Citation: Karofi, I.A., Rabeh, H. and Darma, A.Y. (2024). Tarken Faɗakarwa a Waƙar ‘Annobar Korona’ ta Khalid Imam..Ginshiƙin Nazarin Salon Waƙoƙin Hausa, 487-495. www.doi.org/10.36349/djhs.2024.ɓ03i01.060.
TARKEN FAƊAKARWA
A WAƘAR
‘ANNOBAR KORONA’ TA KHALID IMAM
Isah Abubakar
Karofi
Hassan Rabeh
Abdullahi Yakubu
Darma
Sashen Hausa,
Kwalejin Ilimi ta Isa Kaita, Dutsinma, Katsina
Tsakure
Manufar takardar ita ce yin
nazari a kan waƙar Annobar Korona da hanyar yi wa waƙar filla-filla ta amfani
da hanyoyin nazarin rubutattun waƙoƙin Hausa domin a bayyana muhimman ɓangarori da nazari ya
dogara da su, kuma masana suka amince a yi nazarin kowace rubutacciyar waƙa da
waɗannan hanyoyin. Da
yake nazari ne a kan rubutacciyar waƙa, an karanta waƙar (Annobar Korona) sosai
ta yadda aka iya fayyace waɗannan
muhimman ɓangarorin
nazari, sannan aka kafa hujjoji daga baitocin waƙar. A sakamakon binciken takardar an gano
cewa waƙar
tana ɗauke da turke ko
jigon faɗakarwa a kan
cutar Korona, kuma ta cancanci a yi nazarin ta domin ta hau matakin nazari da
masana da manazarta na adabin Hausa suka amince kowace rubutacciyar waƙa ta
hau kamar salsalar waƙar da tarihin marubuci da shekarar wallafa da jigon waƙar da
warwarar jigo da salo da sarrafa harshe da dabarun jawo hankali da dai sauran
hanyoyi yin tarke ko nazari. Don haka, an bayyana dukkannin hanyoyin tarke ko
nazari a cikin waƙar, sannan aka kafa hujjoji daga baitocin waƙar.
Fitilun Kalmomi: Tarke, Faɗakarwa,Waƙar ‘Annobar Korona, Khalid Imam
Gabatarwa
Annobar Korona, wato Kobid19 kamar yadda ake kiran
ta,ta faro daga gabashin duniya a ƙasar Sin, sannu ta yaɗu tamkar wutar daji zuwa sassan duniya gabas
da yamma, kudu da arewa. Cutar ba ta bar manyan garuruwa ba bare ƙananan
da suke koma-baya wajen harkar kula da lafiya. Wannan annoba ta nuna yatsunta
ga manyan ƙasashe
da hukumomin lafiya masu ji da kansu ganin yadda suka kasa kataɓus wajen daƙile ta
tun farkon ɓullowarta.
Wannan dalilin ya sa marubuta da ma’abota ayyukan adabi bibiyar wannan muguwar
annoba da nufin bayar da gagarumar gudummuwa akan irin tasirinta da illolinta
ga al’umma. Kai! Har ma da nuni ko tattaunawa akan sanin haƙiƙanin
wannan annoba a idon mutanen da suke sun yi nisa a ilimin zamani da ma waɗanda ba su yi zurfi ba.
2.0 Manufar
Bincike
An gudanar da
wannan bincike bisa manufar bayyana hanyoyin nazari da masana suka samar domin
yin tarken faɗakarwa a
rubutattun waƙoƙi a Hausa.
Haka kuma, ana
son a bayyana salsalar waƙa da tarihin marubuci da shekarar wallafa da babban jigon da jigo a gajarce da
warwararsa a waƙar da Khalid Imam
ya yi ta Annobar Korona.
Bayan nan, ana
son a kuma bayyana yadda Malam Khalid ya yi amfani da zubi da tsarin baitoci da
kari da amsa-amo da salo da sarrafa harshe da dubarun jan hankali da kuma
Hausar nahiya a wajen gina waƙarsa ta faɗakarwa
a kan annobar Korona.
3.0
Hanyoyin Gudanar da Bincike
An yi amfani
da hanyoyi biyu wajen gudanar da wannan bincike. Hanyar farko ita ce karantawa
daga wasu rubutattun bayanai, waɗanda
suka haɗa da bugaggun
littattafai da kundayen bincike da mujallu da sauransu.
