𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu Alaikum malam, ina nema shawara, ina da saurayi har anyi baiko tsakanin mu, to tin lokacin da aka yi muna baiko kullum kasuwanci shi naci baya, abubuwan na tabarbarewa, kuma muna garin da ada kananan maganganu, duk abinda yaci baya da wanda zaka aura sai ace daga kaine, afara magana akanka, kuma kullum cikin gayamin halin da ya ke ciki yake, da bahaka yake ba, amma yanzu abubuwa dik canza masa, sai naga kamar yana fada minne abin daga nice, wlh malan duk randa ya fadamin bana iya kwana, Allah nike ina roka mishi Allah, amma yanzu abin ya fara damuna saboda kullum kara fadamin sabbin abubuwa naci baya da yasamu, har nafara tinanin rabuwa da shi, dan Allah ya zanyi, Na gode
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa Alaikis Salaam:
Toh shakka babu indai bai ji tsoron Allah ya Dena
ba sa'annan ya tuba ya cire komai a zuciyar sa ba, toh kiyi gaggawar rabuwa da
shi domin za ki zauna da Miji Wadda yake yin Shirka zuwa ga Allah ne wannan.
Dãman su nau'ukan yin Shirka zuwa ga Allah
kala-Kala ne, Manyan Shirka zuwa ga Allah shi ne mutum ya haɗa bautar sa da Allahu Subhanahu Wa Ta'ala shi ba zai taɓa yin ibada ma Allah shi kaɗai ba sai ya haɗa shi da wani
abun daban, ko kuma mutum ya bautawa wani gumki ko Ɗan Adam ko ma bayan Allahu Subhanahu Wa Ta'ala.
Duk waɗannan Shirka ce.
Ko Kuma mutum yayi tsammanin wani cutarwa daga
wani ɗan Adam ko Jinnu ko ma bayan Allah, ko samun sa ne harkan
Kasuwancin sa ya ce ai ko rashin samun sa ya ce ai daga wani Ɗan Adam ne ko ma bayan
Ubangijin sa, toh waɗannan dukkan su
duk Musulmin da ya sanya su a cikin zuciyar sa yake kwana da su yake ta shi da
su, toh ya tabbatar cewa lallai ne yana yin Shirka zuwa ga Allahu Subhanahu Wa
Ta'ala.
Domin babu wani wadda ya isa ya cutar da wani,
babu wani wadda ya isa ya wadatar da wani ko ya amfanar da wani sai Allah kaɗai, toh daga lokacin da Ɗan Adam ya fara tunanin cewa a'a ai dalilin na
kasance da wane, shiyasa hanyoyin sa suke Kara bumkasa, ko kuma dalilin ya
kasancewa da wata ko wane shiyasa hanyoyin samun sa suka fara yin baya, toh
shakka babu ya ɗauki hanyar yin
Shirka zuwa ga Allah, da duk Waɗanda suke
tunanin cewa ai dalilin rashin samun sa ai sabida ya kai baikon sa ne zuwa ga
wacce, ga shi tun bai Aure ta ba kasuwancin sa ya fara yin baya dãman dangin su
haka suke, su ce, Ina ga Kuma ya Aure ta ai zata talautar da shi domin ita ɗin mai Bakar Kafa ce, toh duk wadda zai yi irin wannan
tunanin har ya furta shi, toh Shi ma yayi Shirka zuwa ga Allah, da shi wadda
abun yake faru da shi.
Kai a naka tunanin Allah bai isa ya jarraba samun
ka ko abun da ka mallaka ba, a'a ai wane ne ya min ko Kuma a'a dalilin na Kai
Baikon ta ne shiyasa ai Mai Bakar Kafa ce wannan Yarinyar, toh wannan Shirka
ce.
Allahu Subhanahu Wa Ta'ala yana cewa;
الَّذِينَ آمَنُوا وَلَمْ يَلْبِسُوا إِيمَانَهُمْ بِظُلْمٍ
أُولَٰئِكَ لَهُمُ الْأَمْنُ وَهُمْ مُهْتَدُونَ
"Waɗanda suka yi
ĩmãni, kuma ba su gauraya ĩmãnin su da zãlunci ba, waɗannan sunã da aminci, kuma sũ ne shiryayyu."
