𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Yaya matsayin auren Wanda ya musulunta? Shawara nake nema , mene ne mahangar malam akan Hakan? Na gode.
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Ai a musulunci babu wani fifikon daraja tsakanin
wanda ya tuba ya shigo musulunci da kuma wanda aka haifa acikin addinin. Kamar
yadda kuma babu fifikon da wasu ke dashi akan wasu saboda garinsu ko Ƙabilar da suka fito.
Kamar dai yadda kika sani, ana samun girma ne ta dalilin fifikon tsoron Allah.
Don haka halayensa za ki duba, da kuma irin rikon
da yake yiwa addinin musuluncin. Idan kin gamsu da halayensa da rikon addininsa
shikenan ki bashi dama ya turo mutanensa. Amma idan baki gamsu da halinsa ko
rikon addininsa ba, kada ki yaudareshi ta hanyar cin kuɗinsa. Gwanda ki sallameshi da wuri ki fito ki gaya masa
gaskiya.
Wannan ita ce shawarata kuma ina tayaki addu'ar
Allah ya zaba miki miji nagari.
WALLAHU A'ALAM.
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku
kasance damu cikin wannan group domin Fadakarwa...
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.