Hanya ta biyu
kuwa, ita ce ta yin hira da masana adabi, musamman na rubutacciyar waƙar
Hausa. A nan, an yi hira da ɗaya
daga cikin editocin littafin wato Khalid Imam, wanda aka samu wasu bayanai da
aka sanya a cikin wannan bincike. Haka kuma, an yi hira da wasu masana
rubutaccen adabin Hausa. A wajensu aka samu wasu bayanai nahanyoyin nazarin waƙoƙin
baka na Hausa kamar yadda Ɗangambo, 1975, 1981 da 2007 ya shimfiɗa a Mazhabar tarken rubutacciyar waƙar
Hausa.
4.0 Hanyar Ɗora
Aiki
An ɗora
wannan takarda bisa ‘Mazhabar Rubutacciyar Waƙar Baka’. Wannan ra’i ne wanda ya fi mayar da
hankali ne ga tattaro ra’ayoyin manazarta kan hanyar nazarin rubutacciyar waƙar Hausa. Masanin da ya
assasa wanna ra’i shi ne Farfesa Abdulƙadir Ɗangambo a shekara ta 1975 har ya rubuta
littafi mai suna Gadon Feɗe Waƙa. A kuma 1981 ya fito da Ɗaurayar Gadon Feɗe Waƙa da kuma Ɗaurayar Gadon Feɗe Waƙa (sabon salo) a shekara ta 2007. Masanin ya assasa wannan
ra’in domin samar da wata hanyar nazarin rubutacciyar waƙa na bai-ɗaya karɓaɓɓe ga kowane mai nazarin rubutacciyar waƙa ta Hausa. Daga cikin
magoya wannan ra’i akwai; Abdullahi Bayero Yahya da Isa Mukhtar da Aminu Lawal
Auta da Halima Abdulƙadir Ɗangambo da Ɗahiru Abdulƙadir da Mustapha Shu’aibu da sauransu (Gusau, 2015:21-22).
Da yake takardar tana magana ne a kan tarken
faɗakarwa a waƙar ‘Annobar Korona’ an yi
amfani da hanyoyin da Mazhabar Rubutacciyar Waƙar Baka ta shimfiɗa wajen yin tarken kowace rubutacciyar waƙa ta Hausa. Kamar yadda
hanyoyin suka zo a cikin littafin Ɗaurayar Gadon Feɗe Waƙa (sabon tsari).
5.0 Tarken Faɗakarwa a Waƙar Annobar Korona
Tarke ya ƙunshi
wasu keɓaɓɓun hanyoyin nazari da
masana suka amince a ɗora
kowane aiki a kansa kafin ya cancanci ya zama karɓaɓɓen nazari ga masana. Don
haka, a nan an yi tarken waƙar ‘Annobar Korona’ ta Khalid Imam kamar yadda Mazhabar
Rubutacciyar Waƙar Baka ta Hausa ta shimfiɗa
domin tarken faɗakarwa
a rubutattun waƙoƙin baka na Hausa.
5.1 Salsalar Waƙar
An sami wannan
waƙar
ne a cikin littafin Corona Blues (A
Bilingual Anthology of Poetry) shafi na 108-114. Kamfanin ɗab’i na Whetstone
Publishers, Kano ne ya buga wannan littafin a shekarar 2020. Waƙar ta
Annobar Korona ita ce ta 2 a jerin waƙoƙin da aka yi da harshen Hausa da suke
cikin littafin.
5.2 Tarihin Marubucin a Taƙaice
An haifi
Khalid Imam a cikin birnin Kano a shekarar 1973. Khalid Imam marubuci ne cikin
harsunan Hausa da Turanci kuma malamin makaranta ne a garin Kano. Khalid Imam
ya yi karatun digiri na ɗaya
da na biyu a Jami’ar Bayero, Kano. Shi manazarci ne wanda yake da matuƙar
sha’awa ta gudanar da bincike na ilimi a fannonin adabi da al’ada da tarihi da
kumarubutu a kan kare haƙƙi, musamman na yara da mata.Zuwa yanzu, Khalid Imam ya
wallafa littattafai sama da goma sha biyu (12) cikin harsunan Hausa da Turanci.
