𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu alaikum Malam akwai wani bawan Allah ɗan iska da yake ɓata min suna a wurin jama'a cikin unguwa. Wallahi yanzu duk yawancin mutane ya haɗa Ni dasu. Kuma wallahi tallahi babu laifin dana yi masa. Shine na yanke shawara yadda ya yi min wannan abin wallahi sai na yi duk yadda zanyi nasa mutane sun tsane shi. Nidai yanzu bani da wani makiyi sama da shi a duk duniya. Malam wai don Allah mi yake damun mutane da zarar an faɗa musu magana basa bincike kawai sai su hau su zauna. Wallahi tallahi har na yanke shawarar yiwa matsiyaci asiri na bakin-jini gun al'umma.
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa alaikumus salam wa rahmatullahi wa barakatuhu.
Wannan laifin da kake zargin wancan mutumin ya
aikata maka, idan har ya aikata ɗin to tabbas ya
chutar dakai kuma ya chutar da kansa. Domin sunan wannan laifin 'Annamimanci'
kuma Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam Ya ce "MAI ANNNAMIMI BAZAI
SHIGA ALJANNAH BA". (Bakhariy hadisi na 5,056. Muslim hadisi na 106. Abu
Dawud hadisi na 4,871. Tirmidhy 2,026).
Acikin wani hadisin kuma wanda Imamu Ahmad ya
riwaito ta hanyar Sayyidah Asma'u bnt Yazeed bn Sakan (radhiyal-Lahu anha), ta
ce Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam Ya ce : "(Kuna so) in baku
labari game da mafiya alkhairin cikinku?' Sune waɗanda idan an gansu akan tuna Allah".
Sannan sai ya sake cewa : "Shin in baku
labari su waye mafiya sharrin cikinku?" Sune masu yawo da Annamimanci,
masu ɓata tsakanin masoya, masu ɗora laifi ga ku'butattun mutane". Aduba : Musnadu
Ahmad juzu'i na 6 shafi na 459 da Sunanu ibn Maajah hadisi na 4119).
Don haka kada ka tada hankalinka bisa miyagun
kalamai da Ƙaskanci ko
mummunar mu'amalar da kake riska daga mutane. Kayi hakuri ka jure, ka gyara
mu'amalarka da Mahaliccinka. In sha Allahu Ubangiji shi zai wankeka tsaf daga
kowanne irin mummunan zaton da mutane ke yi maka, mutukar ka gyara tsakaninka
dashi (SUBHANAHU WA TA'ALA).
Amma dangane da maganar da kakeyi cewar wai zakaje
kayi masa asirin bakin-jini (wato karfa) idan kayi haka za ka kai karshe wajen
zubar da kimarka awajen Allah. Domin kuwa shi sihiri yinsa kafirci ne. Kuma duk
wanda ya yishi, to bashi da sauran rabo awajen Allah. Kuma yana daga cikin
zunuban nan guda bakwai mafiya girman laifi kuma masu saurin hallakarwa.
Imamu Ahmad bn Hanbal da wasu daga cikin maluman
magabata suna ganin cewa duk wanda ya yiwa wani mutum asiri, to ya kafirta.
Ma'ana ya bar musulunci.
Al Hafiz Ibnu Katheer acikin tafsirinsa kan ayah
ta 102 ta suratul baƙarah ya kawo cewar "Sarkin Muminai Umar ɗan khattabi ya rubuta (zuwa ga gwamnoninsa) cewa "KU
KASHE DUK WANI MATSAFI DA MATSAFIYA".
Wanda ya ruwaito hadisin ya ce "Sai muka
kashe wasu matsafa guda uku".
Ya ce Imamul Bukhariy ma ya riwaito acikin
sahihinsa, hakanan ya inganta cewa Nana Hafsatu Uwar muminai (radhiyal-Lahu
anha) wata baiwarta tayi mata asiri sai ta sanya aka kasheta.
Kuma Imamu Ahmad ya ce hadisai sun inganta daga
Sahabban Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam cewa haddin matsafi shine a
kasheshi da takobi".
Kaji tsoron Allah kada ka rama mugunta da mugunta.
Kuma kada ka rasa imaninka wajen yin ramukon gayya. Kayi masa afwa ka barwa
Allah zai maka sakayya aduniya da lahira.
WALLAHU A'ALAM.
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.