Citation: Alhassan, B.A. (2024). Tubalan Ginin Turke Cikin Waƙoƙin Yabo Na Ahmad Muhammad (Shehi). Ginshiƙin Nazarin Salon Waƙoƙin Hausa, 506-514. www.doi.org/10.36349/djhs.2024.v03i01.062.
TUBALAN GININ
TURKE CIKIN WAƘOƘIN YABO NA AHMAD MUHAMMAD (SHEHI)
Badariyya Aliyu
Alhassan
Dept of Nigerian
Languages, Bayero University Kano
Tsakure
Daidai da faɗar
Hausawa ko da iska ta zo, ta iske kaba na rawa, domin kuwa, masana da manazarta
sun yi shekaru suna baje-kolin tunaninsu da fasaharsu da tarken tubalan waƙoƙin
baka na Hausa. Ta haka ne, wannan takarda ke da muradin fayyace yadda Ahmad
Muhammad Shehi yake bayyana wa masu sauraransa irin yabon da yake yi wa annabi
Muhammad, sallallahu alaihi wa sallama a ɗiyan
waƙoƙinsa.
An gina wannan takarda ne bisa ra’in
Waƙar
Baka Bahaushiyya (WBB). A ɓangaren
dabarun gudanarwa kuwa, an yi amfani ne da fasalin bincike sharhantacce. Domin
wannan takarda ta ginu a kan fayyace yadda shehi ya ke gina waƙoƙinsa,
inda yake bayyana girma da matsayin annabi Muhammad, sallallahu alahi wa
sallama a gurin allah subhanahu wa ta’ala
da kuma irin soyayyar da yake yi masa a cikin zuciyarsa.
Fitilun Kalmomi: Tubala, Ginin Turke, Waƙoƙi,
Yabo, Ahmad Muhammad (Shehi)
Gabatarwa
Waƙar baka tana da ɗaɗɗen tarihi a rayuwar Hausawa.
Wannan a bayyane yake cewar makaɗan
baka na Hausa suna da wani giɓi
na adabi da suke cikewa a rayuwar al’umma ta hanyar yin amfani da baiwar hikima
azanci na fasahar shirya zantuka da allah ya huwace musu. Waƙa
babban reshe ce ta adabin Hausa, musamman na waƙar baka wacce ita ta fara samuwa tun
lokaci mai tsawo kafin rubutacciya. A wannan bincike an yi amfani da ra’in Waƙar
Baka Bahaushiya (WBB) da Gusau (2003 da 2011 da 2014) ya gabatar a ayyukansa.
Wannan ra’i na ƙunshe da wasu matakai ko dabarun na turken waƙar
baka. Har ila yau ra’in WBB na magana ne a kan tsarin waƙa a ƙungiya
da kan ƙunshi
jagora wanda ke ƙulli da kuma ‘yan amshi waɗanda
sukan yi wa jagora ƙari wajen isar da saƙo. Wannan bincike an ɗora shi a kan sharhantaccen
bincike (ƙaulitatiɓe research) wata hanya ce
ta tattara bayanai da nazarin tare da rubutu rahoto mabambanta daga dabarar
bincike ta adabi. Wannan bincike ya tattaro bayani tare da ƙididdiga
da samo hanyoyi yayin gudanar da shi.
1.1 Taƙaitaccen Tarihin Ahmad Muhammad (Shehi)
An haifi ahmad Muhammad sabi’u shehi mai tajid’izzi, a
unguwar dukawa ta tsakiyar birnin kano a ƙaramar hukumar birni da kewaye a shekarar
6/2/1995. Tun yana ƙarami ya taso da hazaƙa da saurin haddace abu aƙwakwalwarsa.
Ya fara karatun addinin musulunci a hannun mahaifiyarsa, kasancewar gidansu
gidan malamai ne. Ana yi masa laƙabi da shehi mai tajid’izzi.
Shehi ya fara koyon karatu da rubutun boko tun a gida kafin
ya shiga makarantar firamare ta ‘yan awaki a shekarar 2004 ya gama a shekarar
2010. Daga nan ya shiga ƙaramar sakandare da ke sabuwar ƙofa a shekarar 2010. Daga nan ya tafi
babbar sakandare ta ƙofar nasarawa inda ya gama a shekarar 2016. Tun kafin ya gama
makaranta yake tare da masu gudanar da waƙoƙin yabo na annabi Muhammad sallallahu
alaihi wa salam. Hakan ya ba shi damar haddace waƙoƙi masu yawan gaske, waɗanda yawancin duk na yabo
ne. Sannan ko a makarantar islamiyya shehi gwani ne wajen iya tsara waƙoƙin
yabo musammman a lokacin bukukuwan maulidi. Ya yi ƙungiyoyin yabo da yawa a
matsayin masu kula da kayan sauti, daga baya ya zama daga cikin masu yin amshi.
