𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu alaikum Fatan alkairi Malam ya matsayin sakin mace amusulnci ta waya yake? ni atunanina saki yana afkuwane ta wajan furtashi ko shedar ta takarda Dan Allah adinga tunatar da maza wajan saki ta waya ni aganina sakin wulakanci ne tunda ba ta waya ake ɗaura musu aure da mata ba yakamata malamai sudunga Jan hankalin maza akan haka inda ba hakan yananufin daidai bane nice ban fahimta ba Allah ya sa mu dace
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa Alaikis
Salaam: Kin Saku, Kuma Saki ya tabbata, Sa'annan ai bawai Malamai su dinga yiwa
maza Nasiha ko tunatarwa bane akan wannan, Bari na Gaya Miki duk wannan Laifin
ku ne Mata domin ku ne kuke kawo Mazan ku ce Kun ji Kun gani duk duniya babu
wadda kike so sai shi.
Dalilin shi
ne ai duk Namijin da ya San Darajar Mace, ya San Kimar ki, ya San Mutuncin ki,
ya Martabatan ki, ya San Addinin sa, ya sa tsoron Allah a ran sa, yana ganin
Girman Allah da Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam, ya San Darajar Iyayen
sa da na Matar sa, ya San Mene ne Aure, toh wallahi Bari na Gayaiki ba zai taɓa Sakin Mace a irin
Haka ba, ba tare da Shedun Waliyyin ki da Shedun Waliyyin Sa, ko Kuma Wani
Sheidar wani mutum Mai Mutunci da kima ba. Dole Sai ya nemi Waliyyin ki ko
Waliyyin Sa, ko shaidar wani Mai Mutunci ya ce zai sake Matar sa, ya rubuta
Takarda a gaban sa a tura Miki shedar, Kuma wata kila a dalilin Kawo maganar a
gurin Waliyyin ki ko Waliyyin sa ko wani sheda akan cewa zai Sake ki, toh idan
shedar ya yi Masa Nasiha ya tunatar da shi, sai ki ga ya Fasa Sake ki ya yi amfani
da abun da aka tunatar da shi. Amma Samarin yanzu Auren kawai ake yi amma ba a san
mene ne Dokokin Aure da Hukunce-Hukuncen saki ba, sa'annan ba su San Darajar ki
ba, dole ne a yi sakin da ake yi a Shirin Films domin an ɗauka wasa ne an
mayar da Auren kamar dai yadda ake yi a Fina-Finan Hausa.
Sa'annan
bayan ya Sake ki Yana dakyau a Ka'idar Shari'ar Musulunci ya Miki wani Isani,
wato ya ɗauki Kuɗi ya ba ki kyauta,
ya Siya Miki Suturar Sakawa ya ba ki, abun da Za ki Rika Ci kina Sha har iya
Wadda zai ɗauke ki na Wasu Watanni zuwa gama iddar ki, ba tare da
kin daga Hankalin ki ko kin Fara bin maza ba, in dai mutum yana da hali abun da
Shari'ar Musulunci ya ce kenan amma idan babu shikenan ya sake ki a cikin
Mutuncin kamar yadda na yi bayani a sama. Shin Samarin Yanzu suna yin Haka Idan
sun saki Matar su? Amma kuma idan an taɓo ku sai ku Ce Suna son ku Suna Kaunar Ku kamar za su
Mutu, Kuma duk Wadda yake son Abu yake Kaunar Abu ba zai Yi irin yadda Kika ce
ba.
Kai idan ma
Mijin Yana da Hali wato Mai Arziki ne shi, zai ba ki harda Kyautar Gida da
Motar shiga, idan ba Mai Arziki bane toh zai Miki Isani irin yadda nace a sama
bawai Dole bane sai an Miki, Amma Yana dakyau idan Miji ya sake Matar sa ya bi
irin wannan Tsarin na Shari'a.