An wallafa rubuce-rubucensa na adabi da muƙalun ilimi da dama a cikin gida Nijeriya
da ƙasashen
waje kamar su Amurka da Indiya da Jamus da Poland da Lebanon da sauransu.
Khalid Imam shi ne Shugaban kamfanin fassara da talifi mai suna Whetstone Arts
and Translation Serɓices.
Haka kuma, Babban Darakta ne a makarantar Khalid Imam Academy da take a Kano.
Ya taɓa zama Mataimakin
Shugaban Ƙungiyar
Marubuta ta Nijeriya reshen jihar Kano. Khalid Imam ne ya kafa wani muhimmin
dandali na marubuta a kafar sadarwa ta zamani ta WhatsApp mai suna All Poets
Network. Haka nan kuma, Khalid Imam shi ne yake rubutu a shafin faɗakar da matasa akan
muhimmancin rayuwa da sana’a a mujallar Muryar Arewa mai suna Sirrin Arziki da
Nasara. Khalid Imam yana da mata biyu da yara da yawa. Allah ya yi wa rayuwarsa
albarka amin[1].
5.3 Shekarar Wallafa
An wallafa waƙar
‘Annobar Korona’ a cikin littafin
Corona Blues (A Bilingual Anthology of Poetry) a shekarar 2020, kamfanin ɗab’i na Whetstone Kano ya
wallafa littafin.
5.4 Jigon Waƙar
Muhammad
(2003:143) ya bayyana jigo da “Shi ne gangariyar muhimmin saƙo ko
manufar mawaƙi”.
Jigon wannan
waƙar
dai shi ne faɗakarwa a
kan annobar Korona. A baiti na 18,
marubucin ya
bayyanar da manufar waƙarsa a kan Korona, wato a wannan baitin ne ya bayyana ƙwayar
jigonsa na cutar Korona kamar yadda sunan waƙar ya nuna:
Ita annobar Korona,
Cuta ce babu shakka.
(baiti na 18)
Wannan saƙo ko
jigon ne ya yi ta ƙoƙarin nanatawa da jawo hankali a kan cutar Korona a baitoci
daban-daban na waƙarsa. Misali, a baiti na 30 zuwa baiti na 34 kamar yadda za a
gani a ƙasa:
Ni Khalid bani shakka,
Tabbas cutar Korona.
Jan kunne ce gare mu.
Mu bar saɓo da sharri.
(baiti na 30)
Mu so junanmu gaske,
Hakan zai taimake mu.
(baiti na 31)
Ni Imam Khalid na Indo,
Jikan Hauwa’u tabbas.
(baiti na 32)
Nasan cutar Korona,
Ƙanwa ce gun talauci.
(baiti na 33)
Wajen ƙeta da sharri,
Har ma yawo a dangi.
(baiti na 34)
Haka dai mawallafin ya yi ta kawo baitoci masu
nuna illa ko munin Korona da masifun da take haifarwa cikin al’umma domin a faɗakar da jama’a.
5.5 Jigo a Gajarce
Jigo a gajarce
shi ne masana suke dangantawa da gundarin jigo wato, saƙo a taƙaice
da marubuci yake son isarwa ga jama’a (Muhammad, 2003:143).
Idan aka yi
nazarin waƙar
za a iya fitar da jigonta a gajarce kamar haka:
Tabbas cutar Korona,
Annoba ce ta gaske.
(baiti na 10)
Ita annobar Korona,
Cuta ce babu shakka.
(baiti na 18)
5.6 Warwarar Jigo
Warwarar jigo
shi ne cikakken bayanin hanyoyin da mawaƙi ya bi ya cim ma jigonsa. Ma’ana ya fito
da saƙon
ƙuru-ƙuru, a
fili ta hanyar yin sharhi (Muhammad, 2003:144).
Wannan waƙar
tana ɗaya daga cikin
waƙoƙin da
suke faɗakarwa a kan
annobar Korona domin jama’a su hankalta tareda ɗaukar
matakai da za su kare kansu daga gare ta. Ga misali, daga waƙar:
Ita annobar Korona,
Cuta ce babu shakka.
(baiti na 18)
Wannan baitin ya fito da tabbacin Korona cuta ce
babu shakka a kanta. Don haka, mutane su ɗauki matakin kare kansu daga sharrinta.