Bayan ya gama makarantar sakandare sai ya shiga harkar waƙoƙin
yabo, inda ya kafa tasa tawagarsa ta ƙashin kansa. Ya kafa tawaga mai ƙarfin
gaske, wacce in dai game da harkar yabo ce, ana iya cewa ya tsere sa’o’insa. A
yanzu ahmad shehi ya wallafa waƙoƙin yabon annabi Muhammadu sallallahu
alaihi wa sallam, masu yawan gaske. Haka kuma akan kira shi wurin bukukuwan
aure ko suna domin ya rera waƙoƙin yabo a ciki da wajen jihar kano. Shehi
yana da halaye na ƙwatance ma’ana yana da kyawawan ɗabi’u,
waɗanda sun cancanci a
yi koyi da su; kamar son ibada da karatun addini da son fiyayyen halitta annabi
Muhammad, sallallahu alahi wa sallama. Mutum ne mai yawan fara’a da barkwanci,
sannan ma’abucin sa suturar alfarma, mai girmama mutane ne da baƙi da
maƙwabta.
2.1 Ma’anar Turke ta Lugga
Turke ta fuskar lugga na nufin itace ko wani ƙarfe
mai tsawo wanda ake ɗaure
dabba da shi, ko ɗaure
wani abu (Gusau, 2008:369).
Ɗaure wani abu (Gusau, 2002:295).
Turke shi ne riƙe mutum ko kafe shi har sai ya faɗi wata maganar da ya
shirya, ko a tona masa asiri kan wata ƙarya da ya yi ko kuma a riƙe shi
sai ya yi wani aiki da ake buƙatar ya yi (Bargery,1934:1034) (CNHN,
2006:446).
2.2 Ma’anar Turke a Fannin Ilimi
Gusau (2008:370) ya ce turke a ƙa’idar masu nazarin waƙar
baka na nufin saƙon da waƙa take ɗauke
da shi. Idan an ce saƙo kuma ana magana ne kan manufar da ta ratsa waƙa tun
daga farkonta har zuwa ƙarshenta, ba tare da karkacewa daga ainihin abin da ake zance
a kansa ba. Gusau (2008:370) ya kuma bayyana yanayin turke a waƙoƙin
baka suna da manyan manufofi a kowace waƙa za a sami turke guda wanda aka gina ta
a sababiyyarsa. Akwai kuma ƙananan manufofi inda akan kawo wasu maganganu don su taimaka
daɗa fito da babbar
manufa wadda ita ce aka ba suna turke, ƙananan manufofin nan su ake kira tubalan
ginin turke. Gusau (2008:371) ya bayyana manyan turakan waƙoƙin
baka na Hausa sun haɗa
da yabo zalla da zuga zalla da yabo surke da zuga da zambo da ta’aziyya da
wayar da kai da tarihi da siyasa da kishin ƙasa da soyayya da wasa kai ko koɗa kai da taya murna da
sauransu.
Kings (1980:29) ya bayyana ma’anar turke shi ne wanda ake
harhaɗa ɗiya gwargwadon buƙata
ana yi ana gwama dangantaka a tsakaninsu, ta kusa ko ta nesa, har su bayar da
ma’ana bisa manufar da ake son isarwa.
Tubali ta Fuskar Lugga
Tubali ta fuskar lugga na nufin curin ƙasa da
aka yi ya bushe dan gini (CNHN, 2006:440)
Tubali ta Fuskar Fannin Ilimi
Ma’anar tubali ta fuskar nazari, wato fannu, tubali na nufin
wani ko wasu saƙonni da akan samo a cikin waƙa da makaɗa
da mawaƙa
ke tsattsarmawa a mabambantan gurare. Tubalan ginin waƙa wasu ƙananan
saƙonni
ne da ake gwamawa don ƙara ƙulla waƙa ta yi tsawo amma ba su ne babbar manufar waƙa ba.
Kuma kowane babban turke akwai nau’o’in tubalan da suka dace da shi. Ƙaramin
saƙo
shi ne wanda ake ginawa a cikin ɗan
waƙa
ɗaya, ba kasafai ne
yake zarcewa zuwa wani ɗan
ba a zubi irin na waƙar baka. Za a iya samun waƙa ɗaya
ta ƙunshi
tubalai da dama gwargwadon yadda makaɗin
ya tsara da kuma yadda yake tunanin zurfafa manufar. (Ɗangambo, 2007:14) da (Gusau,
2002:35) (Gusau, 2003:30) tubalan ginin turke ke nan suna nufin wasu maganganu
da aka bi aka ƙuƙƙulla waƙa da su don ta ƙara tsawo, amma ba su ne babbar manufar
waƙar
ba. Misali idan turken waƙa na ‘yabo’ ne, a cikin waƙar za a iya kawo wasu abubuwa waɗanda ba lalle sai a kan
yabo suke magana ba, amma za su iya ƙara wa waƙar kyau da armashi. (Gusau, 2003:30) ya
bayyana kowane ‘turke’ da tubalan gininsa da suka fi dacewa da shi. Alal misali
a turken yabo an fi amfani da ambaton addini da asali ko nasaba da karamci ko
kyauta ko tarihi da sauransu a lokacin da ake ƙoƙarin faɗaɗa shi.
Satatima (2009:82) ya bayyana ma’anar tubali cewa ya yi
cikin hikima ne mawaƙan baka sukan zaɓi
turken waƙarsu
su kuma ƙayatar
da shi ta amfani da ƙananan turaku wato tubalan ginin turke, ko kuma raɓa dannin turke kamar yadda
wasu sukan kirasu. Alal misali idan waƙar turkenta na yabo ne, to sai ka ga mawaƙi ya
taɓo nasaba da riƙo da
addini da kyauta ya tsara wannan yabo nasa da shi.
