Citation: Adamu, Y.I. (2024 Waƙoƙin Siyasar Jam’iyyu a Nijeriya: Taƙaitaccen Sharhi Kan Jigo da Salo. Ginshiƙin Nazarin Salon Waƙoƙin Hausa, 478-486. www.doi.org/10.36349/djhs.2024.v03i01.059.
WAƘOƘIN
SIYASAR JAM’IYYU
A NIJERIYA: TAƘAITACCEN SHARHI KAN JIGO DA SALO
Yunusa
Ibrahim Adamu
Cibiyar
Nazarin Hausa, Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo, Sakkwato
Tsakure:
Manufar wannan bincike
ita ce, fayyace irin gudummuwar da marubuta waƙoƙin siyasa suka bayar wajen bunƙasar
siyasar jam’iyyu a
Nijeriya. An yi amfani da sharhantaccen bincike (Qualitative Method) wajen gina
wannan aiki. Haka kuma, an ɗora
wannan bincike a kan ra’in muhimmancin Rubutacciyar Waƙa, (Theory of
Appreciation on Hausa Written Poetry) wanda Farfesa Ɗangambo (2007) ya assasa,
musamman ɓangaren da
ya yi magana a kan jigo da hanyoyin binciko manya da ƙananan jigogi a
Rubutacciyar waƙa.Da kuma salo da sarrafa harshe.A wajen tattaro bayanan
wannan bincike, an yi amfani da hanyoyi da dama waɗanda suka haɗa
da; ziyartar marubuta waƙoƙin siyasa. Da tattaunawa da su domin jin bayanin yadda suka ɗauki waƙoƙin
siyasar jam’iyyu. An
yi bitar matanin waƙoƙin a rubuce domin a samu damar ƙalailaice jigon siyasa a cikinsu.
Binciken ya gano cewa da yawan marubuta waƙoƙin siyasar jam’iyyu na ƙasar Hausa, sun fi shahara a kan abin da
ya shafi siyasar aƙida, a wasu lokutan sukan yi amfani da dabarun jawo hankalin
masu sauraron waƙoƙinsu wajen yin karin magana da zambo da habaici domin kushe
abokan adawar siyasa, da kushe jam’iyyarsu
duk domin masu zaɓe su
ƙaurace
mata, da kuma cusa musu ra’ayin
riƙau
na kishin jam’iyya da
rashin tsaro a kan duk abin da ya taso. A ƙarshe binciken ya gano cewa, marubuta waƙoƙin
siyasar jam’iyyu sukan
yi amfani da salon kamantawa da kwatantawa da siffantawa da jinsintarwa da
mutuntarwa da dabbantarwa dakambamawa da alamtarwa duk a cikin waƙoƙinsuna
siyasa. Haka kuma, binciken ya lura da
wasu Jigogi da su keamfani da su. Irin waɗannan
jigogi sun haɗa da na
yabo da zuga ta hanyar bayyana manufofin jam’iyyu da na tallata ayyukan raya ƙasa na
gwamnati..
Fitilun Kalmomi: Waƙoƙin
siyasa, Jam’iyyu,
Jigo, Salo, Nijeriya
Gabatarwa
A cikin wannan takarda an yi
nazari ne a kan waƙoƙin siyasa da yadda suke da kuma yadda suke bayar da gudummuwa
ta fuskar kafa gwamnati da takara da lashe zaɓe
da adawa da farfaganda da yarfe na ‘yan siyasa daga jam’iyyu daban-daban tun
daga lokacin da aka samu ‘yancin kai daga Turawan Ingilishi, da irin gudummuwar
da waƙoƙin
siyasa suke bayarwa tun daga jamhuriya ta farko har zuwa yau ɗin nan. An ɗauki wasu daga cikin irin
waɗannan waƙoƙi na
siyasa daga jam’iyyu daban-daban an yi nazarinsu daki-daki, domin samar da
muhimman bayanai game da waƙar, da jigo da salon da mawaƙin ya yi amfani da shi wajen isar da saƙonsa
ga ‘yan jam’iyyarsa. Kafin nan, an duba ma’anar waƙa daga masana daban-daban
domin fito da irin gudummuwar da marubuta waƙoƙin siyasa kan bayar.
1.1 Ma’anar Waƙa
Yahaya (1997:1) ya ce“Ita kanta
kalmar waƙa
a wuirn waɗansu
musamman mawaƙa ta rabu zuwa sassa biyu (2) da aka kira waƙa da
waƙe,
kuma kowacce kalma daga cikinsu ma’anarta daban da ta ‘yar’uwarta. Waƙe a
ganin wasu shi ne rukunonin waƙe da suka danganci addini, wanda muhimman
abubuwan da waƙe suka ƙunsa su ne, wa’azi da madahu (yabo) da furu’a (fiƙhu) da
makamantansu. Daga ɓangaren
da wasu ke kira waƙa ya shafi jigogi baduniya kamar yabon wani mutum domin abin
duniya, wataƙila
mulki ko dukiya ko shahara a ɓangaren
siyasa ko jaruntaka da makamantansu.
To amma, a wurin mawaƙa wato
waɗanda suke mayar da
kiɗa sana’a, an sami
rarrabuwar ra’ayi har kashi 2. A cikinsu akwai masu tunanin waƙa a
matsayin tarin kalmomi da aka ƙuƙƙulla cikin azanci, kuma masu amfani da
kiɗa.
