Ni a fahimtata ba ka iya raba Malamai da siyasa, saboda tun asali siyasar ta Malamai ce, daga baya ne wasu wadanda ba Malamai ba suka kwace musu kayansu.
Kuma Malamai su ne shugabannin al'umma na asali. Saboda su ne masu jagorantar al'umma a Addininsu da rayuwarsu. Su suke gyara wa mutane duniyarsu da ruhinsu da tarbiyyarsu. Su suke gyara wa al'umma duniyarsu da lahirarsu.
Malamai masu
Nasiha ne wa al'umma, wato su suke nuna wa al'umma maslahohinsu na Addini da na
rayuwa, da abin da zai gyara musu duniyarsu da Lahirarsu.
Ita kuma
siyasa da shugabanci na mulki ta shafi Maslahar al'umma, maslaharsu ta Duniya
da Addini da Lahirarsu. Don haka duk lokacin da aka zo zaben shugabannin
siyasa, to al'umma tana bukatar Malamai su yi musu nasiha, su fadakar da su, su
nuna musu wadanda zabarsu shi ne Maslaha wa al'umma a rayuwarta da Addininta.
Saboda haka
lallai Malamai suna da alaka da siyasa. Ba za a ce sun kwace ma 'yan siyasa
kayansu ba, har ma 'yan siyasar suna cewa; bai kamata Malamai su hada biyu ba;
jagorancin Addini da na siyasa.
wannar
magana ba dadai ba ce. Ba a raba siyasa da Addini. Kuma asali siyasar ta
Malamai ce, daga baya ne aka fi karfinsu a kan kayansu.
Daga karshe
wani abu da na fahimta shi ne; idan ka lura, za ka ga cewa; dan siyasa, dan
jam'iyyar PDP shi ne yake sukar Malamai da cewa; sun shiga siyasa. Saboda yana
jin takaicin Malamai sun fadakar da al'umma, sun ce a zabi Buhari. A bayansa
kuma suka ce a zabi Muslim-Muslim ticket, alhali duka 'yan APC ne. To wannan ya
sa dan PDP a kullum yana ganin Malamai sun ba ta masa siyasa, sun kwace musu
harka. Har ya zargin Malamai da saka manyan riguna, alhali kwalliya abu ne mai
kyau a Shari'a.
Amma kuma
fa, duk da haka zargin da ake yi shi ne; asali wasu Malaman ba su cancanci zama
Malamai ba. Kawai sun daura rawanin malumtar ne don su nemi abinci.
Ko kuma, ko
da Malaman ne, amma maslahar aljifansu ne a gabansu, da neman duniya, ba
Maslahar al'umma ba. Irin wadannan kuwa su ne tun a zamanin Magabata ake
zarginsu, ake kiransu da sunan "Malaman fada", kamar yadda a yanzu
ake cewa; "Malaman Gomnati", yaran 'yan siyasa. Masu zayyana musu
barna, da daure ma karya gindi.
Saboda haka
wajibi ne kowa ya ji tsoron Allah a duk matakin da yake.
Daga zauren Dr. Aliyu Muhammad Sani
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.