Umma (2021) ta bayyana tubali na nufin saƙonni
da mawaƙan
baka kan yi amfani da su a cikin waƙoƙinsu domin taimakawa wajen fito da babban
turke. Kaɗan daga
cikin tubalan akwai yabo da zambo da habaici da zuga da kirari da makamantansu.
Tubalin ginin turke yana nufin ƙaramar manufa ko saƙo a
zubin ɗiyan waƙa.
Tubali shi ne ake sassarƙawa a fito da babbar manufa ta waƙa. Tubali shi ke kyautata
tunanin makaɗa wajen
samun manufar waƙa (CNHN, 2006: 446).
3.0 Tubalan Turke a Wasu Waƙoƙin Ahmad
Muhammad Shehi
Binciken gaba ɗaya
an yi shi ne a kan turken yabon ma’aiki da sahabbansa da iyalansa da kuma
tubulan da aka yi amfani da su a ya yi gina wannan turken waƙoƙin.
Daga cikin tubalan da wannnan takarda ta ɗauka
za ta kawo misalansu sun haɗa
da: tubalin mu’ujiza da jarumta da kyakkyawan asali da kyawon halitta da kyawun
ɗabi’a.
3.1 Mu’ujiza
Mu’ujiza tana nufin wata baiwa ta musamman wanda kan faru ga
wani annabi kamar tsagewar wata ga annabi Muhammad (CNHN, 2006:354).
Mu’ujiza kalma ce ta larabci kuma tana nufin gajiyawa, wani
lokaci kuma ta ɗauki
ma’anar wasu ayyuka na ban mamaki da ta’ajibi waɗanda
babu mai ikon gudanar da su sai allah maɗaukaki,
to sai ubangiji allah ya hore wa annabawa ko manzanni su dinga gudananr da su
don ya gajiyar da mutanensu ko kuma don ya tabbatar musu da hujjar lallai shi
annabi ne ko manzo, musamman waɗanda
suka bijire masa suka ƙi gaskata shi. Mu’ujiza takan zama wani abin ta’ajibi wanda
mutane ba za su iya aikatawa ba. Haka kuma mu’ujiza tana da sharuɗa da kuma ƙa’idoji
da suka haɗa da:
Lallai ne ta zama ɗaya
daga cikin ayyukan allah waɗanda
babu wani daga cikin mutane wanda zai iya irinta;
Wajibi ne ta saɓa
wa al’ada wato ta zama abin da mutane ba su gani ba;
Haka kuma wanda duk ba annabi ko manzo ba ba zai iya aikata
irinta ba;
Sannan kuma, ta zamanto ta gudana ne a lokacin da aka yi
jayayya, ko aka yi ƙure, ko kuma don ƙara wa jama’a imani;
Kuma lallai ne ya zama tafi to daga wajen mutumin da ya zo
da saƙo
na annabta ko na manzanci
(Adamu 2014:8-9) cikin (Nura da Ahmad 2018:169).
Mu’ujiza tana nufin abin da ya saɓa wa al’ada ta tafi da hankali ko mamaki wanda
ta bambanta da ƙara ko duba ko sihiri ko rufa-ido da makamantansu. Kuma allah
yana hore wa annabawa da manzanni ita, domin gaskata da kuma ƙarfafa
abin da annabi ko manzo ya zo da shi. Haka kuma, akan sami mu’ujiza domin ƙalubalantar
masu inkarin annabtar wani annabi ko manzo. Kuma annabawa da manzonni ne ke da
mu’ujiza, wato babu wani wanda ke da mu’ujiza face annabi da manzo (Nura da
Ahmad 2018:169).
3.2 Kyakkyawan Asali
Asali shi ne mafari ko salsala ta mutum ko wani abu. (CNHN,
2006:20).
Halima (2015:35) ta bayyana asali da cewa shi ne mafari ko
fito da tushen wani abu domin a fahimci daga inda ya fito. Kyakkyawan asali shi
ne tushen mutum ya zamo mai kyan. Jinsi wato ta yadda aka same shi ya zama abin
alfahari a gare shi.
3.2.1 Kyawun Ɗabi’a
Ɗabi’a, musamman ta mutum (CNHN, 2006:191). Hali wani abu ne da
bahaushe ke dangantawa da sababben abu. Hali yana da makusanciyar ma’ana da’’
al’ada’’ domin al’adar abu shi ne halinsa. Bahaushe ya lura da hali cikin jini
yake har faufau ba a rabashi da shi, don haka yake hange hali da wasu fuskokin
da yawa cikin zantukansa na yau da kullum irin su:
- Hali zanen dutse
- Mai hali ba ya barin halinsa
- Rai da hali ba a raba su
- Halin uwa ɗiya
kan ɗauka
- Hali abokin tafiya (Bunza, 2009:6)
Ita ɗabi’a
wata aba ce da mutane ko dabba ko wata halitta ta saba yi ko aikatawa (Satatima:147).
