba’a tsintuwar raƙumi
ko wata dabba da za ta iya komawa zuwa ga mai ita. Ya shiga ƙarƙashin
wannan hadisi duk wani abu da idan aka barshi mai shi zai iya zuwa ya ɗauki
kayansa ba tare da wani matsala ba kamar yadda mukayi bayani a baya.
3. Na Uku: Dukiya da za ta iya
salwanta idan aka barta, kaman Rago ko akuya da makamantansu. Ko kuma sauran
dukiyoyi kaman kuɗi na takarda, ko zinari ko
azurfa. Idan abin da aka tsinta dabba ne kaman rago ko akuya to wanda ya same
ta zai yi ɗayan abubuwa uku:
1. Ko ya yanka yaci naman.
Amma idan mai ita ya dawo zai biya shi kuɗin
dabbar.
2. Ko ya siyar da dabbar ya
ajiye kuɗin
duk randa aka samu mai ita sai ya bashi.
3. Ko ya ajiye ya cigaba da
kiwon dabbar har randa Allah zai kawo mai shi. Idan ya ɗauki
lokaci mai yawa yaga bazai iya cigaba da ajiya ba to sai ya yi amfani da ɗayan
hanyoyi biyun farko.
Idan kuma dukiyar da ya samu
kuɗi ne
to zai ajiye. Yasan yawan kuɗin da yana yin kuɗin
sannan ya yi shela wa mutane. Zai yi ta sanar wa har na shekara guda. Idan aka
yi shekara guda ba’a samu mai shi ba to sai ya yi amfani da shi ko ya ba da sadaƙar sa. Amma idan mai dukiyar ya dawo
yana neman ta to zai biya shi.
An rawaito daga Annabi
Sallallahu alaihi Wasallam an tambaye shi game da tsintuwa sai ya umarci wanda
ya yi tsintuwa da ya san siffar abin da ya tsinta idan kuɗine
misali to yasan yawan kuɗin sannan yasan yana yin kuɗin
ta yadda idan mai shi ya zo ya yi bayani da ya gamsu cewa nashi ne sai ya
bashi. Sannan sai ya nemi mai ita har tsawon shekara guda. Idan bai samu mai
ita ba to sai ya yi amfani da dukiyar ko ya ba da sadaƙa. Wannan Hadisi Bukhari ya rawaito shi
a hadisi na 2372.
Ya kamata mu lura da abubuwa
kaman haka:
1. Kafin mutum ya ɗauki
tsintuwa dole sai ya aminta da kansa cewa zai nemi mai dukiyar, sannan kuma zai
kiyaye dukiyar har a samu mai ita. Idan yasan bazai iya haka ba to haramun ne
ya ɗauki
wannan tsintuwa.
2. Dole yasan adadin kuɗin
ko nau’in Dukiyar kamar yadda hadisin da muka kawo a sama ya yi bayani.
3. Dole idan ya ɗauki
dukiyar ya yi shela ya nemi mai ita. Zai yi shelan ne kuma da yana yi da ya
dace da zamanin sa. Misali ko ta gidan rediyo ko ta waya da makamantansu.
4. Idan mai dukiyar ya zo kuma
ya siffanta dukiyar daidai to dole a miƙa
masa dukiyar sa.
Idan ba’a samu mai dukiyar
ba to wanda ya samu ta zama tashi. Ko ya yi sadaƙa da
ita ladan ya kai ga mai dukiyar ko kuma ya yi amfani da ita. Amma idan mai
dukiyar ya dawo zai mayar masa da dukiyar sa. Wannan shi ne taƙaitaccen hukuncin Tsintuwa.
WALLAHU A'ALAM
Zauren Fatawoyi Bisa
Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.