Wannan waƙa an tsara ta ne domin taya murna ga Dr. Abu-Ubaida Sani game da kammala karatunsa na digirin digirgir. Da fatan Allah ya sanya wa wannan karatu albarka. Amin.
FURA
DA DAMU (Waƙar Taya Murna Ga Dr. Abu-Ubaida Sani)
Ta
USMAN NAGADO (II)
Na yi ma murna -Ubaidu,
Rabbi Allah ne ya bamu.
Yanzu an maishe ka Dakta,
Ga fura sauranka damu.
Kas siɗe ƙwaryarka tastas,
Kar ka yo wasa a kamu.
Mun yi murna mun yi murna,
Kai fa yaya ne a gunmu.
Yanzu ka koma fa koko,
Ka wuce layin su kamu.
Dan da mun yo tambayoyi,
Sai fa Amsoshi ka bamu.
Rumbunan ilimi ka tara,
Dan ka kore ƙishirwarmu.
Himma dai ɗan Muhamman,
Sani yau ga jinjinarmu.
Kai fari sauranka maimai,
Kai Muhim sauran Ahammu.
Kai ta ƙwazo ba musu sai,
Ka haƙe dukkan biramu.
Saƙon murna a waƙe,
Ni na miƙo gun gwaninmu.
Karɓi
Dakta Abu-Ubaida,
Ƴar mitsil nai kar ka damu.
Sha'iri ne ni wa ismi,
Usman Nagado gulamu.
Rabbana Allah ya kama,
Dakta ga addu'armu.
Biyu rak ga watan Oktoba,
Tu da Faif (25) Miladiyarmu.
Baitukan waƙar ka ƙirga,
Ai Sabintin (17) za ka samu.
FA'ILATUN FA'ILATUN,
Rabbi Allah ne ya ba mu.
©USMAN NAGADO (II)
2/Oktoba/2025.
4:30pm

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.