Ba ta kunya ba ta tsoro,
Ba ta sabo ba sanayya.
(baiti na 19)
Baitin na gaba yana daɗa fito da munin Korona ga jama’a domin
tana iya kama kowa watao ba ta nuna sani ko ragowa ga kowa da kowa.
Yau mutum ya gane cewa,
Bai da ƙarfi sai na Allah.
(baiti na 20)
Bai da sauran duk dabara,
Kariyarsa tana ga Rabbu.
(baiti na 21)
Waɗannan
baitoci biyu suna ƙoƙarin jan hankali ga mutane su gane cewa babu wanda
ya gagari wannan cuta ta Korona komai dubararsa domin ta kama mutane daga ƙasashen
da suka yi zarra a duniya ta fuskar kimiyyar magunguna. Don haka kariya daga
gare ta sai dai Allah.
5.8 Zubi da Tsarin Waƙar
Zubi da tsari
ya danganci yadda mawaƙi ya shimfiɗa
waƙarsa
dangane da salon buɗewa
da rufewa da gina baitoci ko tsarin layuka da amsa amo da karin waƙar da
sauransu (Muhammad, 2003:144).
Wannan waƙar ta
Annobar Korona matsakaiciya ce domin tana da baitoci 36 ne kawai. Mafi
yawancinta ƙwar
biyu mai gajerun jimloli. A taƙaice dai waƙar ‘yar tagwai ce, amma an samu ƙwar huɗu a baiti na 15 da kuma 30
a cikin waƙar.
Mawallafin ya
jeranta tunaninsa, bai yi wa waƙar zubin kwan-gaba-kwan-baya ba yadda za
ta yi wahalar ganewa. Wannan dalili ya sa ana iya fahimtar jigonta da wuri wato
faɗakarwa a kan
annonbar Korona.
Mawallafin ya
jaddada manufarsa inda ya riƙa maimaita wasu baitoci a fakaice ba kai
tsaye ba. Misali,
Tabbas cutar Korona,
Annoba ce ta gaske.
(baiti na 10)
Ita annobar Korona,
Cuta ce babu shakka.
(baiti na 18)
A taƙaice
dai jerin carbin tunanin mawallafin bai tsinke ba.Misali:
Baiti na 1-5 ya nuna yadda ‘yan bariki
da wurare irin su kasuwanni da mashaya da makarantu da sinima da ‘yan ƙwallo
da kuma ‘yan dambe duk sun ɓace
saboda gudun kamuwa da Korona.
Baiti na 6-9 mawallafin ya nuna munin
sharrin Korona domin ta shafi gwamna da minista da manyan ƙasashen
duniya ba wanda ta bari.
Baiti na 10-18 ya bayyana munin Korona
a faɗin duniya domin a
dalilin Korona duk wasanni da sharholiya sun gagara buɗewa a manyan ƙasashen Turai.
Baiti na 19-29mawallafin ya fito da
mafita ɗaya domin kawo
ƙarshen
Korona shi ne komawa ga Allah ana masu tuba akan zunuban da ake aikatawa.
Baiti-30-36 mawallafin ya gaskata cutar
Korona da kuma jan kunne a kan cutar da jan hankalin jama’a a kan komawa ga
Allah da tuba domin kowa ya rabauta daga sharrin Korona.
5.9 Zubi da Tsarin Baitoci
Wannan waƙar dai
tana da baitoci 36 ne kuma‘yar tagwai ce, sannan tana da gajerun jimloli. Mafi
yawan jimlolinta suna da cikakkiyar ma’ana.
5.10 Amsa-amo (Kafiya)
Waƙar ba
ta da amsa amo saboda ba daidaito na haruffan waƙar a farko ko a ciki ko wajen baiti.
Kowane baiti yana ƙarewa daban.
5.11 Salon Waƙar
Waƙar
tana ɗauke da kalmomin
aro daga Turanci (kamar minister da billa da sinima da coci da champions
League) da kuma Larabci (kamar Allah da Rabbu da Ilahu da sharri). Haka nan
mawallafin ya yi amfani da miƙaƙƙen salo da ya isar da saƙonsa
kai tsaye. Da an karanta waƙar za a fahimci cewa mawaƙin yana ƙoƙarin faɗakarwa
ne da jawo hankalin mutane a kan cutar Korona da abubuwan da ta haifar a cikin
duniya.
