SHARAƊI A CIKIN KASUWANCI:
𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu Alaikum, da fatar malam yana cikin ƙoshin lafiya. Mutum ne ya bani kuɗi in yi kasuwanci amma da sharaɗin duk wata ga abin da zan rinƙa ba shi, shin malam wannan ba riba ba ce? Allah ya saka wa malam da Gidan Aljannar Fardausi. Ameen.
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa Alaikumus Salaam Wa Rahmatul Laah.
Allah ya saka mana gaba ɗaya.
Malamai sun yarda cewa: Wani ya bayar da kuɗi, wani kuma ya riƙa yin kasuwanci, a ƙarshe kuma su riƙa raba ribar da aka samu da gwargwadon yadda suka yi sharaɗi tun farko a tsakaninsu daidai ne. Wannan ne suke kira:
MUDAARABAH.
Amma a irin wannan halin da ake tambaya a kansa,
inda ba a san nawa ne ribar da aka samu ba, sai dai kawai duk wata mai kuɗi ya riƙa zuwa yana karɓar wani adadi da
aka yi amince a kansa tun farko, ban san madogarinsa a shari’a ba. Musamman ma
da yake a cikinsa akwai cutarwa da takurawa ga mai gudanar da kasuwancin, domin
ai bai san ko riba za a ci ko kuwa faɗuwa za a yi a
cinikin wannan watan ba. Idan kuma mai kuɗin ya cigaba da
karɓar kuɗi duk wata, za a
wayi gari kenan uwar kuɗin da aka fara
kasuwancin ma da shi ya kare! Zai kuma iya yiwuwa a riƙa samun riba mai yawa a cikin kasuwancin ta yadda
mai kasuwanci ne zai cigaba da samun fa’ida, shi kuma
mai kuɗin zai riƙa cutuwa. A ƙarshe ya zo yana cizon yatsa.
Abin da ya fi dai kawai sai su zauna su sake
tsarin don ya dace da koyarwar addini. Ko da ɗaya bisa goma (1/10) na ribar ce mai kuɗin zai riƙa karɓa ya bar wa mai
kasuwancin tara bisa goma (9/10) ya fi daidai, insha’Allah. Ba za a ce wannan
riba ba ce. Abin dai da ya yikusa da wannan a babin riba shi ne abin da malaman
fiƙhu suke kira: RIBAL ƘARDI, watau: Riba na
Bashi. Shi ne mutum ya bayar da bashin da a ƙarƙashinsa zai samu wani amfani, kamar yadda suke cewa:
ﻛُﻞُّ ﻗَﺮْﺽٍ ﺟَﺮَّ ﻧَﻔْﻌﺎً ﻓَﻬُﻮَ ﺭِﺑﺎً
Duk bashin da ya janyo amfani, to riba ne.
Sai dai kuma a fili yake cewa wannan ba bashi ya
bayar ba, yarjejeniyar ciniki ce ba a ajiye ta yadda ya dace ba.
Wal Laahu A’alam.
Muhammad Abdullaahi Assalafiy
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku
kasance damu cikin wannan group domin Fadakarwa...
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.