Wasu kuma sun ce waƙa
magana ce da ke zuwa cikin wani tsari kuma a rera, sannan ga saurin jan
hankalin mai sauraro. Haka kuma masana ta fannin ilimi da dama sun bayyana
ma’anar waƙa
kowa da yadda ya bayar da ma’anarta. Daga cikin su akwai:
Ɗangambo (1984:3) ya ce “Waƙa rera
ta ake yi kuma tana da tsari da sigogi har ma da ƙa’idoji na musamman”.
Ya ƙara da cewa, “Waƙa wani saƙo ne
da aka gina shi a kan tsararriyar ƙa’ida ta baiti, ɗango, rerawa, kari (bahari), amsa-amo (ƙafiya),
da sauran ƙa’idojin
da suka shafi daidaita kalmomi, zaɓensu
da amfani da su cikin sigogin da ba lallai ne haka suke ba a maganr baka ba”.
Gusau (1993:59) ya bayyana waƙar
baka da cewa “Daɗaɗɗiya ya ce wadda aka faro
ta tun lokaci daɗaɗɗe mai nisan gaske”.
Yahaya (1984:2-3) ya ce“Waƙa
maganar hikima ce da ake rerawa ba faɗa
kurum ba wadda ke da wani saƙo da ke ƙunshe cikin wasu kalmomi zaɓaɓɓu tsararru, kuma zaunannu”.
A ra’ayina ina ganin cewa: “Waƙa wata
dunƙulalliyar
magana ko furuci ne mai ma’ana cikin hikima da basira, wanda ake tsara shi
cikin azanci tare da rerawa,domin jan hankalin mai sauraro cikin wasu ƙa’idojin
da babu su a maganganun yau da kullum”. Na kafa hujja da waƙar da
Malam Tijjani Tukur Yola ya kawo game da ma’anar waƙa, inda yake cewa:
“Waƙa da zance dole ne a raba su,
Zance da ban waƙa ko ana tsarawa.
In za ka yo zance kana yin lura,
Waƙa kana yin lura ka zo ka kwatanta.
Sannan a zance babu tsari ɗas-ɗas,
Tamfar a waƙa
yadda za ka tsananta.
Zance a dokokinsa dai ganewa,
Waƙa kwa sai kogi yake kutsata.
Sannan akwai wasu ƙa’idoji
sosai,
Sauti da sauran ƙafiya
a kula ta.
Tijjani ne ya tsaya yake rabewa,
Domin a san waƙa a ko
gane ta.
Zance ko rarara a zan gane shi,
Sam babu sauti kun ji na nanata.
Tijjani Tukur Yola, 1976.
2.0 Ma’anar Siyasa
Kalmar siyasa ta samo asali daga
“al-siyasat” ta cikin harshen Larabci, kuma kalmar tana nufin shugabanci ko
jagoranci. Ɗiso
(1997:1-2).
Ga alama wannaan na iya zama
ma’anar kalmar ta kai tsaye ko kuma ta zahiri. Abin fahimta a nan, an bayyana
siyasa tamkar salo ko tafarki ko kumadabarun aiwatar da shugabancin jama’a, ba
hanyar hawa kan karagar mulki ba.
Bugu da ƙari akwai bayanai da
masana da masu bincike a kan ma’anar wannan kalma suka bayar daga cikinsu har
da Mashi (1986:41) wanda yake cewa waɗansu
mutane sun ɗauki
siyasa da cewa cin amana ce da butulci, wanda wannan ne ma ya sanya da zarar an
ambaci siyasa cikin mu’amala sai dattawa su zare jikinsu domin kuwa kalmar
kishiyar dattako ce. A nan kalmomin cin amana da butulci su ne suka nuna
bambancin wannanma’ana da wadda aka kawo a farko.
Haka nan, idan muka ƙara
yin nazarin wannan ma’ana tare da la’akari da yadda ake gudanar da siyasa a
yanzu, ba laifi ba ne, don an bayyana siyasa a matsayin jayayya ko yin gumurzu
da fafatuka da kuma tsayuwar mai daka kan meman wani abu da yadda za a kasafta
shi a lokacin da aka samu, kuma a ba wanda aka so.
Ɗiso (1997:1-2) yana cewa, “Siyasa tana
iya ɗaukar ma’anar
dabara da yaudara da sauƙi da sulhu da wayo da kuma ƙwarewa wajen iya hulɗa da jama’a”.
Masana daga ɓangaren koyar da siyasa ma
ba a bar su a baya ba, kuma ga ra’ayin wasu dangane da ma’anar siyasa.
Dahl (1950:1-5) cewa yayi,
“Siyasa hanya ce da akan bi don kafa hukuma kuma a gudanar da tsare-tsarenta
wannan na nuna siyasa tsari ce na shugabanci da tababtar da an kiyaye manufofin
wannan hukuma”.
Jega, (2005:223-224) yana mai
ra’ayin siyasa ta shafi jagorancin mutane da sarrafa albarkatun ƙasa
don ci gaban wannana al’umma.
Sa’id (2002:172) Yana ganin cewa
“Siyasa wata hanya ce ta gudanar da zaɓaɓɓiyar gwamnati ta hanyar
dimokraɗiyya a ƙarƙashin
tsarin mulkin ƙasa, inda za a zaɓi
shugabanni masu tafiyar da ita a ƙarƙashin ƙafafun wasu jam’iyyu”.
Ƙamusun Hausa (2006:397) ya bayyana
ma’anar siyasa da cewa “Tafiyar da al’amuran jama’a ta hanyar neman ra’ayinsu
da shawarwarinsu”.
A nawa ra’ayin na kalli siyasa da
cewa “Wani tsari ne na shugabantar al’umma a madafun iko daban-daban, ta hanyar
zaɓe, ko naɗi, sai dai zaɓen yakan kasance ɗayan biyu, ko dai ya zama
an kwatanta gaskiya ko kuma a yi ka ci baka ci ba, ko kuma baka ci ba ka ci”.