Kalmomin da
aka yi amfani da su masu sauƙin ganewa ne hatta na Turanci da na
Larabcin, kuma mawallafin ya sarƙa saƙonsa cikin gajerun jimloli waɗanda akasari suke da
cikakkiyar ma’ana bisa kansu. A taƙaice dai waƙar ta gamsar kuma saƙonta
ya fito fili.
Wani salo da
aka lura da shi, shi ne mawaƙin bai
buɗe waƙarsa
da yabo ga Ubangiji ko manzonsa ba, amma ya rufe ta da addu’a. Haka kuma,
mawallafin ya buɗe waƙar da
bayanin irin tasirin annobar ga yanayin rayuwa inda ya nuna ta sauya irin
ayyukan sharholiyar da jama’a suke yi duk sun daina.
5.12 Dabarun Jawo Hankali
Dangane da
kalmomin fannu waƙar ta zo da kalmomin da suka dace da jigonta na faɗakarwa da tsoratarwa. An yi
amfani da kalmomi kamar su Ilahu da Rabbu da tuba da rabauta da wa’azi da
zunubi da shakka da Allahuda sharri da saɓo
da sauransu. Waɗannan
kalmomi duk sun dace da jigon waƙar. An lura da cewa waƙar ta
zo da jaddadar ƙarfafawa domin tabbatar da munin cutar Korona ga jama’a.
5.13 Sarrafa Harshe
Sarrafa harshe
ya shafi yadda mawaƙi ya yi amfani da harshe mai sauƙin fahimta ko mai tsauri. Da kuma, yadda
mawaƙi
ya yi amfani da kalmomin aro na Larabci da Turanci da sauransu. Haka nan kuma,
mai nazarin rubutacciyar waƙa zai yi la’akari da luggogin harshe da mawaƙi ya
yi amfani da su domin ƙawata waƙarsa ((Muhammad, 2003:145).
Mawallafin ya
yi zaɓen kalmomin da
suka dace da jigon waƙarsa. Akwai baƙin kalmomin da aka yi amfani da su na
Turanci irin su; sinima da gwamna da minista da coci da Champions League da
sauransu. Haka kuma, ya sanya wasu baƙin kalmomi daga harshen Larabci irin
su; Ilahu da Rabbu da tuba da rabauta da wa’azi da zunubi da shakka da Allahu
da sharri da sauransu. Sannan kuma, mawallafin ya yi amfani da Hausar Kananci a
waƙarsa.
Akwai karin harshen Kananci kamar;
mui da kilaki da kufai da sauransu.
Haka nan kuma,
marubucin ya amfani da alamtarwa a
cikin waƙarsa
ta yadda za ta ƙara armashi ga baitocin waƙar kamar haka:
Ta bi gwamna har gidansa,
Ta shaƙi wuyan minister.
(Baiti na 6)
Abuja har Billa,
Ta shige ta yi sheƙa.
(Baiti na 8)
Masu sheƙe aya su more,
A Italiya ko Amurka.
(Baiti na 14)
Ni Khalid ba ni shakka,
Tabbas cutar Korona,
Jan kunne ce gare mu.
(Baiti na 30)
Bayan nan
kuma, ya yi amfani da mutuntarwa dadabbantarwa domin ya ƙara
fito da yadda Korona ta samu wurin zama a ƙasashe. Misali.
Tai ƙwayaye
ta ‘ya’ya,
Ta miƙe ƙafa a fada.
(Baiti na 9)
Ba ta kunya ba ta tsoro,
Ba ta sabo ba sanayya.
(Baiti na 19)
Sannan kuma,
ya yi amfani da siffantarwa domin
nuna munin Korona a Turai kamar haka:
Kufai a kira yi Turai,
Champion League tsaya cik.
(Baiti na 16)
Haka zalika,
marubucin ya sarƙa karin magana a
cikin waƙarsa
domin ta haskaka, ta faɗakar
ta kuma ilimantar da jama’a kamar yadda za a gani a baitocin da ke a ƙasa.
Kurciya in ta yi kuka,
Saƙo
nata ban da wawa.
