Ticker

6/recent/ticker-posts

Ya Auri Bazawara Ashe Tana Da Ciki

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Assalam alaikum malam dan Allah ina neman fatawa Akan wani aure. Wani bawan Allah ne ya auri bazawara bayan aure da kwana shida sai take laulayi ana dubawa aka ga cikin sati bakwai 7 inda ta yi rantsuwa batasan da cikin ba tasan dai tsohon mijinta ya yaudare ta da cewa zai maida ita ya yi lalata da ita. A yanzu haka ta saka iyayenta da dangi cikin Hali domin kunyar abin da ta iya bayyana sannan shima mijin haka. Malam tambaya ta ta farko shin za su iya zubarda wannan cikin kasancewar sati bakwai ne? Sannan za su iya ci gaba da auren domin rufin asirin iyayen da dangin idan mijin ya amince? Allah yasaka da alkairi.

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Wa alaikumus salam wa rahmatullahi wa barakatuhu.

Tabbas wannan abun akwai rikici mai girma cikinsa. Sai dai in sha Allahu akwai hanyoyi kamar guda biyu da za a iya binsu domin warware sarkakiyar dake cikin lamarin.

Kafin mu shiga cikin maganar warware sarkakiyar, dole ne mu kalli shi wannan sabon auren amatsayin cewa "BAI ƊAURU BA". Wato ka'idar ita ce Duk auren da aka ɗaura alokacin da mace take cikin iddah ko take ɗauke da juna biyu, to ba aure bane.

Don haka wannan mutumin ba mijinta bane. Sai dai ayi kokarin bin hanyar da komawarta gidan farko za ta tabbata.

Hanya ta farko ita ce, mu yi aiki da fatawar Mazhabin Imam Abu Hanifah wanda ya ce "Namiji yana iya mayar da matarsa ta hanyoyi ne guda biyu. Kodai ya gaya mata da bakinsa ko arubuce, ko kuma ya mayar da ita a aikace (wato yaje ya yi kwanciyar aure da ita).

To idan dai wannan saduwar da ya yi da ita, alokacin ba ta Qare iddah ba, to za a ɗauki wannan amatsayin kome ne (wato kai tsaye ya mayar da aurenta tunda har ya sadu da ita). Don haka sai ta kwaso kayanta daga gidan wannan mutumin na biyu, to mayar dasu gidan mijinta na farko.

Idan kuma ta riga ta yi iddah alokacin da ya sadu da ita, to duk da haka dai za a iya jingina abin da ta haifa izuwa gareshi idan har ya yarda kuma ya amince, amma abisa wata fatawa daga magabata na kwarai irin su Imam Hasanul Basariy da kuma wasu daga cikin Maluman Musulunci kamar Shaikhul Islam Ibnu Taimiyyah (Sun ce idan har mazinaci ya amince cewar shi ne ya yi mata ciki kuma ya yarda cewa duk abin da ta haifa nashi ne, shikenan za a jingina yaron izuwa gareshi).

Su kuwa iyaye, dole ne su ajiye son rai su dawo subi abin da addini ya fada, koda kuwa bai zo daidai da son ransu ba. Bai halatta a zubar da wannan cikin ba, domin zubar da ciki haramun ne sai dai idan akwai wata larura wacce shari'ah ta yarda da ita. Wannan kuwa ba larura bane.

WALLAHU A'ALAM.

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

WALLAHU A'ALAM.

https://t.me/TambayaDaAnsa

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam 

Post a Comment

0 Comments