2.1 Ma’anar Waƙar
Siyasa
Yayin da ake ƙoƙarin
fito da ma’anar waƙa, galibi akan yi la’akari da wasu muhimman abubuwa da suka ƙunshi
tsararriyar ƙa’ida
ta baiti da ɗango da
kari da amsa-amo, wani lokacin da zaƙin murya da kuma kiyaye saurna ƙa’idojin
da suka saɓa da
maganar baka, kuma ana gabatar da waƙoƙin domin yaɗa
manufofi iri daban-daban, ciki kuwa har da siyasa. Dan haka da wannan wuri, za
a iya bayyana waƙar siyasa a matsayin wani furuci kan wata manufa da aka gina
ta hanyar amfani da keɓaɓɓun kalmomi a kan tsari da
ya bambanta da hanyoyin rubuta sauran nau’o’in adabi. Alal misali, a waƙar
“NEPU Sawaba” ta Gambo Hawaja Jos cikin Dokaji (1990) yana cewa:
“Jam’iyyan nan da an ka ce,
Wai ta NPC ta mace,
‘Yan halak duk tarkace,
Yanzu saurna sun fice,
Masu son danne gaskiya.
Muhimman kalmomin da ke nuna
wannan baiti cikin waƙar siyasa yake akwai ‘jam’iyya’ wadda ke bayyana taron wasu
mutane bisa aƙida ɗaya
ta yin mulki, sai NPC, wannan kuma suna jam’iyya ce da aka yi a jamhuriya ta ɗaya. Akwai ‘yar halak wadda
ke bayyana rukunin mutane na cikin jam’iyya da suka riƙe manufarta da gaskiya.
Ni kuma a ra’ayina na mai nazari
zan iya cewa waƙar siyasa, wani tsararren zance ne da ake tsara shi da niyyar
yabo ko kambamawa ko zuga ga waɗanda
zuciya ke so, da kuma yin zambo da habaici da gugar zana da hannunka mai sanda
ga abokan adawa.
2.2 Halayen Waƙoƙin
SiyasanaHausa
Waƙoƙin Hausa na siyasa suna da wasu keɓaɓɓun siffofi da suka bambanta su da suaran waƙoƙin Hausa.
Muhimman cikin waɗannan
halaye sune:
Bayanin manufofi da alamomin
jam’iyyu
Yabon shugabanni da fitattun
‘ya’yan jam’iyya
Yadda ake gudanar da siyasa.
Tallata jam’iyya don a zaɓeta
2.3 Ma’anar Jam’iyya
Jam’iyya na nufin wata ƙungiya
mai wakiltar wani ra’ayi na neman mulkin al’umma (Mashi 1986)
Haka kuma Ƙamusun Hausa (2006:212)
ya bayyana cewa “Jam’iyya na nufin wata ƙungiyar jama’a ta siyasa ko ta sana’a,
mai manufa iri ɗaya da
tsarin ƙa’idoji
da zaɓaɓɓun shugabanni”.
A ra’ayina, Jam’iyya na nufin haɗuwar wani rukuni na jama’a
da suka amince su tafi a kan ra’ayi ko manufa iri ɗaya, domin cimma wani buri nasu na neman
mulki”.
Waƙoƙin Siyasa a Nijeriya: Daga shekarar 1946 bayan ƙarewar
yaƙin
duniya nabiyu ne waƙoƙin siyasa suka fara kankama a Najeriya, inda ‘yan ƙasa
suka riƙa
yin aikace-aikace na siyasa” Gusau (1984:64) Waƙoƙin siyasa waƙoƙi ne da ake rubutawa,
domin bayyana abin da ake nufi da siyasar zamani da kuma ƙa’idojin
siyasar jam’iyyu. Haka kuma waƙoƙi ne da ake shiryawa da nufin yabon
shugabanni ko jam’iyyun siyasa daban-daban, da kuma yin suka ga abokan hamayya
na wasu jam’iyyun. Akan shirya waƙoƙin siyasa ne ta yadda za su isar da saƙon da
ake son su isar ga jama’a. Yahaya (1997:21)
Marubuta Waƙoƙin
Siyasa a Jamhuriyya ta farko 1960-1966
Mulkin Turawa ya zo ƙarshe
ranar 1 ga watan 10, 1960.Inda aka kafa jam’iyyun siyasa da suka samo asali
daga ƙungiyoyi.An samu jam’iyyun NEPU daga Arewa, sai NCNC daga
yankin Ibo daUNCP daga tsakiyar Nijeriya, sai kuma A.G daga yankin Yarabawa.
Mawaƙa irin su Gambo Hawaja da
malam Aƙilu
Aliyu da Mudi Sipikin duk sun gabatar da waƙoƙi da nufin kare jam’iyyunsu.Misali Alhaji
Mudi Sipikin ya yi wata waƙa mai suna ‘Murnar Karɓar
Mulki Kan Jihar Arewa ta Nijeriya. Inda yake cewa:
Bauta da zafi da ciwo da ɗaci, Ballantana har a ce ba mutunci, Kayanka an ƙwace duk shugabanci,
Yaya idan kana ka samu ‘yanci, Kayanka an ba su mulki nasa.
Abin da ya shekara sittin rabonmu,
Da shi yanzu yau ya zo gare mu,
Gidan nan Arewa ƙasar kakannimu,
Da can ƙaddara
ta taho ta rabab u,
Allahu yau ya yi iko nasa.
