TAMBAYA (252)❓
Assalamu
alaekum Ina wuni malam ya ibada Allah yakarba mana
Mallam don Allah Ina Neman shawara ne nasamu scholarship domin yin karatun degree a saudiya kuma tafiyan baxae wuce cikin shekarar nan ba insha Allah amma Matsalar shi ne Ina karatu a nan Nigeria har na Kai 300 level shekara daya ya rageman nagama shi ne nake Neman shawara malam miye yakamata na yi gashi kuma Idan nace nabari nagama karatu na a nan xan yi missing wancan opportunity din don Allah abani shawara malam nagode asha ruwa lafiya.
AMSA❗
Waalaikumus
salam
Masha Allaah
Da farko dai
na tayaka murna domin kuwa wannan dama ce babba wadda ba kowa bane yake samunta
Idan mutum
ya tsinci kansa a wannan yanayin ba abin da yafi cancanta ya yi sama da bawa
Allaah zabi ta hanyar yin Istikhara
Sannan kuma
abu na biyu shi ne
Ka duba ka
ga tunda al'amuran sun shigo cikin shekara guda ne to sai ka duba yaushe zamu
tafi Saudiyya din ?
Shin zamu
tafine a lokacin da muka yi graduation a level 400 ?
Shawarar da
zan baka anan ita ce
Ka yi
Istikhara din sannan kuma idan ya rage sauran kwanaki kadan ku kammala karatun
alhalin tafiyar za ta tabbata ne kafin ku kammala to sai ka je ka samu
Department naku ka nemi alfarmar su akan ba ka son wannan damar ta subuce maka
Idan suka ce
ba za su iya ba
Sai ka
garzaya Faculty
Suma idan
suka ce ka hakura sai ka tafi Admin na Jami'ar ka ce a baka appointment da VC
akan wani emergency issue
Idan nan ma
ka ga an ki baka damar haduwa da shugaban jami'ar sai ka dinga ware lokacin da
yake zuwa office
Kana ganinsa
sai kayi sauri ka sameshi ka ce masa ga issue din da ya taso kuma Allaah ne
kadai zai kawo maka mafita kuma ta dalilin sa
Ka girmama
shi
In sha
Allaah zai baka lokacin da za ku tattauna
Daganan
tunda an samu shugaban Jami'ar to in sha Allaahu za a samu mafita
Mu kaddara
ya rage maka lokacin da zaka kammala level 400 din cikin alfarmarsa, to Alhamdulillah
haka ake so
Amman idan
shima yace sai dai ka zabi guda daya
To shawara
ta anan shi ne ka zabi zuwa Saudiyya din
Hujja:
Ina maka
kwadayin falalar dake cikin sahihin hadisin da Annabi (Sallallahu alaihi
wasallam) ya ce: "Yin sallah a Masallachin Ka'aba ya fi falala sau 100,000
akan kowanne masallachi sai dai Al-Masjid An-Nabawi wanda shi kuma za ka samu
ladan sallah 1,000 akan kowanne masallachi wanda ba shi ba"
Ko da ace
inda zakaje karatun ba Jami'atul Islam dake Madinah bane amman dukda haka
kusancinka da can yafi nan (Nigeria) kuma akwai yiwuwar za ka samu damar sauke
farali na aikin Hajji ga kuma bonus na Umrah
Wallaahu
taala aalam
Masu bukatar
shiga Telegram Class na littafin "KURA KURAI 100 A CIKIN SALLAR MU",
ku shiga Telegram kuyi searching:
USMANNOOR
ACADEMY
Amsawa:
Usman
Danliti Mato (Usmannoor_Assalafy)
Zauren
Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.