Toh Amma ke
kin je kin Auri Namijin da Bai San Komai ba a rayuwar da sai kawai ya yi Jima'i
da ke ya ji daɗin ki Bukatar sa ta biya, don Haka ne ma ya Auro ki, Bai
San Darajar Mace ba, Bai San Kimar Mace ba, Bai San Mutuncin Mace ba, Bai San
Martabatan Mace ba, Uwa Uba Bai San Girman Allah da Manzon Allah Sallallahu
Alaihi Wasallam, Bai San Mutuncin Waliyyin Sa ba, Bai San naki ba, Bai san
Darajar Iyayen ki ba, Bai San Naki ba, Bai San Dokakin Sakin Mace ba, Bai San
hukunce-hukuncen Aure ba, Shin Yaya ba zai Sake ki ta yadda yake so ba a Ransa
ba??
Wallahi duk
Namijin da ya San waɗannan abubuwan ba zai Sake Mace irin yadda Kika ce ba,
Amma Wadda bai san su ba, ai Dole ne ya yi irin wannan Sakin fiye da hakan ma,
ai kema kin San me Kika Aura, inda a Lokacin Za a ba ki Shawara ace ki bar shi
kada ki Aure shi, zai Zo ya Miki irin wannan Sakin, da Wadda ya ba ki Shawarar shi
ne abokin Gaban ki, toh yanzu ga shi ta faru.
Don Haka Ni
a ganina laifin ku ne Mata domin Kun San me kuke Aurowa su Zama Mazajen ku,
yanzu Haka inda ace Za a tara Samari masu yin Aure, ace idan ka sake Matar Ka,
sai kayi mata Isani zaka ba ta kuɗi da siya mata Suturar Sakawa da Sauran su, da za su yi
ta mamaki Sabon Hadisi ya zo, domin ba su san ma ana Yi ba Kuma ba su yin Haka.
Kina Gaya
musu za su ce an kawo Sabon Addini Amma a gurin Wadda ya San me yake Yi, shi ya
San ba Sabon Addinin bane.
Samarin
kawai sai dai suyi Aure amma ba su San Darajar Waliyyan su ba, kuma Allah ya
sanya Waliyyin ki da Waliyyin sa domin su zama garkuwa ne gare ku duk wani abun
da zai faru a tsakanin ki da shi, toh dole ne Waliyyin sa ko naki su ji
sa'annan su zo suyi muku Silhu da Nasiha, idan abun ya gagara su Waliyyan da
kansu za su bayar da shawarar a rabu, amma kuma duk wadda ya san Darajar
Waliyyin sa da naki wallahi ba zai taɓa Kunya ta su ba duk abun da suka gaya masa dole ne ya
gyara, kema duk abun da suka gaya miki dolen ki ne ki gyara, toh amma da yake
ke da Mijin gaba ɗayan ba a Darajar Waliyyin Aure ba shiyasa komai zai iya
faruwa.
Wata ma
wallahi a yanzu haka tafi shekara 10 ko 5 da yin Auren amma idan kin tambaye ta
waye Waliyyin ta da Waliyyin Mijin ta? za ta ce ba ta San su ba, haka shima
Namiji da za ki tambaye shi waye Waliyyin sa da Waliyyin Matar sa zai ce bai
sani ba, don Allah an San Darajar Aure kenan? Ai dole ne in dai Miji me tsoron
Allah ne dole ne ya San Waliyyin ki da Waliyyin sa, kema haka dole ne ki san su
sa'annan a rika girmama su, domin haqqin Auren ku yana kansu dolen su Allah zai
tambaye su akan zamantakewar Auren ku, amma wani zai Sake Matar sa babu wadda
zai sani, wani zai yi ta kuntatawa Matar sa Waliyyan ba su sani ba ko sun sani
amma Mijin ya fi Karfin su, sabida haka a ji tsoron Allah a san wanne irin Miji
za a Aura a rayuwa. Allah ya shirya dafatan kin gane Koh???
WALLAHU
A'ALAM
Zauren Fatawoyi
Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.