Ɗabi’a
asalinta kalma ce ta larabci, tana nufin wani abu da aka saba yi. Kyawon ɗabi’a ko halaye da wani ko
wasu ke yi a zamantakewarsu da mutane wajen mu’amalantarsu. Ita ɗabi’a tana ɗauke da abubuwa da dama a ƙarƙashinta
wanda duk siffofinta ne. Misali, jarumtaka da gaskiya da amana da halaye da
sauransu.
3.2.2 Jarumtaka
Gusau (2008:387) ya bayyana kalmar jarumtaka tana nufin nuna
juriya ko ƙarfin
hali ko wata bajinta a lokacin aiwatar da wani abu. Idan an ce mutum mai
jarumtaka ne, to ana nufin gwarzan namiji ne, mai taurin hali, ko mai nacewa ga
al’amari ko maras tsoro wanda ba ya firgita balantana ya samu faɗuwar gaba. Mai jarumtaka
yakan sa gabansa inda ya nufa ba tare da ya ja da baya ba, bai kuma yin
waiwaye, bai karkacewa, sai ya kai inda ya dosa. Gusau (2007:387) ya kuma
bayyana turken jarumta yana tafiya kafaɗa
da kafaɗa da turken
yabo mai surke da zuga. Bisa yawanci makaɗan
jarumtaka sukan yabi gwarzayensu ne ko kuma su zuga su ta yadda za su ƙara
bajinta. Domin haka, turken jaruntaka yana da dangantaka makusanciya da turken
yabo mai haɗe da zuga.
Tubalan ginin turke a waƙoƙin shehi
A wajen ginin tubali a waƙar bege mawaƙa suna amfani da kaifin
basira wajen fito da ƙananan saƙonni domin faɗaɗa babbar manufa a kowace waƙar
yabo, tare da yin la'akari da wanda suke yi wa waƙar, domin yin taka-tsantsan wajen ƙwarewa
tare da kiyaye mutuncinsa, tare da nuna tsananin soyayyarsu da ƙaunarsu
a gare shi. Haka kuma
Kowacce waƙa na ƙunsar nau'o'in tubalai daban-daban da
suka dace da babbar mabufa ta waƙar yabo.
Bugu da ƙari, ta wani ɓangaren
tubali a waƙar
yabo shi ne yadda mawaƙa da makaɗan
yabo suke amfani da tubalan da suke ƙara wa al 'ummar Hausawa musulmai
soyayyar annabi Muhammad, sallallahu alaihi wa sallama a cikin zukatansu. Da
kuma son masoya annabi Muhammad sallallahu alaihi wa sallam da kuma kyautata ɗabi'un jama'a ta hanyar yin
koyi da annabi Muhammad sallallahu alaihi wa sallama.
Tubalan da shehi ke amfani da su wajen gina waƙoƙinsa
domin jan hankali da kuma isar da saƙon da yake san isarwa ga jama'a. Waɗannan tubalan sun haɗa da mu’ujiza da jarumta da
kyakkyawan asali da kyawon halitta da sauransu.
4.0 Tubalin Mu'ujiza
Ahmad Muhammad Shehi makaɗi
ne wanda yake da zalaƙar harshe domin isar da saƙo ga jama’a, kuma yana amfani da kalmomi
masu nauyi cikin Hausar karin harshen kananci. Sannan yakan fayyace kyan ɗabi’u da kyawon fuska da
kyauta da zamantakewarsa da jama’arsa annabi Muhammad sallallahu alaihi wa
sallama, ta amfani da gina tubalan ginin turke a waƙokinsa. Shehi a cikin waƙoƙinsa
yana ambaton mu'ujiza ta annabi Muhammad sallallahu alaihi wa sallama wanda ba
a ba wa wani irinta ba. Misali a cikin waƙarsa mai suna ya gayatul huna yabon ka ba
za ni bar shi ba.
Jagora: Har yau ban ga wanda ya kira yi wata ya tsaga shi
ba,
:Har yau ban ga wanda ya yi magana da matacce ya bi shi ba,
:Har yau ban ga wanda abincinsa ya ya beshiba da kan shi ba,
:Har yau ban ga wanda raƙumi ya yi ƙara a gurinsa ba,
:Har yau ban ga wanda zaki ya zabure ya tare shi ba,
:Har yau ban ga wanda rai ya fice kuma ya mai da shi ba,
:Har yau ban ga mai mayar da itace takobi a hannunsaba,
:Har yau ban ga wanda rabbi ya ke hidima a gare shi ba,
:Har yau ban ga wanda in ba shi musulunci bai cika ba,
:Sai mai sirrin subuhun ƙuddusin ya mujitafa.
'Y/amshi: ya gayatul huna yabon ka ba za na bar shi ba.
(Waƙar Ya Gayatul Huna ɗa
na 12 mp3).
A wannan ɗan
waƙar
Ahmad Muhammad Shehi ya bayyana yadda mu’ujiza annabi Muhammad, sallallahu
alaihi wa sallama ta ke wanda ya kira wata ya zo, sannan kuma ya tsage biyu.
Wannan abin ya faru ne a lokacin da mutanen makka suka tambayi annabi da ya
nuna musu wata aya da za su gaskata shi, shi annabin allah ne. Sai annabin Muhammad
tsira da amincin allah su ƙara tabbata a gare ya kirawo wata sannan kuma ya tsage biyu.