Mun samu kanmu yau ba wata illa,
Babu jinaya faɗa
ko su zilla,
Sai lafiya da aminci kamala,
Cikin haƙuri gaskiya da adala,
Kowa ya zauna da hujja tasa.
Idan har mutum ya zamo babu ‘yanci,
Ƙalata da yunwa da zafi da ƙunci,
Rashin lafiya kuma sanyi da kirci,
Yawan zazzaɓi
kuma sannan talauci,
Ga duk wanda ya rasa ‘yanci nasa.
A yau ga shim mun zama ‘ya’ya kamar da,
Mutunci da ‘yancinmu yau ba makida,
Aminci na sosai cikin fa’ida,
Yau ga shi mun soma samun sa’ida,
Mai hassada kuma kaito nasa.
Mudi Sipikin 1966.
3.1 Jamhuriya ta Biyu (1979
-1983)
Ranar 18 ga watan Janairun 1966
ne aka kawo ƙarshen
mulkin jamhuriyya ta farko,wanda sojoji suka yi a ƙarƙashin Manjo General
Johnson Thomas Aguyi Ironsi. A lokacin ne aka kawo ƙarshen mulkin siyasa a ƙarƙashin
dokar soja ta Deccree 33 of 1966, aka kuma haramta duk wata jam’iyyar siyasa,
sai dai daga baya, Sojoji sun yarda su bayar da mulki ga farar hula. A nan ne
jam’iyyun siyasa kusan 50 suka bayyana. Waɗanda
suka haɗa da Unity
Party of Nigeria (UPN) ta Chief Obafemi Awolowo, sai Nigerian People Party
(NPP) ta Waziri Ibrahim wanda daga baya ta koma GNPP, sai kuma People’s
Redemption Party (PRP) ta Malam Aminu Kano. Duk da yawan jam’iyyun siyasar da
suka fito a wancan lokacin, jam’iyyu biyar ne kacal suka samu damar tsallake
sharuɗɗan da gwamnati
ta kafa.Waɗannan
jam’iyyu sun haɗa da
UPN da NPP da GNPP da NPN da PRP. Daga baya kuma aka samu ƙarin
su NCNC wato National Congress of Nigerian’s and Cameroon, ta Dr. Nnamdi
Azikiwe, da NPN sai kuma PRP wadda ta zama NEPU ta fuskar aƙida.
Awannan jamhuriya an samu manya da ƙananan mawaƙan siyasa da suka waƙe
jam’iyyunsu, waɗanda
suka haɗa da Malam
Bello Giɗaɗawa wanda ya yi waƙar
siyasa lokacin salama, da Shekara Sa’ad wanda ya yi waƙar yabon Sardauna. Da
Malam Aƙilu
Aliyu da ya yi waƙar Tauraron zamani, sai Malam Gambo Hawaja Jos, wanda ya yi waƙar
‘Yan sawaba, da sauransu da dama. (Ɗangambo1984: 14)
3.2 Jadawalin Sunayen wasu
Fitattun Mawaƙan Siyasar jam’iyyun da suka yi waƙa a
jamhuriya ta biyu
S/N |
MAWAƘI |
WAƘA |
JAM’IYA |
1. |
Shekara Sa’ad |
Yabon Ahmadu Bello |
NPC |
2. |
Bello Giɗaɗawa |
Siyasar Zamani |
NPC |
3. |
Abdullahi mai Gwandu |
Yabon Sardauna |
NPC |
4. |
Mohd Giɗaɗo |
Yabon Sardauna |
NPC |
5. |
Aƙilu Alyu |
Tauraron zamani |
NEPU |
6. |
Aƙilu Aliyu |
Jiya da Yau |
NEPU |
7. |
Yusuf Kantu |
Ya Allah K aba mu Sawaba |
NEPU |
8. |
Gambo Hawaja |
Waƙar ‘Yan Sawaba |
NEPU |
9. |
Malami A. Yabo |
A zaɓi ‘yan Fi ‘yan |
NPN |
10. |
M.S. Ɗunɗaye |
‘Yan santsi kun zama ƙaya |
NPN |
11. |
Yakubu Labaran |
‘Yan santsi sun ji kunya |
NPN |
12. |
Musa Madugu |
Ya Allah K aba mu Aminci |
NPN |
13. |
Isah I. Bunguɗu |
Fi Ar Fi maganin zamba |
PRP |
14. |
Isah I. Bunguɗu |
Ɓarawon Akwatu |
PRP |
15. |
Magaji Sudawa |
Jam’iyyarmu ce PRP |
PRP |
16. |
Garba Gashuwa |
Ɗan hakin da ka raina |
PRP |
Kamar yadda kowa ya sani ne, ɗaya daga cikin irin
gudummuwar da waƙoƙin siyasa suke bayarwa sun haɗa
da tallata jam’iyyu da ‘yan takara da jawo hankalin masu zaɓe da kuma yin kushe ko
zambo ko habaici ko gugar zana ga abokan hamayya. Don haka, wanna takarda ta
duba wasu waƙoƙin
siyasa da aka yi a wannan jamhuriyya, da nufin yin tsokaci game da zambo da
habaici.
A waƙar ‘Yan Sawaba ta Gambo Hawaja
yana cewa:
Kai tunturmi jaki daƙiƙin
duniya,
Ƙaton cikin wofi na cinye haramiya,
Gemunka har sajenka ba su da
martaba,
In dai ya zam aikinka babu na
gaskiya.
(Gambo Hawaja a waƙar
Sawaba).