(Baitoci na
25).
Marubucin waƙar ba
tsaya nan ba, ya yi amfani da kirari da
wasa kai ga kansadomin nuna mallaka ga abin ƙaunarsa da kuma nuna nasabarsa kamar
yadda yake a baiti na 32.
Ni Imam Khalid na Indo,
Jikan Hauwa’u
tabbas.
Daga ƙarshe,
ya rufe waƙarsa
da addu’ar neman ƙarin fahimta da tuba ga Ubangiji a kan laifuka. Kamar haka:
Allahu kasa mu gane,
Mu tuba zuwa gare Ka.
(Baiti na 36).
5.14 Karin Waƙar
An gina wannan
waƙa
a kan karin Ramal inda aka samu ƙafa ta 7 ta maimaita kanta wato aka samu:
Faa-i-laa-tun
+ Faa-i-laa-tun (- Ɓ - - + - Ɓ - -).
Misali a baiti
na uku:
Tituna leƙa ka duba, (- ɓ
- - + - ɓ - -).
Kasuwanni har
mashaya. (- ɓ - - + - ɓ - -).
7 + 7
7 + 7
Ramal.
6.0 Shawarwari
A duk lokacin
da mai rubutu ya gama rubutunsa bai rasa bayar da shawara domin inganta ɓangaren da ya zaɓa ya gudanar da bincikensa,
don haka muna masu bayar da shawara ga manazarta da masana da su duƙufa
wajen yin bicike-bincike a kan ayyukan da mawallafa rubutattun waƙoƙin
Hausa suka yi a kan cutar Korona biros domin an yi waƙoƙi masu ma’ana masu ɗauke da jigogi mabambanta a
kan cutar waɗanda da
suke da buƙatar
a gudanar da bincike a kansu.
Wannan kuma
shawara ce ga mawallafa da ƙara zage damtse wajen ƙirƙiro sababbin waƙoƙin faɗakarwa a kan cutar Korona
saboda waƙoƙinsu
suna da saurin isar da saƙo ga jama’a ga shi kuma manazarta suna ƙara samun damar gudanar
da bincike-bicike a kansu.
7.0 Kammalawa
Wannan
takarda ta ƙunshi
muhimman bayanai a kan hanyoyinda masana suka samar domin yin tarken kowace
rubutacciyar waƙar
Hausa, sannan aka yi amfani da waɗannan hanyoyin domin yin tarken faɗakarwa a waƙar Annobar Korona ta Khalid Imam. Takardar ta ƙunshi salsalar waƙar da tarihin mawallafi
da shekarar waƙar
da jigo da gajarce jigo da warwarar jigo da zubi da tsarin waƙar da zubi tsarin
baitoci da karin waƙar da salo da dabarun jawo hankali da sarrafa harshen
waƙar.
A sakamakon
bincike an gano cewa waƙar ta cancanci a yi
nazarinta domin tana ɗauke da muhimmin jigo na faɗakarwa
wanda aka gina waƙar a kansa. Kuma waƙar ta mallaki muhimman ɓangarori
da tarke yake buƙata a yayin nazari.
Manazarta
Auta, A.L.
(2017). Faɗakarwa A
Rubutattun Waƙoƙin
Hausa. Bayero Uniɓersity,
Press.
Bala, I. da
Imam. K. (2020). Corona blues (A
Bilingual Anthology of Poetry). Whetstone Publishers.
C.N.H.N (2006). Ƙamusun Hausa. Ahmadu
Bello Uniɓersity, Printing Press.
Ɗangambo, A. (1975). Gadon Feɗe Waƙa. Takardar da ya Gabatar a
Taron Ƙara wa Juna Sani. Sashen Koyar da Harsunan
Nijeriya, Jami’ar Bayero.
Ɗangambo, A. (1981). Ɗaurayar Gadon Feɗe Waƙa. Amana Printers.
Ɗangambo, A. (2007). Ɗaurayar Gadon Feɗe Waƙa(Sabon tsari). Amana
Publishers.
Ɗamgambo, Halima, A. (2012). Kwatanta Tubalan Gina Jigo Tsakanin Rubutattun Waƙoƙi da Ƙagaggun Labarai na Hausa. [Kundin digiri na uku da ba a buga ba]. Sashen Koyar da Harsunan
Nijeriya, Jami’ar Bayero.