Sannan yana daga cikin mu’ujizar annabi ya yi magana da matacce. Shehi ya kuma
kawo wata mu’ujizar annabi Muhammad sallallahu alaihi wa sallama inda dabbobi
suka kawo masa ƙarar iyayen gidansu kamar raƙumi da ya kawo wa annabi ƙara a
kan mai kiwon sa zai yanka shi bayan tun yana da ƙarfinsa yake yi masa bauta, yanzu da
girma ya kama shi zai yanka shi. Annabi Muhammad, sallallahu alaihi wa sallama
ya yi wa wannan mutumin magana da ya rabu da shi. Shehi ya bayyana annabi ya
mayar da itace takobi a hannunsa a lokacin yaƙin hunainu, sai annabi ya zari zangarniya
sai ta zama takobi da ya kai sara sai dai kafirai su dunga faɗuwa. Kuma babu wanda rabbi
yake hidima a kansa sai annabi, wanda idan ka yi wa annabi salati ɗaya allah zai yi maka goma.
Shehi ya bayyana inda ba ka ambaci annabi Muhammad sallallahu alaihi wa sallama
a yayin kalmar shahada ba to musulunci aka bai cika ba. Har sai ka ambace shi
sannan musulunci ya cika. Misali.
Jagora :Ya mai bayyana gaibu ya mai sanin fili ga baɗini,
:Mai magana da kafaɗar
tunkiya an yanka tun tuni,
:Kai ke zanta zantuka da barewa ya mu'azzami,
:Haka rabbu ya yi maka baiwa ba za a sanka ba.
(waƙar ya gayatul huna ɗa
na 13 mp3).
A nan, Ahmad Muhammad Shehi ya bayyana annabi Muhammad
sallallahu alaihi wa sallama ya san gaibu duk abin da zai faru ya san shi kafin
ya faru. Wannan abin ya faru ne lokacin da aka kama abbas a matsayin bawa sai
aka ce ya fanshi kansa, sai ya ce ba shi da kuɗi.
Sai annabi ya ba shi labarin abin da suka yi da matarsa a kan kuɗin da ya bar mata, abbas ya
yi mamakin abin da annabi ya faɗa
don ya san babu wanda ya sani. Yana daga cikin mu’ujizar annabi ya yi magana da
ƙafar/katarar
akuya bayan an yanka
Ta, inda take faɗa
masa an yi masa sihiri a cikinta ka da ya ci. Babu wanda ya yi wannan sai
annabin ƙarshen
zamani.
Bugu da ƙari shehi a cikin wata waƙarsa mai suna labbaika ya kuma bayar da ɗiyan waka da ke ɗauke da mu'ujizar annabin
tsira alaihimul salatu wassalamu, kamar haka:
Jagora: Tsarki ya tabbata gurin ainun yaƙini
farkon duba,
:Wanda aka baiwa biyar waninsa banji ya samu ba,
:Wanda girgije ya ke yi wa inuwa waninsa bai samuba,
:Mai rugurguje gunki da masu bautarsa basu tanka ba.
Jagora: Ma abocin mu'ujiza da take shedarka,
:Wacce duk sakan take nuna muƙaminka,
:Ga maziya ta kankanka a kayinka,
:Mai ƙarfi boye ya tsarata,
:Ga muƙami aliyu na zatunka,
:Wanda ko nubuwa ba ta samu a nan. (waƙar
labbaika ɗa na 4 mp3).
A wannan ɗan
waƙar
yana jaddada wa akan tsarki ya tabbata a gurin annabi Muhammad wanda dama shi
tsarkakakke ne shi ne farkon duba a gurin allah subahanahu wa ta’ala. Wanda
allah ya baiwa salloli guda biyar da ya umarci al’ummarsa da yi, an bashi waɗannan sallolin ne lokacin
da ya je ganawa da allah. Wanda babu wani annabi da ka ba wa. Shehi ya bayyana
annabi Muhammad sallallahu alaika wa sallama sabo da mu’ujizarsa har girgije ne
yake yi masa inuwa a lokacin da suka je sham da maisaratu yaran nana khadija.
Shehi yana bayyana ita kanta mu’ujiza tana shaidawa shi annabin allah ne wanda
har take nuna muƙaminsa a gurin allah subhanahu wa ta’ala.
5.0 Tubalin Kyakkyawan Asali
Shehi a cikin wasu ɗiyan
waƙoƙinsa
ya kawo kyakkyawan asalin annabu muhammmad sallallahu alaihi wa sallama da
yadda allah ya halicce shi da haskensa. Misali a cikin waƙar
salamu alaika ga abin da shehi y ace:
Jagora :Ka zo kana ta kaɗaita
buwayaar ainihin asalinka,
:Ka sanu daidaito da abin da ya zamo ainihinka,
:Ka samu yaƙinin ce wa an same ka,
:Ka wanzu kai ka yi fanadi har ka fito ka koma cikinka,
:Sunanka ya yi kama da abin da sufar jikinka ta ɗauka,
:Ka kore biyun ka kasa ɗaukar
numbar biyunka.
J agora:A lokacin ba jijabai da suke rufe ɓuyanka,
:Ba wata ba rana ba mai sheda e da akwai ka,
:Sai dai haskenka da asalin haskenka.