A baitukan da suka gabata, Gambo
Hawaja mawaƙin
NEPU ya yi zambo ga wani da ake zato Sardauna ne, inda yake siffanta shi da
wasu halaye na rashin adalci. Da yin wannan waƙar Gambo Hawaja bai ci ɓagas ba, domin kuwa Malami
A. Yabo na jam'’yyar NPN, ya yi masa raddi a cikin waƙar a zaɓi NPN, inda ya ce:
Na ji wanda ya tsara waƙar Nepuka,
Asalinsa Arne ne a Jos Sardauna.
Sunan Ubansa Aɓom
tsirara ma yake,
Goyon tsiraici jakunan Sardauna.
(Malami A. Yabo a waƙar ‘Mu
Zaɓi NPN)
Wannan ya nuna irin ɗauki ba daɗin da ake yi a tsakanin
mawaƙan
siyasa na wancan zamani, duk da nufin kare muradunsu na siyasa a jam’iyyunsu. A
wani misalin inda Malam Lawal Maiturare a cikin waƙar murna inda yake yi wa
‘yan jam’iyyar NPC, inda yake cewa:
Wasu sun je sun zo tuntuni,
Sun kasa bayani gaskiya.
Ba wakilai ne bana gaskiya,
Burinsu kashe Nijeriya.
A wannan baitin, Malam Lawan
Maiturare ya nuna irin yadda ‘yan jam’iyyar adawa da rashin gaskiya da kuma son
kasha ƙasar
ma baki ɗaya.
Shi ma Malam Aƙilu
Aliyu ya yi irin wannan zambon inda yake cewa:
Aikinsu kamar rawaninsu yake,
Ɗaure-ɗauren
banza ba nazari.
Akwai waƙoƙin siysa da dama masu
jigon zambo ko habaici,waɗanda
ake yi domin a aibata abokan adawar siyasa. Auwal Isah Bunguɗu a waƙar Ɓarawon
Akwatu, ya yi irin wannan zambon.Haka ma Muhammad S. Ɗunɗaye a waƙar ‘Yan Santsi Kun Zama Kaya, da Yakubu
Labaran a waƙar
‘Yan Santsi Sun Ji Kunya, da sauransu da dama. Don haka yanzu wannan nazari zai
ɗauki waƙoƙi biyu
daga kowanne ɓangare
da nufin yin nazarinsu ta fuskar jigo da Salo da sarrafa harshe.
Nazarin waƙar Ya Allah Ka ba mu
Aminci ta Musa Madugu
An haifi Malam Musa Madugu a
garin Keffi a lokacin tana cikin jihar Platoe, yanzu kuma tana jihar Nasarawa,
a shekarar 1948. Ya halarci makarantar Allo tun yana ƙarami, a garin na Keffi.
Bayan ya sauke Alƙur’ani mai tsarki ne ya karanci litattafai manya da ƙanana
waɗanda suka shafi
addini. Bai halarci makarantar Boko ba, sai da yako yi yadda ake yin rubutun
boko na Hausa, da karantawa har ma da Ingilishi daga abokai da ‘yan uwa. Tun
yana ƙarami
ya fara koyon sana’ar tela, wacce sana’ar mahaifinsa ce, har ya ƙware
sosai, sai kuma noma da kiwo a matsayin sana’a kamar kowane Bahaushe.
Mutum ne mai sha’awar waƙe-waƙe tun
yana ƙarami
sosai, har ya iya karanta wasu waƙoƙi guda biyu, ɗaya ta Hausa ɗaya
kuwa ta Larabci. Ta Larabcin itace ‘Al-wasa’il Al-mutaƙabbala wadda aka fi sani
da Ishiriniya ta Alfazazi, sai kuma ya iya karanta waƙar Infiraji ta marigayi
malam Aliyu na Mangi. Bai taɓa
rubuta waƙa
ba, har sai shekarar 1978, inda ya rubuta waƙar ‘Rabbana Nuna Mana Gaskiya Mu Bi NPN
Baki Ɗaya,
sai kuma ya rubuta waƙar ‘Ya Allah KaBa Mu Aminci Ya Riƙa Mana Ba Da Ya Gaza Ba,
ya rubuta wata mai suna ‘Haɗa
Kai a Wajenmu a Zauna ba Bambanci Tsakaninmu, da sauran waƙoƙi da
dama.
Sharhin waƙar Ya Allah kaba mu
Aminci.
Amshi: Ya Allah ka ba mu aminci
NPN ba za ta gaza ba.
To Bismillah ni zan fara,
Sunan Rabbana naf fara,
Nai nufin waƙa in
tsara,
Ya Allah kaba ni basira,
In waƙar ba ban fasa ba.
Tun a amshin wannan waƙa
Malam Musa ya nuna cewa waƙar siyasa zai yi, kuma ta jam’iyyar NPN. Don haka sai ya yi roƙo ga
Sarki Allah kan yaba su aminci, ya zamo jam’iyyarsu ta NPN ba ta gaza ba wajen
lashe zaɓuka da kafa
gwamnati.
A baiti na farko mawaƙin ya
fara buɗe waƙarsa
da sunan Allah, domin Allah ya lamunce masa, yadda zai fara waƙar NPN.
Wannan wani salo ne daga cikin mawaƙan ƙarni na19 waɗanda tasirin addini ya shige su sosai.A baiti
na biyu ya ci gaba da cewa:
Idan aka ce da ku wane ne,
Mai waƙar ga ? Ni Musah ne,
Nai nufin waƙar haɗa
kai ne,
Yau waƙar na NPN ne,
Za mu yi ba da mun fasa ba.