Allahu Subhanahu Wa Ta'ala ya ce waɗannan mutanen zai Amintar da su daga Azabar cikin qabari,
zai Amintar da su zuwa ga yi musu Hisabi me Sauki, dalilin shi ne ba su yin
irin wannan tunanin irin na saurayin ki, shin tunanin sa me yake jawowa ko yake
nunawa a kanki? Shi ne Shirka zuwa ga Allah.
Annabi Muhammad Sallallahu Alaihi Wa Sallam ya ce
duk wadda ya mutu Yana Shirka zuwa ga Allah toh ba zai shiga Aljannah ba, shin
ke kin yarda ki Auri Namiji me irin wannan tunanin tun a waje? Sa'annan Annabi
Muhammad Sallallahu Alaihi Wa Sallam ya ce duk wadda ya mutu bai taɓa yin Shirka zuwa ga Allah ba, toh Lallai Aljannah ta
tabbata gare shi (Bukhary), kenan indai Miji Nagari kike so shin wannan da yake
da irin waɗannan tunanin ya dace da
Miji Nagari ne ya dace ki Aure shi?
Allahu Subhanahu Wa Ta'ala yana cewa duk wadda ya
mutu yana yin Shirka bai tuba ya nema Gafarar Allah ba, toh makomar sa Wuta ce
sa'annan zai dawwama a cikin sa. Shirka yana da hatsari sosai kuma a yanzu mafi
Yawancin Al'umma suna aikata shi ba tare da ma sun San cewa Shirka bane, ko
kuma sun sani amma sai a take sanin a juya abun ta wani hanyar daban zuwa ga
yin Shirka ga Allah, kamar yadda a yanzu shi Saurayin ki yake gaya miki, ya
fito Fili ne ya ce miki ga shi tun da ya kawo Baikon ki kasuwancin sa komai
nashi yake yin baya a dalilin ki, yana gudun ya furta miki hakan ne domin kada
ki ce ya zage ki, amma shi ko a yanzu idan kin ce za ki rabu da shi sabida irin
abubuwan da ya ga suke faruwa da shi, toh da gudu zai yarda ku rubu, kai ko ba
ki Faɗa cewa ku rabu ba, toh a aje aje idan Bakin Jama'a suka
yi masa Yawa, shi ma tunanin sa ya Kara tafiya gaba akan haka ɗin ne, toh abun da zai ce miki kenan zai ce kawai ai ya
ga tunda ya kawo baikon ki yake Haɗuwa da masifu
daban daban da kuma kariyar kasuwancin sa, sabida haka shi ba zai iya Aure ki
ba, domin idan ya Aure ki abun zai fi haka. A karshe shi zai ce ku rabu kin ga
kenan wannan ya fada cikin Shirka ga Allah ɗin gadan-Gadan wallahi.
Akwai masu yin Shirka zuwa ga Allah a gurin yin
ibadar su don neman abun duniya, sai Allahu Subhanahu Wa Ta'ala yake cewa;
مَنْ كَانَ يُرِيدُ الْحَيَاةَ الدُّنْيَا وَزِينَتَهَا نُوَفِّ
إِلَيْهِمْ أَعْمَالَهُمْ فِيهَا وَهُمْ فِيهَا لَا يُبْخَسُونَ
Wanda ya kasance yã yi nufin rãyuwar dũniya da ƙawar ta, Munã cika musu ayyukan su zuwa gare su a cikin ta, kuma a
cikin ta bã zã a rage su ba.
Wato duk abun da mutum yake so na rayuwar domin
yana yin sa domin Jama'a don ya samu abun duniya toh zai same shi komai Allah ya
ce zai cika masa shi bai rage masa komai daga cikin sa ba, amma kuma fa bai
rabo a Ranar Alqimaya.
