Assalamu Alaikum
FADAKARWA GAME DA
RAYUWARMU MATA, KAN ZAMANTAKEWA DA KISHIYA!
Daga
A’ishatu Muhammad
Bazango
A yau dai na so in yi maganar da na daɗe ina son yi ban samu na yi ba sai yau, dangane da mata masu kishiya da suke zalunci da munafurci...
Dan Allah 'yan uwa mata zan yi
magana game da yanda muke daukar rayuwar duniya da muhimmanci, da yanda muke
daukar kishiya, mun manta da lahirarmu, ba ma tinanin mutuwarmu, ba ma tinanin
hisabinmu.
Na sani cewa kishi halal ne,
sannan akwai zafi sosai, amma dan Allah kar mu bari kishi ya raba mu da
imaninmu, kar mu bari sheɗan
ya yi tasiri a kanmu, a kan ɗan
ƙaramin
abu na rayuwar duniya, shin ba ma lissafi ne? ba ma tinani ne?
Na taso na ga gidan su Mahaifina
mata biyu ne, kuma a iya zaman da na ga suna yi zama ne na fahimta
Alhamdulillah, a kwana a tashi har Allah ya yi ma Uwar gidan rasuwa, bayan
rayuwarta da wasu shekaru shi ma mijin ya rasu, ya rasu ba a dade sosai ba, ita
ma ɗayar ta rasu.
(Allah Ubangiji ya gafarta musu baki dayansu ya sa sun huta.)
Abin da ya sa na kawo wannan
maganar, ya kamata mu yi nazari a kai sosai mu yi tinani, yanzu fa su shikenan
sun yi rayuwarsu har sun wuce, to kamar haka ne misalin rayuwar duniya, da mai
kishiya da wacce ba ta da ita, duk rayuwar da za a yi ba za a kai shekaru ɗari a duniya ba, yanzu dan Allah wannan bai kai ya zama tashin
hankali ba? bai kai mu shiga hankalinmu ba? rayuwar lahira ita ce din-din-din,
abun da ka aikata a rayuwar duniya shi ne zai ba ka sakamakon lahira, mai kyau
ne ko marar kyau.
Mu dinga tinawa, babu wanda yake
tsara ma kansa rayuwa, da Amarya da Uwar gida tin kafin a haife su, kowa Allah
ya rubuta cewa ga mijin da zai aure ta, babu wanda ya isa ya guje ma hukuncin
Ubangiji. Ko da ke ba ki da kishiya, shin ba kya tinanin rayuwarki? ko kin san
yanda rayuwa za ta kasance miki zuwa gaba? kin san miji zai iya mutuwa ya barki
da yara? kin san za ki iya mutuwa ki bad yaranki? kin san miji zai iya mutuwa
ki zo wani mai mata ya aure ki? ya kike gani idan a rayuwarki na baya kina da
kishiya kin musguna mata? ba kya ganin ke ma hakan zai same ki?
To ke nan idan har mun san wannan
mi zai saka mu biye ma sheɗan?
Muna gaɓa da juna,
muna zaluntar juna? Muna saka gaɓa
a tsakanin yaranmu? Shin ba ma tinanin wannan da ba ma so, ita ma Allah ne ya
halicce ta? baiwar Allah ne? idan muka zalunceta Allah ba ya barin wanda aka
zalunta face Allah ya saka masa? ashe ba za mu ji tsoron Allah ba?
Ashe mutuwa bai ishe mu wa'azi
ba? wata rana kamar yanzu ko wanne a cikinmu baya nan, duk mun mutu, sannan a
lahira duk abin da muka aikata dole ne sai an mana hisabi a kai.
Ko da ace babu tashi bayan
mutuwa, yanzu mutuwa ba za ta zama mana wa'azi ba? ga rayuwar kabari ba mu san
mi za mu tarar ba? ga mutuwa koyaushe zuwa take babu sallama, shin mun shirya
ma duka wadannan? ita mutuwa babu ruwanta da shekarunmu nawa ne, yaron da aka
haifa yau ma ya tafi, wasu daga ciki ma suke mutuwa, manya sun mutu, ƙanana
sun mutu, Malama sun mutu, 'yan siyasa sun mutu, shuwagabanni sun mutu, ke nan
babu mai tsira a cikinmu? Dan Allah mu dena la'akari da shekarunmu, mu saka a
ranmu ko yaushe za mu iya mutuwa, ko yau ko gobe ki anjima, ko mun shirya ko ba
mu shirya ba. idan muka gina mai kyau kanmu za mu amfana, idan muka yi mummuna
a kanmu ne.
Ba ma tinanin mu ma muna da yara
ko ƙanne
ko 'yan uwa? ba ma tinanin abin da muka yi ma wasu na zalunci mu ma za a iya yi
ma namu?.
Allah ya kyauta ya sa mu dace
baki dayanmu ameen ya rabbi.
Daga:
A’ishatu Muhammad Bazango
Ummu Amatulqahhar Kitchen
#Amsoshi Kitchen
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.