A baiti na biyu mawaƙin ya
sa hannu ya kuma buga hatiminsa, ya sanar da mai sauraro sunansa ta fuskar jawo
hankalinsa ya san cewa, ga wanda ya yi waƙar. sai kuma ya fara fito da manufar waƙar,
wato ya bayyana jigon waƙar da cewa haɗinkai
ne ga ‘yan jam’iyyar NPN.
Da farko nai kira ga samari,
‘Yanmata mu tashi da sauri,
Mui yaƙi mu kakkaɓe ƙwari,
Don ‘yanci ya tabbata sauri,
Ba su wane mai ha’inci ba.
A baitoci na 3 da 4 da 5 Malam
Musah Madugu ya ƙara fito da jigon wannan waƙar ne, domin ya nuna cewa matasa maza da
mata su tashi tsaye wajen ganin sun haɗa
kai.
Na yi kira wajen haɗa kanmu,
Samari har da ‘yanmatanmu,
Mui haƙuri mu riƙe
junanmu,
Mui ladabi wajen manyanmu,
In mun haka to ba ma taɓe
ba.
Kar mu riƙe juna a zukata,
Samari har zuwa ‘yanmata,
Yau mu riƙe a shirya zumunta,
Kar mu wa junanmu mugunta,
Mu dage ba da ha’inci ba.
Duk jam’iyyu huɗu ba ma son su,
Don mun gane irin manufarsu,
Su burinsu dai gina kan su,
Kana har zuwa ‘ya’yansu,
Mun gane ba ma faɗa
ba.
Kalli ji NPP mun manta ta,
UPN kuma tamfar ba ta,
NPP mun gane ta,
PRP kuma mun ɗaure ta,
Ba za ta ɗaga
ta je yawo ba.
To yanzu sai mu kame kanmu,
Don mu tsare mutuncin kanmu,
Mui haƙuri mu riƙe
junanmu,
Ba gaba a tsakaninmu,
Mu ɗaure ba da
mun watse ba.
Idan an duba baitocin da suka
gabata za a ga cewa marubucin wannan waƙayana ƙoƙarin warware zaren waƙarsa
ne, ta hanyar koɗa
jam’iyyarsa da tallatata da kuma dakushe hasken jam’iyyun adawa. Ya ci gaba da
yi wa ‘yan jam’iyyarsa nasiha a kan kowa ya tsaya a matsayinsa kar manya ko ƙananan
‘yan jam’iyya wani ya je yana aikata wasu abubuwan da ba su dace ba.Haka wannan
mawaƙi
ya yi amfani da abubuwan da suka shafi warwarar jigo a cikin wannan waƙar,
har zuwa ƙarshe.
4.1 Sharhin Waƙar
Nagari na Kowa ta Alhaji Garba Gashuwa wadda ya yi wa tsohon Gwamnan jihar
Kano, Malam Ibrahim Shekarau
An haifi Alhaji Garba Gashuwa a
shekarar 1957 a cikin garin Bade da ke ciki tsohuwar jihar Borno, wanda yanzu
garin Bade ya ke a jihar Yobe.Ya yi karatun Alƙur’ani mai tsarki, sai ya shiga harkokin
kasuwanci. Ya fara waƙa a shekarar 1978 wato yana shekara 21 kacal a duniya. A
lokacin da Malam Aminu Kano na jam’iyyar PRP, ya je garin Gashuwa yaƙin
neman zaɓe ne ya ga
Garba Gashuwa, ya kuma lura yana da basira sosai. Sai ya nemi ya dawo Kano da
zama, domin ya riƙa waƙe jam’iyyarsu. Garba Gashuwa ya rubuta waƙoƙi sama
da 600, sai dai sabo da daɗewar
lamura da rashin taskace waɗannan
waƙoƙi ya
sa, waƙoƙin da
aka samu ba su fi 400 kacal ba. Malam Garba yana rubuta waɗannan waƙoƙi ne
da Hausar Ajami.
4.1.1 Jigo
Jigo na nufin muhimmin saƙon da
mawaƙi
yake son isarwa ga al’umma, wato abin da waƙar ta ƙunsa dangane da manufa. Auta(2008:203)
Jigon waƙar ‘Na gari na kowa’:
Idan an yi la’akari da babban jigon wannan waƙar za a iya cewa yabo ne na Sardaunan
Kano, Malam Ibrahim Shekarau. Za a iya ganin haka tun a sunan waƙar,
sai kuma mawaƙin ya ƙara tabbatar da haka a cikin baiti na 7, inda yake cewa:
Ibrahim Allah sa kana gida,
Gaisuwa ta ishe wa maigida,
Sardauna riƙonka yana da fa’ida,
Ku jama’a ku gujewa mahassada,
Gara ku san Allah shi ne ɗaya.
Jigo a taƙaice: Baiti na 3-4 kira
ya ke yi ga jama’ar birni da na karkara a kan su zo su tsaya kan gaskiya, su zaɓi mutum na gari wanda ya zo
da gaskiya.
A baiti na 5-7 kuwa mawaƙin
yana bayani ne a kan kyawawan halayen malam Ibrahim Shekarau.
A baiti na 8-10, mawaƙi ya ɗan yi shaguɓe ne a kan wasu abokan
adawar Malam Shekarau.
A baiti na 11-12 ya bayyana irin
samun nasarar da Malam ya yi sakamakon halayensa na kirki.
4.1.2 Warwarar Jigo
Wannan waƙa tana da babban jigo na
yabo ne. Ya ƙara
fito da hakan tun a baiti na 4, inda ya ce :
Kai ku san malam ya zo da gaskiya,
Yai horo a tafi da gaskiya,
Ya kori du mai son hayaniya,
Mai haƙuri shi zai ci moriya.