Har yanzu Allah ya sake cewa;
أُولَٰئِكَ الَّذِينَ لَيْسَ لَهُمْ فِي الْآخِرَةِ إِلَّا النَّارُ
ۖ وَحَبِطَ مَا صَنَعُوا فِيهَا وَبَاطِلٌ مَا كَانُوا يَعْمَلُونَ
Waɗannan ne waɗanda bã su da kõme a cikin Lãhira fãce wuta, kuma abin da
suka sanã´an ta a cikin ta (dũniya) yã ɓãci, kuma abin
da suka kasance sunã aikatãwa ɓãtacce ne.
Kin gani duk abun da mutum yake so zai samu kuma
Allah zai cika masa ayyukan sa ma'ana yana neman duniya ne, shi kuɗi yake so rayuwar sa da duniyar sa, shiyasa yake yin irin
waɗannan ayyukan, toh Allah ya ce zai ba shi Ladan sa gaba ɗayan sa tun anan duniya ba zai rage masa komai ba sai ya
gama cinye su gaba ɗayan sa, amma
kuma makomar sa Wuta ce, sa'annan duk wasu ayyukan sa kamar su Azumi ne,
Zakkah, aikin Hajji da sauran su, duk sun Lalace bai da wani aikin Lada wadda
zai sa Allah yayi masa Rahma zuwa Aljannah, Domin ya gama cinye komai nashi tun
anan duniya Wuta ce Kaɗai makomar sa.
Sa'annan akwai wani Shirkan da Jama'a suke
aikatawa ba su ma San cewa Shirka bane, shi ne Shirka na So wato Shirka ta
soyayya. Kuma Annabi Muhammad Sallallahu Alaihi Wa Sallam yana ɗayan ku bai shiga Aljannah ba, Sai ya so ni wato kin so
Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam fiye da yadda yake son kanki, fiye da
yadda yake son iyayen sa fiye da yadda yake son Yaran sa, fiye da yadda yake
son Matar sa fiye da yadda kike son Mijin ki ko Saurayin ki, fiye da yadda yake
son komai na duniya.
Amma kina iya samun wasu Mazãjen sabida son Matar
sa da yake yi, ko tana cikin jinin haila babu Ruwan sa, sabida yayi mata abun
da take so haka zai yarda yayi Jima'i da ita Alhalin tana cikin jinin hailar
fa, kin ga anan me? Ga dokar Allah nan an take shi yanzu sabida irin yadda yake
son Matar sa akan ya ce mata ta yi hakuri Haramun ne, a'a ba zai fada mata ba
gara yayi Jima'in da ita sabida Hankalin ta ya kwanta shikenan.
Wani Kuma za ki ga an yi saki Ukku Allah ya Sanya
musu soyayya sosai a tsakanin su kin ga babu Aure a tsakanin su sai ta Auri
wani Sahihin Aure, amma haka za suyi ta yin Karya har su komar da Auren su an
ba su Fatawar karya, ko kuma kullum su je suna ta yin Zina babu wadda ya sani
sun manta cewa Allah na ganin su, kin ga yanzu ga dokar Allah nan sun take shi
dalilin soyayyar da suke yiwa Junan su, hakan ya hana su bin dokar Allah da
Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wa Sallam, a nasu tunanin babu wadda ya sani
amma sun manta cewa Allah ya sani, kin ga wannan ma Shirka ce Kuma Jama'a
dayawa suna aikata shi sosai.