Jagora :Tun babu sammai ba ƙassai ba bauta bare aljanna
:Ba malakai ba insi da jinni bare a ba su su zauna,
:Kana nan cikinsu kana ta yin sha’aninka.
(wakar salamu alaika ɗa
na 13 da 14 da 16 da 17 mp3).
A nan, Ahmad Muhammad Shehi ya bayyana allah ya halicci
hasken annabi ne tun kafin ya halicci komai na duniya. Wato ba wata ba rana ba
sammai da ƙassai
ba mala’iku ba insi da jinni sai hasken annabi Muhammad sallallahu alaihi wa
sallama wanda da shi ne aka halicci komai na duniya.
Jagora: Kai ta bauta wa rabbul arshi cikin hijaban mulki,
:Ka kure bauta da daɗaɗɗan mamaki,
:Har sai da ibadar ta zamo siffar sunanka.
Jagora :Daga nan aka fara hijabai dan rufe matsayinka,
:Kai abin da ka yi a cikinka ta yadda ba mai biyo ka,
:To wa ma zai biyo ka bayan ba hanyar biyoka.
Jagora : Sai aka nufin samar da abin da babu a zati,
:Komai da komai ya samu cikin ƙudirar iklahil baiti,
:Ta wannan hasken da shi ne asalinka.
(waƙar salamu alaika ɗa
19 da 20 da 21 mp3).
A cikin wannan ɗiyan
waƙar
ya kawo inda allah ya halicci annabi yana ta bautawar allah a cikin hijaban
ubangiji ya daɗe da
halittarsa kuma yana bauta masa, har sai da allah ya mayar da ibadar ta zamo
siffar sunansa. Wato lokacin da allah ya yi nufin halittar ɗan adam, sai aka halicce
shi da siffar sunan annabi Muhammad sallallahu alaihi wa sallama daga cikin
hasken da allah ya halicce shi. Ga abin da shehi y ace:
Jagora: Aka fara ƙaddara Adamu domin fitar da jikinka,
:Aka yi masa suffa da irin sunanka,
:Mimun ha’un mimum dalun in dauwamarka,
Jagora: Sai ya hau aiki ya samu hauwa’u alfarka,
:Su ka shiga jannatul fiddausi gidan ni’imarka,
:Aka yi abin da aka yi sha’anin akwai wata harka.
(waƙa salamu alaika ɗa
na 23 da 24 mp3).
A cikin waɗannan
ɗiyan waƙa ya
bayyana allah subahanahu wa ta’ala ya fara halittar annabi Adamu domin ya
halicci ɗan adam a
doran duniya, wanda duk mutanen duniya ta tsatson annabi Adamu suka fito. Kuma
allah subahanahu wa ta’ala da ya halicce ɗan
adam sai ya yi masa siffa da irin sunan annabin Muhammadu, sallallahu alaihi wa
sallama cikamakin annabawa wato mimun ha’un mimun dalun. Daga nan sai allah ya
halicci hauwa’u daga ƙashin kirjin annabi Adamu wannan duk ya faru ne alfarmar
annabin tsira. Sai allah ya saka su cikin aljannar firdausi su zauna. Daga nan
sai allah ya halicci shitu wanda hakan yana nunawa annabi Muhammadu sallallahu
alahi wa sallama shi ne zai bayyana a ƙarshen annabawa.
Jagora : Tafiya tana tafiya aka haifo shitu ba shi da sani,
:Koma bayan yadda aka saba a cikin ikiwani,
:To a nan aka gane akwai babbar harka.
Jagora: Ya zahirin daga nan ne sai ka fara zagaya garinka,
:Ka na ta juyawa a mahaifa wadda ba ta shirka,
:Kana biyo zamanai domain cikar sharaɗinka.
Jagora :A kwana a tashi sai ibrahima ya ɗauka,
:Har ka ba shi salama randa ya haɗu da dabar shirka,
:Ba ka barshi ba har sai da ya gina maka daularka.
(waƙar salamu alaika ɗa
na 26 da 27 da 29 mp3).
A nan, Ahmad Muhammad Shehi ya bayyana allah subahanahu wa
ta’ala ya halicci annabi Ibrahim wanda da ya haɗu
da dabar shirka sai da allah ya ba shi mafita kuma ya kare shi daga wutar da
suka sanya shi a ciki don su halakar da shi. Annabi ibrahim bai gushe ba har
sai da ya gina ka’aba a makka wanda yanzu ake bautar allah a wurinta. Shehi ya
kawo waɗannan:
Jagora :Daga nan sai babban baba ya ce da umma,
:A samu mai matar kirki ma’ana mai himma,
:Da ma da akwai haka lokaci ne ya sauka, jagora : aka yi
juyi sai aka yi cikinsa akwai ƙasaita,
:Harka ya yi tajalli ina maganar annabta,
:Sai rabi’ul auwalu ta zo mana barka.
(waƙar salamu alaika ɗa
na 31 da 32 mp3).
