TAMBAYA (253)❓
Assalamu
alaikum Warahmatullahi Wabarakatuhu
Wani mushriki ne ya mutu jiya a nan kasar NIGER, ya shahara da tsibbace - tsibbace, gashinan an kawo shi cikin masallachi, shin ya halatta mu yi masa Sallar Gawa sannan mu yi masa addu'a?
AMSA❗
Waalaikumus
Salam Warahmatullahi Wabarakatuhu
Baya halatta
a yiwa mushriki Sallah
Idan kun yi
masa Sallah a rashin sani ba laifi amman idan mutum ya sani to yana da laifi
Domin kuwa
munada nassi:
( مَا كَانَ
لِلنَّبِيِّ وَالَّذِينَ آمَنُوا أَن يَسْتَغْفِرُوا لِلْمُشْرِكِينَ وَلَوْ
كَانُوا أُولِي قُرْبَىٰ مِن بَعْدِ مَا تَبَيَّنَ لَهُمْ أَنَّهُمْ أَصْحَابُ
الْجَحِيمِ )
التوبة (113) At-Tawba
Bã ya kasancẽwa ga Annabi da waɗanda suka yi ĩmãni, su yi istigifãri ga mushirikai, kuma kõ dã sun
kasance ma'abũta zumunta
ne daga bãyan sun bayyana a gare su, cẽwa lalle ne, sũ, 'yan Jahĩm ne.
To in dai
baya kasancewa a nemi yafiya ga Kafirai to Ina Kuma ga ayi Masa Sallah idan ya
mutu
Don haka in
dai ya mutu ne yana wannan harkar ta duba a matsayin sa na "ar-Raf"
kamar yanda Annabi ya fada a cikin Sahihul Muslim to makomar sa Jahannama ce
kamar yanda Allaah Azzawajallah ya fada a cikin waccan ayar
Muna zaune
da irinsu a anguwanmu
Sannan kuma zan
yi amfani da wannan damar don jan hankalin mutane su guji bibiyar wani
qasurgumin boka da ake Kira da Malam Zaki, yananan a media platforms yana ta
dulmiyar da mutane. Sannan a jawa mutane irinsu Musa Mai Sana'a kunne da su
dinga fadakar da mutane illar bibiyar bokaye
Ya Allaah ka
rabamu da Yan Duba da Yan Tsibbu da Yan bugun Kasa da Yan Gobe da Nisa da
Astrologers da sauransu
Ya Allaah ka
tsare imaninmu ka dauki ranmu Muna Muminai la'akarida kowanne mumini musulmi ne
sai dai ba kowanne musulmi bane mumini
Allaah ka
zabemu cikin Muminai masu gadon birnin Aljannah kamar yanda ya faɗa:
( الَّذِينَ يَرِثُونَ
الْفِرْدَوْسَ هُمْ فِيهَا خَالِدُونَ
)
المؤمنون (11)
Al-Muminoon
Waɗanda suke gãdõn
(Aljannar) Firdausi, su a cikinta madawwama ne.
Wallaahu
taala aalam
Masu bukatar
shiga Telegram Class na littafin "KURA KURAI 100 A CIKIN SALLAR MU",
ku shiga Telegram kuyi searching:
USMANNOOR
ACADEMY
Amsawa:
Usman
Danliti Mato (Usmannoor_Assalafy)
Zauren
Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.