Jalla ka ba mu riƙo na gaskiya.
A baiti na gaba ya ci gaba da
zayyana kyawawan halayen Shekarau, inda yake cewa:
Tunda shi Gwamna ne mai kishin ƙasa,
Ga taimakon jama’a mutan ƙasa,
Hadda na nesa zuwa na nan kusa,
Ku daina zuwa neman bugun ƙasa,
Yarda da Allah kuma gaskiya.
A nan mawaƙin ya yi ƙoƙarin
dai-daita ma’auninsa a cikin baitocin inda ya ɗora
baitocin a kan Karin ‘Madid’ wato 7+5+7(+5) na faa’ilatun + faa’ilun.
4.1.3 Salo
Salo shi ne hanyoyi ko dabarun
isar da saƙo
ga mai karatu ko sauraro (Ɗangambo 2007:35-37). Dangane da salo a wannan waƙar ana
iya cewa mawaƙin ya yi amfani da miƙaƙƙen salo ne, sabo da ya isar da saƙonsa
kai tsaye, ba tare da ya yi wani ƙaƙale-ƙaƙale ba.Wannan ba ya rasa nasaba da jigon
waƙar.
Akwai iren-iren salo da mawaƙin ya yi amfani da su, wanda suka haɗa da:
4.1.5 Mutuntarwa
Mutuntarwa ita ce a mayar da abin
da ba mutun ba, ya zama mutum. Ɗangambo(2007:45-46) Malam Garba Gashuwa a
cikin wanna waƙar yakan ɗauki
wasu halaye ko siffofi da darajoji da mutane ke da su, ya laƙaba wa
wani maras rai ko dabba ko tsuntsu ko ƙwari. Kamar yadda za a ga misali a baiti
na 8, inda ya ce:
Ke kurciya ki guje wa hassada,
Ke hasbiya ki rage gada-gada,
Ke ba ki dawa kuma ba ku nan gida,
Ku yi fassara ku fahimci gaskiya.
(Garba Gashuwa a waƙar Na
gari na kowa).
4.1.6 Alamtarwa
Dabara ce ta bayyana wani abu ta
hanyar ba shi wata alama, wadda za ta tsaya a maimakonsa. Ɗangambo(2007:423)
A cikin wannan waƙar ta ‘Na gari na kowa wadda malam Garba Gashuwa ya yi wa
Sardaunan Kano malam Ibrahim Shekarau, ya yi irin wannan alamtarwar a baiti na
12. Ga abin da ya ce:
To a she malam ya samu garkuwa,
A gun Allah ya samu karɓuwa,
Ai ruwan tasah na ta ɗuruwa,
Mik kai mai shanu shige ruwa,
Tai ka fake kar in yi dariya.
(Garba Gashuwa a waƙar ‘Na
gari na kowa’ baiti na 12)
A ƙarshen wannan nazari an kawo abuwan da
suka shafi wannan waƙar muhimmai.
4.2 Sharhin waƙar CPC
mai Alƙalami
ta Malam IbrahimSaleh (Iyala)
An haifi Ibrahim Saleh a unguwar
Kawo a cikin ƙaramar hukumar Kaduna ta Arewa, ranar 1-1-1973.Ya yi karatu a
KTC Kaduna, da Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Jihar Kaduna (KAD-POLY) inda ya
karanci fannin aikin jarida a shekarar 2002. Tun Ibrahim yana ƙarami
ya ke da sha’awar waƙoƙi har ya girma. Shi ne ya wallafa waƙar ‘Yan Najeriya riƙo sai
mai gaskiya, Baba Buhari kai muke so Najeriya’ wacce ta yi fice sosai.Daga baya
kuma ya wallafa wannan waƙar ta CPC Mai Alƙalami.
Dalilin yin wannan waƙar: Babban dalilin yin wannan waƙar ba
ya rasa nasaba da sauya sheƙar da tsohon shugaban ƙasar Najeriya na mulkin soja Janaral
Muhammadu Buhari mai ritaya, ya yi ba daga jam’iyyar APP, zuwa CPC Mai Alƙalami.
Kai tsaye jigon wannan waƙar ya
fara ne tun daga baiti na 7 da 8 a cikin waƙar, Inda ya ce:
Na ɗau
Alƙalamin
rubutu,
Zan fara baituka da dama.
Kaifinsa ya wuce takobi,
Da Bindiga Allah ba ni himma.
Mai sha’awar ya bi tafiyarmu,
Yo maza kar mu baro ka baya.
(Ibrahim Saleh, waƙar CPC
mai Alƙalami
6-10)
Tsarin waƙar: Waƙar ta
fara da Basmala, ta kuma ƙara jaddada manufar waƙar. Sannan ‘yanƙwar biyu ce, tana ɗauke mabambantan amsa amon
da yake sauyawa daga baiti zuwa baiti. Sannan tana da yawan baituka 205. Ta
fuskar aron kalmomi, an yi amfani da kalmomin harshin larabci da ingilishi.
Misalan kalmomin larabci sun haɗa
da: Alƙawiyyu
da Allamal insan bil ƙalam da khaliƙi da Alƙur’ani da Alƙalami da Ahli Ashabu. Da
sauransu.