A wannan ɗiyan
waƙoƙin Ahmad
Muhammad Shehi ya bayyana kakan annabi abdulmuɗallib
ya ce a samo wa mahaifin annabi matar aure wanda bayan an yi masa aure aka sami
cikin annabi Muhammad sallallahu alaihi wa sallama wanda aka haife shi a watan
rabi’ul auwal sha biyu ga ranar litinin. A wannan rana haƙiƙa anga
abin mamaki a wannan rana da aka haifi annabin annabawa, wanda kowa
albarkacinsa yake ci . Allah ka yi salati ga shugaba annabi Muhammad sallalahu
alaihi wa sallama. Shehi ya ƙara da cewa:
Jagora: Sannu da zuwa ga ka ka zo arabiyyu abdayyu,
:Sannu da zuwa hashimiyyu arabiyyu ƙuraishiyyu,
:Barka da sauka mafi tsarkin nasaba mafi alfarma,
:Barka da sauka mai babban burni ƙiyasul umma,
:Barka da sauka mai tutar shiriya runfar salama,
:Barka da sauka ya gatan aiki baiti na ke ma,
:Barka da sauka ainin ni’ima da salama,
:Ka yarda na ganka cikin siffar girmanka.
(waƙar salamu alaika ɗa
na 33 mp3).
A nan, Ahmad Muhammad Shehi ya yi wa annabi barka da zuwa
wannan duniyar da kuma jinjina a gare shi. Sannan kuma ya bayyana annabi
balarabe ne, kuma ɗan ƙabilar
ƙuraishawa.
Kuma annabi shi ne mafi tsarkin annabawa mafi alfarma. Shehi ya bayyana annabi
aka ba wa tutar shiriya da al’ummarsa tare da salama. Annabi Muhammad
sallallahu alaihi wa sallama shi ne ni’ima ga kowa sannan shi salama ne ga
mutane baki ɗaya.
Shehi ya yi roƙo da allah ya sa ya ga annabi cikin siffar girmansa.
6.0 Tubalin Kyawun Ɗabi'a
Ahmad Muhammad Shehi yana amfani da wannan tubalan gurin
gina waƙoƙinsa.
Yana
Faɗar
kyawun ɗabi’ar annabi Muhammad
sallallahu alaihi wa sallama. Ga abin da ya ce:
Jagora : Kyan ɗabi’a
sai saduƙul
amin,
: Tausayi sai akramul akrami
: Haƙuri sai akramul amin,
: Duk kyan tadodi sun taru a gurinka.
‘Y/ amshi: Ya rasulullah musɗafal
arabi labbaika.
(waƙar musɗafal
arabi ɗa na 25 mp3).
A nan, annabi Muhammad sallallahu alaihi wa sallama yana da
kyan ɗabi’a ga tausayi
ga al’ummarsa. Sannan ga haƙuri da duk mutanan da suka yi masa wauta. Kuma sai ya yi musu
addu’a akan allah ya shirya su don ba su san shi annabin allah ba ne.
Jarumtaka:
Ahmad Muhammad Shehi a cikin waƙoƙinsa ya kan yi amfani da
tubulin jarunta domin ya faɗi
jarumtakar annabi Muhammad sallallahu alaihi wa sallam a gurin yaƙi.
Misali
Jagora : Sarkin yana
burge ni idan na hango shi can da takobi,
:Wannan ke nan ya kuma idan ya yi danƙa da hannun rabbi,
:Sarki kusama ke nan kaga sirrin haske rabbi,
:Ya raƙibul ƙasuwa a hawanka ba irin na kowa ne ba.
Jagora : Sallama ga
mafi ƙarfi
a dantsan nan.
: Sallama ga mafi kashe kafire a gurin yaƙin
nan.
(waƙar labbaika ɗa
na 16 mp3).
A misalin ɗiyan
waƙar
da aka kawo a sama, Ahmad Muhammad Shehi ya nuna annabi yana burge shi a
lokacin da ake bayar da tarihi ya ɗauki
takobi, sannan kuma a lokacin da yaƙi allah da kansa ya ce shi ya yi wannan.
Sannan ya kuma cewa allah ya ƙara sallama ga mafi ƙarfin
dantsen wato annabi Muhammad shi ne yake da dantse da yafi na kowa. Sannan
annabi Muhammad sallallahu alaihi wa sallama shi ya fi kowa kashe kafirai a
gurin yaƙi
daga ya kai sara sai ɗai
kawuna su dunga faɗuwa.
7.0 Tubalin Kyawon Halitta
A cikin irin waƙoƙin yabo da Ahmad Muhammad Shehi ya ke yi
yana faɗar irin kyawun
halitta da allah ya yi wa annabin ƙarshen zamani wato annabi Muhammad
sallallahu Alaihi wa sallama wanda ba a yi wa wani annabi kafinsa ba. Shi ne ƙarshan
kyau, duk wani mai taƙama da kyawo a ƙasansa yake. Misali :
Jagora : Mai mulkin duk duniya ƙiyama sarki ne kai
munzali,
: Kai ne mai ido ga kyallin fuska ga ka da ƙyalƙyali,
:Ga ka da tsarin girarka ga idonka da tozali,
: Kyautar kyau kai ne ka fara ban ji waninka ba,
'Y/amshi : Ya gayatul huna yabonka ba za na bar shi ba.
(waƙar ya gayatul huna ɗa
na 10 mp3).
Ga wani ɗa:
Jagora : Mai mabayyanin launi siffarka ba irin siffa ba,
: Ga ka da jiki sai dai ban ji jikinka ya yi inuwa ba,
: Ga shi in ka taka ƙasa sawunka ba zai yo sheda ba,
: Zai riƙa idanun shi zai ga duk abin da ake saƙawa.
