𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu alaikum mene ne hukunci sanya niqab a musulunci shin wata daga cikin matan Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam) ko matan magabata sun sanya niqab ɗin kuma sunna ce ko farilla?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa'alaykumus-Salam.
Niqabi shi ne macce ta rufe fuskarta duka ya zamana ba a ganin komai a fuskarta
sai kwayar idanunta kawai.
An samo daga
Nana Aisha (RA) ta ce Mun kasance a wajen aikin Hajji tare da Manzon Allah
Sallallahu Alaihi Wasallam idan mahaya suka zo wu cewa ta wajen mu sai mu saki
Niqabin mu, mu rufe fuskarmu, idan sun wuce sai mu buɗe fuskarmu. (Imamu
Buhari ya ruwaito shi).
Haka kuma
Nana Asma'u 'yar Abubakar (RA) ta ce, Mun kasance muna rufe fuskarmu daga maza
kafin haka a wajen aikin hajji ba ma rufewa. (A duba a Sahih Buhari).
Imamu
bayhaqi ya ruwaito hadisi na 93 daga Asim dan Ahwal ya ce, "Mun kasance
muna shiga wajen Hafsatu 'yar Sirin wadda ta haddace Qur'ani tana da shekara
goma sha-biyu, ta mutu tana da shekara saba'in. Idan muka shiga sai ta ja
Jilbab dinta ta rufe fuskarta da Niqabinta.
Kenan ansamu
daga wasu mata masu daraja suna rufe fuskokinsu. Sai dai Malaman Musulunci sun
kasu kashi 2 game da hukuncin Sanya Niqabin wasu suka ce, SUNNA CE wasu suka ce
SUNNACE MUSTAHABBIYA.
Wajibi Ne
(Dole ne mace ta rufe fuskanta).
A Mazhabar
Shafi`iyya da Malikiyya, da Hanabila sun tafi kan cewa fuskar mace al'aura ce
kuma dole ne ta rufe fuskarta wajibi ne, buɗe fuska haramun ne.
Mazhabar
Hanafiyya kuma suka ce fuskar mace ba dole ba ne ta rufe fuskarta ya halasta ta
buɗe fuskarta In dai
ba a tunanin faɗa wa cikin fitina. In an tabbatar ana lokacin aminci to
ba komai tana iya buɗe fuskar ta.
An taɓa tambayar Sheikh
Nasiruddeen Albany hukuncin rufe fuskar mace, sai ya ce, Ba musan wani daga
cikin sahabbai ba wanda ya ce dole ne mace ta rufe fuskarta, Sai dai abin da
yake mafifici shi ne mata su rufe fuskar su shi ya fi mutunci. Amma mu ce
wajibi ne bai dace wani mutum ya ce wajibi ne ba.
WALLAHU
A'ALAM.
Ku Kasance
Damu Cikin Wannan Group Domin Ilimantarwa Tare Da Fadakarwa a Sunnah.
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.