4.2.1 Salo da Sarrafa Harshe
Mawaƙi ya yi amfani da sassauƙan
Salo wajen isar da saƙonsa. Sai dai akwai adon harshe kamar su ba’a da zambo da
kirari da habaici da baƙar Magana. Haka kuma akwai alamtarwa da dabbantarwa da
kamantawa da sauransu. Misalin inda ya yi zambo a waƙar ya haɗa da baiti na 32 da 33 da
34 da da 41 da 46 da 47 da 52 da 56 da 57 da 66 da 88 da 92 da 158 da 175 da
kuma 176. Misali a baiti na 32 ya ce :
32. Ashe malami tsiya ne,
Kun ji Babur mai kaya da kowa.
33. Sai na ce kun gad an baƙin
nan,
In ya yahe za mu dinga fama.
57. Akwai wani ma mai kama da
Malam,
Gulma kwai shi yai yo iyawa.
5.0 Naɗewa
A wannan takarda an bayar da
ma’anar siyasa da ma’anar jam’iyya da yadda mawaƙan siyasa suka sha gwagwarmayar neman
‘yanci da yadda suka riƙa faɗi-tashin
tallata ‘yan takara daga matakai mabambanta da yadda suke tallata jam’iyya.
Wannan aikin ya duba yadda irin waɗannan
mawaƙa
suka riƙa
aiwatar da waƙoƙinsu na siyasa masu jigogi mabambanta, tun daga jamhuriya ta
farko da jamhuriya ta biyu da ta uku da kuma wacce ake ciki a yanzu wato
jamhuriya ta huɗu. Haƙiƙa
wannan aiki ne da zai bayar da haske musamman ga manazarta Adabin Hausa da kuma
ma su sha’awar waƙoƙin siyasa. Don haka an samar da sharhin wasu daga cikin waɗannan waƙoƙi na
siysa, an kuma kawo salonsu da jigoginsu da yadda aka yi afani da dabaru
iri-iri wajen isar da wannan saƙo.
Manazarta
Auta, A.L. (2008). Rubutattun Waƙoƙin
Hausa na Faɗakarwa a Ƙarni
na Ashirin. Kundin Digiri na Uku. Kano: Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya.
Jami’ar Bayero.
Birniwa, H.A. (2010). “Matsayin
Rubutattun Waƙoƙin Siyasa Wajen Yaƙin neman zaɓe:
Misali daga Jamhuriya ta Ɗaya da ta Biyu”. Takardar da aka Gabatar a Taron Ƙara wa Juna Sani, Katsina: Sashen
Harsunan Nijeriya, Jami’ar Umaru Musa ‘Yar’adua.
CNHN. (2006). Ƙamusun
Hausa na Jami’ar Bayero. Ahamadu Bello University Press Limited.
Ɗangulbi, A.R. (2003). “Siyasa a Nijeriya:
Gudunmuwar Marubuta Waƙoƙin Siyasa naHausa ga Kafa Dimokraɗiyya.” Kundin Digiri na Biyu. Sakkwato: Sashen
Harsunan Nijeriya. Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo.
Ɗan’illela, A. (2010). Rubutattun Waƙoƙin
Siyasa: Nazari a kan Jihohin Sakkwato da Kebbi da kuma Zamfara.” Kundin Digiri
na Biyu. Sakkwato: Sashen Harsunan Nijeriya. Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo.
Ɗangambo, A. (2007) Ɗaurayar
gadon feɗe waƙa.
Zaria: Amana Publishers Ltd.
Ɗangambo, A. (1986). “Rabe-raben Adabin
Hausa da Muhimmancinsa ga Rayuwar Hausawa. Kano Triumph.
Ɗiso, A.H (1997). Zambo da Yabo a Matsayin
Dabarun Jawo Hankali a Rubutattun Waƙoƙin Siyasa na Hausa. Kundin Digiri na
Biyu. Kano: Sashen HarsunanNijeriya. Jami’ar Bayero.
Furniss, G. (1996). Poetry, Prose
And Popular Culture in Hausa. London EPU Press.
Gusau, S. M (1984).(2) Nazarin zaɓaɓɓun waƙoƙin baka na Hausa. Cyclostyled Edition.
Kano: Sashen koyar da Harsunan Najeriya, Jami’ar Bayero.
Jumare, B. (2008). Tarken Waƙoƙi Uku
na Mudi Spikin. Kundin Digiri na Farko. Zaria: Sashen Harsunan Nijeriya da
Al’adun Afrika, Jami’ar Ahmadu Bello.
Mashi, M.B. (1986). Waƙoƙin
Baka na Siyasa: Dalilansu da Tasirinsu ga Rayuwar Hausawa. Kundin Digiri na Biyu. Kano: Sashen Harsunan
Nijeriya. Jami’ar Bayero.
Mukhtar, I. (2006). Gudunmawar
Rubutattun Waƙoƙin Siyasa Wajen Adana Tarihin Siyasar Nijeriya. Algaita:
Journal Of Current Research In Hausa Studies, (14).
Sa’id, B. (2002). Rubutattun Waƙoƙin
Hausa na Ƙarni
na Ashirin a Sakkwato, Kabi da Zamfara.
Kundin Digiri na Uku. Sashen Nazarin Harsunan Najeriya. Kano: BayeroUniversity,
Nigeria.
Yahaya, A.B. (1997). Jigon
Nazarin Waƙa.
Kaduna: Fisbas Media Serɓices.
Yahaya, A.B. (2001). Salo Asirin
Waƙa.
Kaduna: Fisbas Media Serɓices.
Yahaya, I.Y. & Ɗangambo,
A. (1986). Jagoran Nazarin Hausa. Zaria: NNPC.
Yakawada, M.T. (1987). Tarkakken
Matanin Waƙar
‘Kanzil Azim’ ta Aliyu Namangi. M.A Arts. Department of Nigeria and African
Languages. Zaria: AhmaduBello University, Nigeria.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.