Haka Matar Aure ce za ki ga Mijin ta Mazinaci ne
babu wadda bai sani ba Kuma ya qi ya tuba ya Dena, ga abun da Allah da Manzon
Allah Sallallahu Alaihi Wasallam suka ce Mazinaci sai Yar uwar sa Mazinaciya a
gurin yin Aure, ga shi Mijin ya qi ya tuba ya dena yin Zinar, sai ki ji Mace ta
ce ai zata zauna da shi don Yaran ta, ko Kuma iyayen ta su ce, toh Ina ruwan ki
da Zinar sa laifin ai nashi ne bawai naki ba, ko kuma Ina ruwan ki Zinar sa zai
shafe ki ne ko Yaran ku? Ki bar sa mana ai qabarin kowa da nashi. Kin ga yanzu
kokarin su shi ne kada ta rabu da shi ta ci gaba da Zama da shi a hakan, ga shi
kuma sai Saɓawa Allah yake yi na yin
Zina ko aikata wani abun Haramun, tana son shi a hakan zata zauna da shi, ba za
ta iya rabuwa da shi ba dalilin uban Yaran ta ne kuma tana son sa ita, yanzu
kin ga anan tana son zama da shi ne domin tana son sa ne, ita babu Ruwan ta
kawai ya ci gaba da yin Zinar sa ko Saɓawa Allah daidai
ne akan ta rabu da shi, tafi yarda ta ci gaba da zama da shi a hakan yana Saɓawa akan ta rabu da shi, kin ga su a nasu tunanin gara a
take dokar Allah tunda Zunubin ba a kanta zai sauka ba tunda akan sa ne, toh
babu komai ta zauna da shi don tana son sa, ga dokar Allah nan cewa Mazinaci
sai Mazinaciya Yar uwar sa, ga shi ya qi ya tuba ya Dena, kika ce a'a Uban
Yaran ki ne kina son sa wallahi za ki zauna da shi a hakan, toh wannan ma
Shirka ce. Kuma ke kin manta cewa Ciwo zai kama ki ne? Kwanan Hakan ya faru
Mijin Mazinaci ne ta qi ta rabu da shi karshe ta sama masa HIV ga shi ya mutu,
ya bar ta da Ciwo sai mu ga ta tsiya kuma, ko dai za ki bi shi da Yaran zuwa
cikin qabarin sa ne tunda Uban Yaran ki ne kuma kina son sa? Indai kina son sa
sai ki bi wallahi da Yaran dukka Nan ne za a gane kina son sa sosai.
Haka kuma za ki ga Uba yana ganin Yar sa tana Saɓawa Allah, tana yin duk abun da take so a rayuwar ta
wadda ba daidai bane, amma sabida baya son fushin Yar sa yana son ta sosai,
kada ya ce ta Dena ta shiga cikin tashin hankali da damuwa yana son ta sosai,
baya Jin maganar kowa indai a kanta ne, domin irin yadda yake son Yar sa, ko
Kuma mu ce Matar sa shiyasa akan ya hana ta Saɓawa Allah gara kawai ya bar ta ta ci gaba yin komai,
domin kada ya bakan ta mata Rai, sai ya ce ai idan lokacin shiryuwan ta yayi ai
zata Dena, toh wannan ma Shirka ce ma Allahu Subhanahu Wa Ta'ala, shi ne
Shirkan soyayya.
Wallahi akwai wadda irin yadda yake son Yan
kwallon Kafa, Arna Makiya Allah da Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam,
Makiya Addinin sa, ko Yan Films wato Fina-Finan Hausa ko Nigerian Films, toh
akan ki zage su gara kin Zagi iyayen sa, za ki Zagi iyayen su ba za su ce komai
ba, za ki yi Ɓatanci ga
Addinin Musulunci ko a jikin su, amma da kin Zagi waɗannan mutanen ko kin yi ɓatanci a kansu, sai Hankalin sa ya tashi, kai wani ma har
fada sai Kun yi da shi, dalilin kawai kin Zagi Yan kwallon Kafa ko Yan Films,
Hankalin sa na tashi idan an taɓo su, toh wannan
ma Shirka ce ga Allah ta soyayya. Toh waɗannan abubuwan
sun yiwa a cikin zuciyar Jama'a wadda ba su ɗauke shi bakin komai ba, alhalin Shirka ce zuwa ga Allah,
shiyasa Allahu Subhanahu Wa Ta'ala yana cewa;
وَمِنَ النَّاسِ مَنْ يَتَّخِذُ مِنْ دُونِ اللَّهِ أَنْدَادًا
يُحِبُّونَهُمْ كَحُبِّ اللَّهِ ۖ وَالَّذِينَ آمَنُوا أَشَدُّ حُبًّا لِلَّهِ ۗ وَلَوْ
يَرَى الَّذِينَ ظَلَمُوا إِذْ يَرَوْنَ الْعَذَابَ أَنَّ الْقُوَّةَ لِلَّهِ جَمِيعًا
وَأَنَّ اللَّهَ شَدِيدُ الْعَذَابِ
Kuma akwai daga mutãne wanda yake riƙon kinãye, baicin Allah, suna son su, kamar son Allah, kuma waɗanda suka yi ĩmãni ne mafiya tsananin so ga Allah. Kuma
dã waɗanda suka yi zãlunci, suna ganin lõkacin da zã su ga
azãba, da cewa lalle ne ƙarfi ga Allah yake duka, da cewa lalle ne Allah Mai tsananin azãba ne.