'Y/amshi : labbaika masani wanda ilahu ya ke yi wa tarba.
(waƙar labbaika ɗa
na 14 mp3).
A ɗiyan
waƙoƙin da
suke a sama Ahmad Muhammad Shehi ya bayyana annabi Muhammadsallallahu alaihi wa
sallama shi ne mai mulkin duk duniya har da ƙiyama. Sannan kuma ga shi da kyawon ido,
fuskarsa ɗauke da
kyalkyali, kuma girar annbai mai tsari ba irin ta kowa ce ba. Annabi shi ya yi
kyautar kyau. Ya kuma launin siffar annabi ba irin ta kowa ce ba, kuma jikin
annabi ba ya inuwa kamar yadda na sauran mutane ya ke yin inuwa. Annabin tsiya
idan ya taka ƙasa sawun ƙafarsa ba ya fitowa.
Ahamad Muhammad shehi a cikin waƙarsa ta musɗafal arabi ya kuma bayyana
kyawon halitta na annabi Muhammad tsira da amincin allah su ƙara
tabbata a gare shi. Misali
Jagora : Balaraben allah
kuma mujauhari,
: Mai gogar giyar fata ja madorari,
:Antal zainun akyari,
:Babu gwanin da za ya bayyana kyawunka.
'Y/amshi: Ya rasulullah musɗafal
arabi labbaika.
(waƙar musɗafal
arabi ɗa na 23 mp3).
A nan, ya bayyana annabi Muhammad sallallahu alaihi wa
sallama balarabe ne, kuma bawan allah mujauhari. Annabi tsira ƙirar
fatarsa mai kyau ce da kuma santsi ba irin ta kowa ce ba. Duk wani kyau na
kyawon halitta ya tabbata a gurinsa.
8.0 kammalawa
A wannan takarda an yi magana ne game da tubalan ginin turke
na waƙar
Ahmad Muhammad Shehi ta yabon annabi Muhammad, sallallahu alaihi wa sallama. An
kawo misalan ire-iren tubalan ginin turke da ke cikin wannan waƙa.
Kamar yadda aka lura a takardar nan, Ahmad Muhammad Shehi yana amfani da dabaru
na jefa ƙananan
saƙonni
a zubin waƙar.
Ta haka ne ya saƙa ƙananan saƙonni waɗanda
suka da ce da babban turke na wannan waƙa masu nuna irin daraja da matsayi da
annabi Muhammad, sallallahu alaihi wa sallama da kuma son da yake yi wa annabi Muhammad,
sallallahu alaihi wa sallama yana kuma bayyanawa mutane da su so shi domin shi
ne mafita a duniya da lahira. Kuma addini baya cika sai an ambace shi.
Manazarta
Abbas, U.A. (2021). Warwarar tubalan ninin turken waƙar
almajiri ta haruna aliyu ningi. yojallac: yobe journal of language literature
and culture, 9 (1) 245:252
Adamu, T.M (2011). Nazarin a kan waƙoƙin yabon annabi
sallallahu alaihi wa sallam. kundi na goma sha shida zuwa na goma sha bakwai,
takardun tattaunawa ɗaliban
hau 3304. sashin koyar da harsunan nijeria, jami’ar bayero.
Bargery, G.P (1934). Hausa english dictionary. Oɗford University press.
Bunza, A.M (20009). Narambaɗa.
Ibrashi islamic
CNHN, (2006). Hausa dictionary. Jami’ar bayero kano.
Ɗangambo, A. (2007). Ɗaurayar gadon feɗe waƙa (sabon tari): k.d.g publisher limited
Gusau, S.M (2002). Salihu jankiɗi: sarkin taushi. Baraka publisher limited
Gusau, S .M (2008a). Dabarun Nazarin Adabin Hausa. Benchmark
Publisher
Gusau, S .M (2008b). Waƙoƙin Baka A Ƙasar Hausa. Benchmark Publisher.
Gusau, s.m (2014). Waƙar Baka Bahaushiya. Bayero University,
Publisher.
Gusau, S. M (2003). Jagoran Nazarin Waƙa.
Benchmark Publisher Limited
Halima, I (2015). Tarken Turken Koɗa Kai Da Yabo A Waƙoƙin Alhaji Dr. Manman
Shata.
Kundin digiri na biyu. Sashen Koyar Da Harsunan Nijeria,
Jam’ar Bayero, Kano.
King, A. Ɓ (1980). Statement restatement and extension: stanzaic structure
in Hausa Court Songs’ takardar wadda ya gabatar Zaria: Sashen Harsunan Nijeria
Africa Jami’ar Ahmadu Bello.
Lawan, N da Magaji, A (2018). Ƙalailaice Tubalan Ginin Turke a Waƙoƙin
Bege na Hausa. Journal of Multi Disciplinary Studies v.3, no 1.
Satatima, I. G (2009). Waƙoƙin Ɗarsashin Zuciya na Makaɗan Baka. Kundin Digiri na
Uku Sashin Koyar Da Harsunan Nijeriya, Jami’ar Bayero Kano.
________________________
Ɓiew other publications of the Department of Nigerian
Languages, UDUS at: https://www.dundaye.com
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.