Ticker

6/recent/ticker-posts

Hukuncin Sanya Niqabi

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Assalamu alaikum mene ne hukunci sanya niqab a musulunci shin wata daga cikin matan Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam) ko matan magabata sun sanya niqab ɗin kuma sunna ce ko farilla?

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Wa'alaykumus-Salam. Niqabi shi ne macce ta rufe fuskarta duka ya zamana ba a ganin komai a fuskarta sai kwayar idanunta kawai.

An samo daga Nana Aisha (RA) ta ce Mun kasance a wajen aikin Hajji tare da Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam idan mahaya suka zo wu cewa ta wajen mu sai mu saki Niqabin mu, mu rufe fuskarmu, idan sun wuce sai mu buɗe fuskarmu. (Imamu Buhari ya ruwaito shi).

Haka kuma Nana Asma'u 'yar Abubakar (RA) ta ce, Mun kasance muna rufe fuskarmu daga maza kafin haka a wajen aikin hajji ba ma rufewa. (A duba a Sahih Buhari).

Imamu bayhaqi ya ruwaito hadisi na 93 daga Asim dan Ahwal ya ce, "Mun kasance muna shiga wajen Hafsatu 'yar Sirin wadda ta haddace Qur'ani tana da shekara goma sha-biyu, ta mutu tana da shekara saba'in. Idan muka shiga sai ta ja Jilbab dinta ta rufe fuskarta da Niqabinta.

Kenan ansamu daga wasu mata masu daraja suna rufe fuskokinsu. Sai dai Malaman Musulunci sun kasu kashi 2 game da hukuncin Sanya Niqabin wasu suka ce, SUNNA CE wasu suka ce SUNNACE MUSTAHABBIYA.

Wajibi Ne (Dole ne mace ta rufe fuskanta).

A Mazhabar Shafi`iyya da Malikiyya, da Hanabila sun tafi kan cewa fuskar mace al'aura ce kuma dole ne ta rufe fuskarta wajibi ne, buɗe fuska haramun ne.

Mazhabar Hanafiyya kuma suka ce fuskar mace ba dole ba ne ta rufe fuskarta ya halasta ta buɗe fuskarta In dai ba a tunanin faɗa wa cikin fitina. In an tabbatar ana lokacin aminci to ba komai tana iya buɗe fuskar ta.

An taɓa tambayar Sheikh Nasiruddeen Albany hukuncin rufe fuskar mace, sai ya ce, Ba musan wani daga cikin sahabbai ba wanda ya ce dole ne mace ta rufe fuskarta, Sai dai abin da yake mafifici shi ne mata su rufe fuskar su shi ya fi mutunci. Amma mu ce wajibi ne bai dace wani mutum ya ce wajibi ne ba.

WALLAHU A'ALAM.

Ku Kasance Damu Cikin Wannan Group Domin Ilimantarwa Tare Da Fadakarwa a Sunnah.

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

WALLAHU A'ALAM.

https://t.me/TambayaDaAnsa

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam 

Post a Comment

0 Comments