Sa'annan yana da cikin Shirka zuwa ga Allah shi ne
rashin ɗaukar abun da Allah ya hukuntawa wannan Bawan nashi, Abu
zai Sami mutum sai Rika Jin haushin kansa, ina ma da yayi kaza ai da Abu kaza
Bai same shi ba, ko kuma irin yadda a yanzu shi Saurayin ki ya kawo Baikon ki,
shikenan kasuwancin sa suke yin sa Allah ya jarrabe shi yana yin baya a yanzu,
sai ya Koma zargi da tunanin cewa ai dalilin neman ki da yake yi, dalilin zai
Aure ki dalilin ya kawo Baikon ki shiyasa komai nashi yake komawa baya, yanzu
ke kanki ya fara Jin haushin neman Auren ki da yake yi, domin a nasu tunanin da
shi Saurayin naki kene silar Lalacewar komai nashi, sa'annan yana Jin haushin
Ubangijin sa, ai meyasa kasuwancin sa yake yin baya me yayiwa Allah? zai Rika
yin irin waɗannan tunanin, jama'a ko
Yan Uwan sa, su Rika cewa ai ga dalilin nan domin za ka auro wannan me Bakar
Kafar ce, toh gara ka rabu da ita tun yanzu in ba haka ba zata talauta ka, ai
wane ma haka da Auri wacce, shi ma da me Arziki ne Amma yanzu Bai da komai, a
yi ta zuga shi, duk waɗannan abubuwan
Shirka ce zuwa ga Allah ga duk masu tuna irin wannan.
Ko Kuma mutum ya fara tunanin ai dalilin wannan
abun da ya same shi, ai wani ne ya min ko su wane ne suka min wannan abun, an
San cewa akwai Sihiri kuma Sihiri gaskiya ne, toh amma shi Musulmi ba zai taɓa tuna cewa ai su wane ne suka min ba wai har ma ya Koma
yin gaba da su, har ma ya Koma bin Malamai ko Bokaye wai shi ma zai kare kansa,
duk Shirka ce wannan.
Sabida haka wannan saurayin naki bai siffantu da
mijin da Mace ta Aure shi ba ta ji daɗi ko ta zauna
lafiya da shi ba, duk Namijin da tun a waje ba a ma Yi Auren ba, amma tun yanzu
ga irin abubuwan da yake ta cewa a kanki, toh Ina ga kuma ya Aure ki yana da
iko akan ki? Kin ga kenan Zagi da tozarci da cin Mutunci har da iyayen ki, duk
ba su tsira ba idan ya tashi yin Zagin sa da tsinuwar sa, Kuma ba za ki taɓa samun jin daɗi ko kwanciyar
hankali ba, sa'annan kullum kin Rika shan Zagi da tsinuwa kenan, domin da kin
yi magana bani Abu kaza ko Siya min Abu kaza, toh zai zage ki ya ce ai kene
silan Lalacewar Arzikin sa ko kasuwancin sa.
Don haka ki zauna kiyi tunani me kyau ga wadda za
ki Aura ki sanarwa iyayen ki idan kin Yanke Hukunci, Amma dai wannan saurayin
naki matukar bai ji tsoron Allah yayi gaggawar tuba ya cire wannan mummunar
tunanin a Zuciyar sa ba, toh lallai ne ya kama Hanyar da babu kyau, kawai
shawarar da zan ba ki Ki rabu da shi. Allah ya shirya ya tsare. Dafatan Kin
gane ko???????
WALLAHU A'ALAMU
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku
kasance damu cikin wannan group domin Fadakarwa...
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.