Ticker

6/recent/ticker-posts

Kokarin Gano Masu Daukar Nauyin Ta'addanci da Sunan Muslunci a Duniya

ƘOƘARIN GANO MASU ƊAUKAR NAUYIN TA'ADDANCI DA SUNAN MUSLUNCI A DUNIYA

Bayanai suna ta kara bayyana, wadanda suke tona asirin masu daukar nauyin ta'addanci a Duniya, ta yadda zuwa yanzu, mutane da yawa sun fita daga tababa a kan haka.

Yanzu abin da ya saura shi ne abin da ya shafi mabubbugar tunanin ta'addancin. Inda ake yaudaran mutane masu yawa, ana ce musu -wai- tunanin ta'addancin ya fito ne daga Ibnu Taimiyya da Muhammad bn Abdulwahhab. Alhali wannan ra'ayi ne wanda aka gina shi a kan ta'assubanci, da karancin ilimi, da rashin bincike. Wannan ya sa hatta cikin Malaman Sufaye a wannan zamani suke inkarin jingina bullar tunanin ta'addancin ga Ibnu Taimiyya, saboda a iya saninsu ga Ibnu Taimiyya ba su ga ta'addanci a cikin littatafansa ba. Irin su Aliy Gumu'a, tsohon Mufti a Misra. Da kuma Shaikh Sharif Saleh, shugaban kwamitin Fatawa a Nigeria.

Hatta jingina haifar da tunanin ta'addancin ga Saudiyya, duk wanda zai yi adalci ya san cewa; ita Saudiyya sawun barawo ta taka. Ma'ana; tausayin rai ne ya sa ta yi alaka da wadanda suka haifi tunanin ta'addancin. Asali wadanda manazarta da Malamai suke danganta haifar da tunanin ta'addancin gare su su ne Sayyid Qutub - abin da ya dauko daga al-Maududiy - da mabiya na Sayyid Qutub din, wato Qutbawa suka yi ta renon tunanin har ya iso wannan zamani, aka samar da al-Qa*ida, Bo.ko Har.am IS.IS da sauransu.

Duk wanda ya bibiyi silsilan rubutu da muka yi a kan Sayyid Qutub, da "Tarihin Bullar Ta'addanci" zai ga yadda muka yi bayani, bisa yadda su Dr. Yusuf al-Qardhawiy, Dr. Muhammad Amarah da sauran manazarta da masana, da masu bincike a tarihin kungiyoyi suka tabbatar. Haka mun kawo maganganun manyan kwamandoji na kungiyoyin ta'addanci, wadanda suka tabbatar da cewa sun sha wannan ra'ayi ne daga littatafan Sayyid Qutub. Kamar su Abdallah Azzam, Ai.man Zaw.ahir.iy da sauransu.

Abin da ya shafi Nigeria kuwa, mun tabbatar da cewa; shugabannin Muslim Brothers sun tabbatar da cewa; sun dauko Akidun ta'addanci ne daga littatafan Sayyid Qutub.

Kuma daga wancan tafiya Muhammad Yu.su..f ya dauko tunanin.

A takaice, abin da ya faru da Saudiyya shi ne ta tausaya wa Qutbawa, irin su Muhammad Qutub, da sauran 'yan Ikhwan, bisa muzgunawa da suke fiskanta daga Jamal Abdunnasir, sai ta ba su mafaka, ta ba su koyarwa a makarantu da Jami'o'i, da rike ma'aikatar ilimi. Har ta kai ga ana buga littatafan Sayyid Qutub a ma'aikatar Gomnati. Haka kuma wadannan mutane, wato Qutbawa suka zama cikin masu tsara Manhajar karatu. Wannan ya sa aka cakuda koyarwar Shaikh Muhammad bn Abdulwahhab da na Sayyid Qutb, alhali sun yi hanun riga. Na farko yana tafiya ne bisa Manhajin Salaf, Ahlus Sunnati wal Jama'a, na biyu kuma yana tafiya kan Manhajin Khawarijawa. An dauki lokaci mai tsawo Qutbawa suna yada wannan mummunan Manhaji, har sai bayan harin da aka kai Amurka a 11 Satumba aka gano abubuwa masu yawa. Kuma tun daga nan Gomnatin Saudiyya ta dauki matakin kakkabe wancan Manhaji da ake so ya samu gindin zama a Saudiyyan.

Ala ayyi halin, duk wanda zai yi magana ta adalci, bisa ilimi da bincike na hakika, ya san cewa; Sayyid Qutub shi ne tushen ta'addanci a wannan zamani, ba Manhajin Ibnu Taimiyya ko Muhammad bn Abdilwahhab ba.

Daga zauren Dr. Aliyu Muhammad Sani

zauren Dr. Aliyu Muhammad Sani

Post a Comment

0 Comments