Gusau, S.M. (2003). Jagoran Nazarin Waƙoƙin Baka. Benchmark Publishers Limited.
Gusau, S.M. (2008). Dabarun Nazarin Adabin Hausa. Fisbas Media Serɓices.
Muhammad, Y.M. (2003). Adabin Hausa.
Ahmadu Bello Uniɓersity Press Ltd.
Yahya, A.B. (2014). Gudale Waƙar Soyayya: Misalin Gazl (Ghazal) Cikin Rubutattun Waƙoƙin Hausa. Garkuwan
Adabin Hausa a Festschrift in Tribute to Abdulƙadir Ɗangambo. Bayero Uniɓersity Kano. 125-138.
Yahya, A.B. (2015). Rerawa Ruhin Waƙa da Matsayinta a Waƙoƙin Hausa na Baka da Rubutattu. Algaita
Journal of Current Research in Hausa Studies. Bayero Uniɓersity. Special Edition, 10-15.
Ratayen
Waƙar
Annobar Korona
1. Masu gaɗa suna ta shewa,
'Yan caca da masu karta.
2. 'Yan daudu da ma
kilaki,
Sun tsere babu kowa.
3.Tituna leƙa ka
duba,
Kasuwanni har mashaya.
4. Makarantu har
sinima,
'Yan ƙwallo da masu dambe.
5. Sun ɓace duk don Korona,
Ko'ina duka tsit kake ji.
6. Ta bi Gwamna har
gidansa,
Ta shaƙi wuyan Minista.
7. Can a Landan ga Yarima,
Ta bi shi cikin turaka.
8. A Abuja har a
Billa,
Ta shige ciki ta yi sheƙa.
9. Tai ƙwayaye
ta yi 'ya'ya,
Ta miƙe ƙafa a fada.
10. Tabbas cutar
Korona,
Annoba ce ta gaske.
11. A masallatai da
coci,
Duk an koma ga Allah.
12. Sarki mai shirya
komai,
Dole ne bauta gare shi.
13. Ba tsumi kuma ba
dabara,
Duniya yau an bi Allah.
14. Masu sheƙe aya
su more,
A Italiya ko Amurka.
15. Har ƙasar
Sin can a Chana,
Ta kai da yawa kushewa.
Ko Farisa har Faransa,
Ba kowa yau a titi.
16. Kufai a kira yi
Turai,
Champions
League an tsaya cik.
17. Ba a yin zancen Ronaldo,
Har Messi ba batunsa.
18. Ita annobar
Korona,
Cuta ce babu shakka.
19. Ba ta kunya ba ta
tsoro,
Ba ta sabo ba sanayya.
20. Yau mutum ya gane
cewa,
Bai da ƙarfi, sai na Allah.
21. Bai da sauran duk
dabara,
Kariyarsa tana ga Rabbu.
22. Gatan kowa Ilahu,
Mui ta bauta mai da ɗa'a.
23. Ma rabauata a yau
da gobe,
Don ko dai cutar Korona.
24. Wa'azi ce babu
shakka,
Me je shi ke asara.
25. Kurciya in ta yi
kuka,
Saƙo nata ban da wawa,
26. Bare gaula da
soko.
Masu shashanci a hanya.
27. Hankali kura kira
shi,
Ta yin zabari na guga.
28. Mai rabo shi ke
rabauta,
In an wa'azi ya
ɗauka.
29. Zunubansa ya nemi tuba,
Kan ya ji shi
cikin kushewa.
30. Ni Khalid bani
shakka,
Tabbas cutar Korona.
Jan kunne ce gare mu.
Mu bar saɓo da sharri.
31. Mu so junanmu
gaske,
Hakan zai taimake mu.
32. Ni Imam Khalid na
Indo,
Jikan Hauwa’u tabbas.
33. Nasan cutar
Korona,
Ƙanwa ce gun talauci.
34. Wajen ƙeta da
sharri,
Har ma yawo a dangi.
35. Ni nan zan sanya
aya,
Cikin waƙar Korana.
36. Allahu kasa mu gane,
Mu tuba zuwa gare Ka.
(Bala da Imam, 2020 sh. 108-114).
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.